Showing 183001 words to 186000 words out of 296907 words
Chapter 62 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT
waccan yarinyar kana kashe mata kudi,ko ka dauka bansan private ka kaita mai tsada ba?,itama taci kudinka ballantana ni,ita din da duka duka kwananta nawa a rayuwarka,duk kawaicina baka ganshi ba kenan tunda ni dama a wajenka babu abinda na iya na alkhairi"
Ido ya maida ya rufe kamar me shirin bacci,saidai ba baccin zaiyi ba,yana sauraren bugun zuciyarsa ne da duk bugawa take bugawar da zallar qaunar yarinyar tare da ambato sunanta,she means alort to him,batasan wace widad cikin rayuwarsa ba,yana dai qoqarin dannewa ne kawai,bai baiwa soyayayyarta kaso daya cikin goma damar fitowa ba saboda kada ya bada kafar barna ko baraka a tsakaninsu,a wannan yanayin yasan duk bayanin da zaiwa hafsat din a banza,ba zata fahimceshi ba sam,idan idanunta suja rufe kan abu kamar cin qwan makauniya,burinta kawai ayi mata abinda ranta yakeso,yana jinta tana ci gaba da zayyano dalilai marasa tushe bare makama,da ya gaji da jinta sai ya miqe tsam kawai ya dauki pillow ya yada a qasa ya kwana abinsa,abun da ya sake tunzurata kenan,ta miqe ta cire rigar baccin jikinta ta maida rigar lace dinta data cire,ta buda qofar tayi ficewarta,yadan bude idanunsa a hankali yabi bayanta da kallo harta fice,sai ya gyara kwanciyarsa yana rufe idanunsa,sam baiji wata damuwa ba don ta fita din,tun yana tunane tunane har bacci yayi gaba dashi.
A ranar kwanan kuka tayi ta godewa Allah,gaba daya tsanar widad ta gama cika mata zuciya,abubuwa da yawa basa faruwa saita sanadin zuwanta,gaba daya ta hargitsa mata gida ina dalili?,cikin ranta da zuciyarta takejin matakin data dauka shine dai dai, hukuncin data yanke kuma yayi dai dai,domin a yanzun babu wani abu da zai saurin sadata zuwa ga cimma burinta idan ba ta wannan hanyar ta biyo ba.
Washegari widad din ta shirya ita dasu mimi,tun da safe tayi musu wanka,ta cire kaya cikin wadanda abbas a taho musu dashi ya manta su cikin kayanta tayi musu kwalliya da kyau suka wuce gidan hajiya.
Taji dadin ganinsu matuqa,ta rasa inda zata sanyasu,a nan akayi mata jan lalle har bayan hannunta,hatta hajiya sai data yaba, idanunta na buye da Widad din tana ji a ranta anya ba juna biyu widad din ke dashi ba?, quruciya ta hanata ganewa,shi kuma uban gayyar hankalinsa baikai ba?,amma da yake hajiyan bata cika sanya baki a lamuran surukanta ba duk da tana jin widad sosai cikin ranta,kamar diyar data haifa a cikinta,duk da haka sai tayi shuru,cikin ranta ta bisu da addu'a.
Da yamma tace masa zata koma taje tayi girki,suna shirin tafiya sai gashi,tayi mamaki don bata tsammaci zaizo ya dauketa ba,haka kawai yaji duka gidan babu dadi bayan fitarsu,amma hakanan dai ya daure suka wuni da giwar tasa a haka😂,duk da babu abinda ya tsinta a zaman,don gaba daya babu fara'ar arziqi a tattare da ita bare hirar arziqi,to dama yaya lafiyar kura bare tayi hauka?.
Tunda ya shigo shima yake binta da kallo,lallen ya sake fito da ita sosai,ya kasa daurewa har sai daya bita kitchen yasha dumin jikinta sannan ya samu nutsuwa,suka tattare sukabar gidan hajiyan suka wuce gida.
Tare yau sukayi girki kamar yadda suka saba a Kaduna,gaba daya yau sai takejin kasala,har yana tsokanarta
"Kindaiyi qiba baby kawai" saita hau bubbuga qafa
"Niba wata qiba,Allah banaso" dariya mai taushi ya saki,ya dauketa cak ya dorata saman kantar kitchen din
"Ni kuwa bakiga yadda kikayimin kyau ba,komai ya fito yadda nakeso.....fiye ma da yadda nakeso,sannan kin qara dad......." Hannu tasa ta toshe masa baki,don tasan qaarshen zancan,kalmar tana matuqar bata kunya,amma taga shi kansa tsaye yake fadarta.
A daren ya same tantancewa,ya kuma sake nutsuwa da gamsuwa da cewa Allah ne kawai ya dubi zuciyarsa ya bashi widad din a lokacin da bai shirya ba,zuciyarsa kuma bata taba kawo masa ya aikata hakan ba.
*W A S H E G A R I*
Tunda sukayi sallar asuba tace masa tana son zuwa saloon,daga can zata wuce gidan uncle muhsin,kallonta yayi
"Baby.....salon yawo ko?,kinsan banason kina yawan fita,jiya me yasa baki gayamin an hada duka ba?" Kai ta langabe gefe,kwata kwata batason zaman gidan,sannan haka kawai takejin haushin hafsat duk sanda ta kalleta,shi yasa batason ma hada waje da ita,bare yau tasan can zai kwana,may be tana kallonsa zaua tafi can ya barta ita kadai a sassanta,sai mimi dake tayata kwana,ta narke fuska
"Don Allah uncle,na dade fa banje ba" ido yadan zuba mata,sai kuma yadan saki murmushi
"Shikenan" qanqameshi tayi tana fadin
"Thank you uncle" ido ya lumshe yana murmushi,jikinsa na amsawa saboda yadda ta manna masa jikinta sosai,hannunsa yasa ya dagota yana duban qwayar idonta,kamar me rada yace mata
"In dan qara?" zamewa tayi tana dariya hadi da boye fuskarta cikin hijabinta,duk sanda ya buqaci kadaicewa da ita a fargaba yake sakata,har yanzun bata saba da abun nan ba
"Ni uncle....banason nayi ciki,mutuwa zanyi idan nayi ciki fa" ta fada a shagwabe,tattausan hannunta ya kamo ya riqe,duk da qarancin shekarunta amma yasan tana da matuqar juriya dashi,shi kansa baisan me yasa baya gajiya da ita ba
"Bana gaya miki ba wannan abun ne yake sawa a samu ciki ba?,sai kinsha ruwa kin qoshi sosai idan aka gama shine ake samun ciki" kai ta gyada a hankali alamun gamsuwa,ya bita da kallo can qasan ransa yana danne dariyar daketa cinsa,yana mamakin yadda ta yadda da wannan dabarar daya shirya mata,quruciyarta tana bala'in tafiya dashi,wani abune da yake kallonsa na musamman tattare da ita,don tana debe masa damuwa sosai,tana barinsa a nishadi duk sanda ta tafka wani babbar wautar da quruciyar.
Tada da himma sosai,duk da tana danjin kasala da nauyin jiki amma sai data gama gyara gidan tsaf,ta shirya breakfast sannan sukayi wanka,tare suke wanka daman,indai ba wani babban uzurin fita bane ya taso masa,wannan yasa suka gama da wuri ya rigata fita parlor ya fara yin break din,ita kuma tana ciki tana qarasa shiryawa.
Cikin baqa wul din abaya mai wani irin aiki da stones masu sheqi ta shirya,wani irin kyau tayi mai daukar hankali saboda yadda abayar tabi lafiyayyar farar fatarta ta kwanta da kyau,ita kanta sai data kalli kanta har sau babu adadi,ta juya gaba da baya sannan ta rola mayafin sama kanta,ta dauki wata 'yar mitsitsiyar hand bag mai hade da takalmi ta jefa wayarta a ciki sannan ta fito.
Mug din da yayi niyyar kaiwa bakinsa ya sauke,ya bita da kallo tamkar yau idanuwansa suka saba ganinta
"Ma sha Allah!" Ya furta yana kallonta,yana ji kamar ya buda zuciyarsa ya sanyata ya huta da radadin sonta da yake ji.
Sama sama tayi break din,yanata tsokanarta da zumudin zuwa gidan uncle ya hanata cin abinci,suka fito tare
"Bari na sallami antynki" ya fada yana buda mata motar ta shiga,sannan ya wuce sasssn hafsat din,tadan bishi da kallo saita dauke kanta zuwa gaban motar,ta jawo wani littafi ta soma buda shafukansa don ta ragewa kanta damuwar da take ta ji,da kuma wata irin faduwar gaba data tashi da ita tun dazun da safe.
Suna zaune da yaran suna breakfast suma,wanda ba komai bane sai ruwan tea da tsurar bread,ya dauki yaran ya musu wasa yayi kissing dinsu sannan ya ajjiyesu,ta gaidashi fuska a cunkushe ya amsa mata,har batason kallonsa musamman idan ta tuna daga inda ya fito,wajen waye ya kwana,ya ajjiye mata kudi yadda ya saba,zai fita mimi tace ya tsayata zata gurin anty weedad
"Antynku fita zatayi" jin haka yasa hafsat din tasha jinin jikinta kan tare zasu fita,don haka ta miqe sa nufin masa rakiya,abun yadan bashi mamaki don ba sabonta bane,amma.bai hanata ba,suka jero tare suka fito.
Cikin jikinta taji kamar yana tahowa,ta daga kai sai ta hangosu a jere da juna,tashin farko taji wani abu ya tsaya mata a wuya ganin yadda suka jera din,ta maida dubanta kan fuskar hafsat din,wani haushinta ya cikata,saita dauke kanta ta mayar kan littafin tayi kamar bata gansu ba.
Har suka iso wajen idanun hafsat din na kan widad,wani irin zafi me tsanani takeji a ranta game da yarinyar,kyan da tayi ya tsaya mata a rai,ta fito sakkk balarabiya,to amma tana samun sassauci ta wani fannin idan ta tuna gab take da yin maganin matsalarta,kowanne lokaci ne daga yanzu,don haka tayi masa a dawo lafiya tan juya zuwa ciki ranta yana mata suya da yadda yarinyar ta nuna halin ko in kula da ita,gaisuwar ma da take mata yau bata sameta ba,lallai ta yarda raini ne yake ci gaba da tsirowa a tsakaninsu,sai kuma ta saki wani irin murmushi tana jan qwafa
"Zakisan ni ban sa'ar yinki bace yarinya" ta furta tana shigewa sassanta.
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*
Page 94
Tunda ta isa gidan uncle muhsin sai ta sake sosai abinta cikinsu nujood,bayan sun gama hira da hajjaa a kebance,ta tabbatar babu sauran abinda yake damunta,saidai lokaci lokaci gabanta yana yawaita faduwa,saita tsaya da abinda takeyi idan ya lafa kuma taci gaba da sabgarta.
Da yamma ya kira ta yaji kota wuce saloon din,tace eh gata ita da nujood sun fito zata rakata,abun mamakin saita taddashi acan,zaune cikin mota yana jiran isowarsu.
"Gaskiya gaskiya nima cewa abban zanyi ko ya samo min police na aura,ko ya samomin cikin abokansa,irin wannan kulawa widad ba kowacce mace ke samun irinta ba,just saloon ma sai an miki rakiya ko anzo an jiraki harki gama a maidaki gida don kada ki shiga motar haya?" Idanun widad din akan abbas din sanda nujood ke maganar,duk da basu qarasa ba suna kusa da qarasawar amma idanun kowa yana kan dan uwansa,saita saki murmushi kawai ba tare data amsawa nujood ba, saidai can qasan ranta ita kadai tasan ya takeji akan uncle din nata,har wani lokacin takan zauna tace wai shin wa tafi ji dashi,wa tafi so tsakanin shi ummu ko mommynta?(quruci dangin hauka,kowanne so akwai kalarshi,na iyaye daban na miji daban).
Fitowa yayi ya taka mata har zuwa bakin qofar wajen,sannan ya gaya mata abinda ya saba fadi
"Ki fada mata tayi miki mai kyau,irin wanda ba'a taba yiwa kowacce mace ba" dariya ta kamata itama kamar kullum,shidai yanason gayun nan,yana son kwalliya,duk sonta da kwalliya ta samu wanda ya fita,tana murmushi ta shige,yayin da nujood ta rigata yin gaba tana jin kunya,saboda tamkar mahaifi take kallonsa.
Sanda aka gama sai suka sauke nujood a gida,bayan ya bata kyautar dubu biyar,ta shiga ta yiwa hajjaa sallama,wadda ta hada mata kayan miya,kamansu kuka daddawa kubewa mai kyau da sauransu, saboda itama tasan abas din dason wannan cimar na gargajiya,tayi musu sallama ta fito.
Suna tafe a hanya suna hira,duk da uncle din nata shine jigon hirar,kadan kadan take saka baki,saboda yadda faduwar gabanta take qara yawa fiye da dazu,a wani shopping mall ya tsaya yana dubanta
"Zaki rakani?" Ya fada a tausashe,ta sake masa murmushi tana ajjiye jakarta ta fito tabi bayansa.
Tana biye dashi ne kawai,shi ya dinga daukan kalar kayan da yakeso,wanda duka qananun kaya,irinsu mini skert leggings shirt shirt na masu daukan hankali da kuma lalatattun sleeping wears,kusan wannan din al'adarsa ce,yanason wannan shigar a wajen matarsa,a lokacin da hafsa kadai yake da ita,duk sanda yayi siyayya irin wannan asarar kudinsa kawai yakeyi,don ba sakawa takeyi ba,a yanzun kuwa kusan tare suke zabar kayan da zata saka masa duk rana shi da widad din,musamman idan suna Kaduna,sai wanda ya zaba zata saka masa,bata wani damuwa saboda kayan sunfi mata dadin sakawa a yanzun,idan tana cikin gida zaiyi wuya ka ganta da atamfa bare lace ko shadda,kayanta kenan,wani mugun kyau kuma sukeyi mata,bama kamar idan ta raba gashinta biyu,kota musu manyan kalba,yakan lalace wajen kallonta ne,itakam da batajin nauyin jikinta tayita tsalle tsallenta abinta.
Chocolate ya hada dasu masu dan yawa saboda su mimi ya biya kudin suka fito,ya miqa mata ledojin yana cewa sanda yake shirin kunna motar
"Ta kayan taki ce,ta chocolate kuma ta sha zumamu mimi ce" qaramar dariya tadanyi, tanason zaqi kam yarinyar,sai ta buda ledar kayan nata tana diban wasu tana zubawa a ledar su mimi,yadan kalleta yana yin reverse
"Me kikeyi haka?"
"Mommyn mimi na sakawa wasu kayan,baka siya da ita ba,naga kudin da yawa" kai ya girgiza suna haurawa kwalta
"Kinason kiyimin asarar kudina na kawai....." Sai kuma yayi shuru ba tare daya qarasa ba,sannan ya sake cewa
"Duka naki ne,jibi nakeson ki zaba me kyau a ciki.....wadda tafi kowacce kyau ki sakamin,ita kuma duk sanda muka fita ko tace tanaso saina siya mata nata daban" bata kawo komai cikin kanta ba ta gyara ledar ta mayar dasu yadda suke.
Ana kiran magariba suka isa gida,wasu masallatan ma har sun tayar,ya kashe motar ya rakota,gudun kada sallar ta qwace masa saiya tsaya daga qofar falonta ta bude ta shiga shi kuma ya koma da dan sauri don ya riski sallar.
Duhu falon saboda ta kashe dukka qwayaye kafin ta fita,tana tsoma qafarta gabanta yayi mummunar faduwar da har sai data dora hannunta a qirjinta,wani irin mahaukacin tsoro ya saukar mata,saita saka hannu tayi hanzarin kunna wutar sassan nata.
Duk da haske ya wadaci wajen amma abinda ya gushe na tsoron daya saukar mata din bashi da yawa,ta fara takawa a hankali kamar mai sanda ta nufi dakinta,duk inda ta tsoma qafarta ta dauke sai taji kamar ana biye da ita,wannan ya sakata qara hanzari,ta fada dakinta ta tura qofar tayi zaune bakin gado tana wuwwurga idonta cikin dakin,cikin sa'a bakinta ya kama kalmar
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil,ni'imal maula wa ni'iman nasir" sannu a hankali saita fara jin tsoron yana raguwa,ta rufe idonta tayita maimaitawa kafin ta bude idon a hankali,sai taji tadan samu nutsuwa,ta ajjiye ledar da mugun takatsantsan saboda qarar ledar tana jinta har cikin kanta,ta cire mayafinta ta shige bandaki tana fatan mimi ta shigo mata ko ta rage zaman shurun.
Alwalar data yo ta qara mata nutsuwa,ta dawo ta tayar da sallah,sanda ta idar sai tayi zaune saman abun sallar,gidan shuru ba motsin kowa,sai qarar babban generator dake aiki a farfajiyar gidan,yana daya daga cikin abinda yasa ta tsani bauchin,wannan zaman,inda a kaduna suke da yanzun tana jikin uncle dinta,suna karatu k suna wani abun tare,komai ma tare sukeyi ita dashi,ba wani abu da suke rabawa,kama daga wanka bacci cin abinci,sallar ma wataran jam'i sukeyi ita dashi,ya tsefe mata kai ya yanke mata farce,wani zubin ma har ya gwada mata kalba,amma a bauchi fa,duka time dinsa yana rabasu ne a tsakaninsu.
Tana nan zaune har akayi kiran isha'i ta tashi ta gabatar,ta sake komawa ta zauna,tun yamma rabonta da abinci,amma kuma bata jin yunwa,batasan me yake damunta ba,wani lokacin ta tashi da mahaukaciyar yunwa,wani lokacin kuma ta tashi bata sha'awar cin komai,duk da haka dole ta tashi ta shiga kitchen bayan ta leqa window ko zataga wulgawar mimi amma ba ita ba alamarta,ta tsaya ta dafa indomie guda daya ta soya qwai biyu,tana yi tana takatsantsan,duk duk wani motsi da zatayi da kwanukan firgita takeyi,tana gamawa ta dawo daki ta zauna ta tasa abincin a gaba.
Tana fara ci taji bataso,saita ture plate din,zuciyarta na mata wani qunci,kawai sai ta fashe da kuka sosai tana curewa waje daya,gidan gaba daya ya fice mata akai.
Yana zaune da wayarsa a hannu yana amsa saqonni,su mimi na gefe suna wasansu,yayin da hafsat din ke hada masa abincin dare
"Yau ba zuwa wajen anty mimi?" Ya tambayi yarinyar yana aje wayarsa bayan hafsat din tace ta gama zubawar
"A wajen mahaifiyarta zata kwana" hafsat dake shirin zama tayi caraf da maganar,duba daya yayi mata ya kauda kansa gun yaran yana gayyatarsu suzo suci abinci,kusan al'adarsa ce wannan,tunda mamarsu bata iya cin abinci dashi ba,tare dasu yake cin abinsa,tun bai saba ba har ya zame masa jiki.
Tana daga zaune a gefensu,bata ce komai ba,suna cin abincin suna hirar su da yaransa yana dariya abinsa,abinda yake sake qule hafsat kenan,sai abu mai ciwo ya faru,tana ganin abun yakai munzalin bacin rai,amma sai yasa yaransa a gaba suyita sabgarsu,taja qwafa can qasa tana jijjiga kai,idan komai bai faru ba ashe bata cika hafsatu ba.
Suna gama cin abincin ta kada kan yaran zuwa dakinsu,basa jin bacci a sannan amma haka ta tilasta musu kwanciya,ya fahimci me take nufi,bayason suje wajen widad din,sai shima ya watsar da ita,ya wuce toilet yayi wanka hade da brush,ya shirya cikin wasu silk pyjama sky blue,ya dauki wayarsa ya wuce sassan widad din don ya mata sallama,ta bishi da harara ba tare da yasan me takeyi ba,cikin ranta fana fadin
"Na kusa maganin matsalata naga qarshen wannan rawar kan".