Header Ads
Showing 195001 words to 198000 words out of 296907 words

Chapter 66 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

yanzu ba ta tabbata da safe zai shigo,zata ga da wanne ido zai kalleta.

Daga sallar asuba ya zarce da wanka,kafin qarfe shida ya gama shirinsa tsaf,ya fidda luggage dinsa ya saka a mota.

Sale ya barwa envelope yace ya bawa matar gidan,kudaden hidimar gida ne a ciki,ya zare dukkan wasu kudade daya saba bar mata wanda suke kyautatawa ce kawai bawai na haqqin dake wuyansa na shari'a ba.

*********Da farko ta watsar dashi kamar yadda ya watsar da ita,don ba qaramin shaqar takaici tayi ba sanda ta karba saqon ta hannun sale,ya rasa wa zai bawa aiken kudin amfanin gidanta sai salen?,bata sake shiga rudu ba sai dataga kowanne kudi ya fadi na meye,babu ko qarin sile akan abinda ya saba bata,gashi buqatar kudin take da gaske saboda fara adashin asara data yi,ko cikin satin ummanta tace lallai lallai ta tanadi kudi,saboda ba zasu taba bari sakaci ya shigo cikin aikin da aka fara ba,wannan ya sanya ta sake qullatar widad din qwarai,a duniya idan aka bata bindiga akace ta kashe mutum daya widad din zata fara harbewa.

Yadda ya dauke mata wuta abin ya fara damunta,gashi tana fuskantar EDD dinta yana sake matsowa,wata zuciyar tana ta kirashi wata tana ta shareshi,a haka kwanakin suka fara tafiya, dole daga bisani ta karya billent ta kirashi,ta kuma maida komai ba komai ba,don lallai tana buqatar kudi.

*B a y a n wa t a u k u*


Bayan watanni uku hafsat din ta sauka,ta sake samun baby girl,zagayowar kwanaki hudu abbas ya dauki excuse don zuwa ganin baby,dole widad ta soma shirin binsa itama,don rabonta da bauchi tun wancan lokacin da suka samu sabani da hafsat,duk sanda zaije weekend tabar binsa,saidai yaje yayi kwanaki biyu ya dawo Kaduna,hakan yafi mata kwanciyar hankali,har ya zamana koda wasa batason taji ya ambaci xuwa bauchi da ita,yanzu zataji hankalinta ya tashi.

Ta shirya tsaf tayi sabbin dinkunanta,gyaran gashi zuwa lalle suka wuce bauchi,ranar ta shiga sassan hafsat din,wanda rabonta dashi har ta manta.

Ba wani mutane bane sosai, kasancewar ita din dama bata mutane bace,mai zuwa mata sha'ani sai wanda ya dubi Allah,anty ummee ce sai wasu baqi mata biyu sai 'yar yayarta data dauko saboda aikace aikacen gidan,sai hajiya habiba.

Ciki ciki hafsat din ta amsa mata barkan data mata,itama sai bata saka kanta can ba,ta zauna daga hannun kujera,anty ummee ta miqa mata baby da aka gama yiwa wanka tana qarewa widad din kallo tsafff tana kaduwa da yadda taga ta sauya,ta karbeta tana jin sha'awar yarinyar har cikin zuciyarta,kasancewarta mai son yara sosai.

"Uhmmm.....ko a bar miki ita ne?,naga kin kasa daina kallonta" hajiya habiba ta fada tana wani munafukin murmushi tana kallon widad,sai ta saki murmushi kafin tace komai hafsat ta rigata,taja wani mugun tsaki tana gyara zamanta

"Ki daina irin wannan wasan hajiya habiba......haihuwa wasa ce da zaka dauki yaro danka ka baiwa yaro,wanda ko ciwon kansa bai sani ba?,tab..... garinsu da nisa ai,idan fitsari banza ne kaza tayi mana" tsaf ya fahimci abinda hafsat din take nufi,don haka ta miqe tsam ta miqawa anty ummee babyn tana cewa

"Allah ya rayata" ta fice a nutse a falon ta wuce sassanta,don saukarsu kenan ta fara shigowa nan din.

Tare hajiya habiba da anty ummee suka dauke kai daga kallon widad bayan ta bace musu,suka maida kan hafsat data fara qananun motoci tana sakin tsaki kamar ta tsinke harshenta

"Banso kika sanya baki ba,kallon me juna biyu nakewa yarinyar,naso na bugar mana cikinta muji akwai ko babu" hajiya habiba ta fada tana duban hafsat

"Ai banza ce,nima kallon da nakeyi yarinyar kenan tunda ta shigo,kamar me yaron ciki,canzawar tayi yawa,ni tsorata ma nayi dana ganta wallahi,ta zama wata babbar mace?" Anty ummee ta fadi tana kama bakinta.

"Allah ya kiyaye Allah ya sawwaqe,ni kuwa ina me zan zauna na barta tayi ciki?,haba don Allah,bazai yiwu ba" hafsat ta fada tana girgiza kai,cikin zuciyarta tana jin wani irin zafi kamar ma ance cikinne,tana qiyasta yadda zata cakuda 'ya'yanta da 'ya'yan wata matar?,ba zaiyuwu ba,ba zata iya ba,barin widad din ta samu ciki harta haihu shine babban kuskuren da zata tafka

"Idan ba mataki kika dauka ba sanda zai narka mata cikin sani kikayi?,kina nan kina bacci saidai ki tashi ki ganshi" hajiya habiba ta fada tana miqewa tsaye gami da daukar jakarta

"Bafa wannan maganar hajiya,matakin nasa aka dauka,shi yasa nake cika miki baki"

"To yanzu naji magana.....hmmm aikin hadu da alaqaqai ciwon zamani mai wuyar magani"

"Ko tunata banason yi wallahi hajiya,ban taba kawowa yarinyar nan zata shiga rayuwata tayimin karen tsaye har haka ba" hafsat din ta fada yana sauke idanunta a sassan widad din tana jin ranta yana mata ciwo.

Duk da jego take amma hakan bai sanyata ta barwa widad din kwananta ba,haka take diban jiki tabar masu tayata zama ta wuce sassansa ta kwana,ko daya widad din bata bari taga damuwarta ba,saita shiga sabgar gabanta kawai.

Da kansa yace me take buqata na taron suna,tace zata kirasa idan ya fita,saita dauki waya sukayi magana da anty madina

"Kiyi komai naki ta yadda ba ruwanki da abincin taronta,wanda ya shigo miki ki bashi,wanda ma baizo na ya hutasheki" da suka gama wayan saita kira hajjaa ita kuma ta gaya mata yadda suke komai na taron suna,ta yiwa abbas din waya ta gaya masa,ya ajjiye mata komai,da taimakon hajja takai aikin abincinta,masa da sinasir sai soyayyiyar shinkafa (fried rice).

Ana gobe suna ta yiwa uncle muhsin waya ya bar nujood tazo suka kwana tare,washegari aka tashi da suna.

Kwalliya ta dinga yi sosai,tana canza shiga cikin kayan da abbas din ya dinka musu,duk da na hafsat din ya dara nata,da kadan da kadan saiga mutane sun cika sashen nata, don duk wanda ya shigo din ga abinci nan zaici ya qoshi,sashen mai jego kuwa babu bayani,don kudinta ta adana,ta sada mutane da wata irin jallop din shinkafa data hadu da taqadiriyar dahuwa mara tsaro,dukka lemon roban da yasa aka jibge ta debesu,ta musanya da zobo dan dauri.

Daga qarshe dai sassan widad sai ya zamana kaman a nan akayi haihuwar,duk wanda ya shigo din kuwa saiya qoshi da abinci me kyau,hafsat na daga sassanta amma labarin abinda ke faruwa a sassan widad din tuni yaje mata,ta cika tayi fam,musamman matan abokan abbas din da suka yada zango a can bayan sun mata barka,don ba wadda ta zauna a cikinsu,saboda ba wani kyakkyawan mu'amala bace tsakaninsu,tsananin kirkin abbas din ne ma ya sanya suka kasa qin zuwa,dama kuma idan ka gansu a gidan to saifa irin hakan ta kama.

Kasa zaune bare tsaye hafsat din tayi,da yammar ta canza kaya na biyu shima bisa takurawar anty ummee

"Kiyita zama,suttura iya sutura an miki amma kin jibgesu,ga kishiyarki can kowa fadin shigar ta yakeyi,keda ake taron don ke amma kamar saboda ita akeyi" sannan ne ta sake saka wata atamfar.

Sanda ta fito falon tayi baqi ta hangi fitowar widad din ta window din falon nata da aka dauke curtains dinsa,ta yima matan abokan nasa rakiya,tana sanye da shadda 'yar mali,baqa ce da aka yiwa adon mustard yellow,zo kaga baqar shadda jikin farar mace,an tsara mata wani mugun dinkin bubu,ido kawai ta runtse hafsat din tana dauke kanta daga wajen tana jin Zuciyarta kamar zata fashe.

Kwana biyu da suna suka koma inda suka fito,tabar hafsat din da tarin ciwo a zuciyar ta,da kuma K'ULLACI hadi da ALWASHI iri daban daban akan widad din.

Duka duka sati uku da komawarsu bauchi tafiyarsu ta taso,zasu tashi ta kano,don haka suka shirya zuwa bauchin yayi sallama da hajiyansa,ya kuma sallami gida sannan su wuce kanon.

Kamar ko yaushe,cikin tsoro da wani mugun bacin rai da qunci ta sauka a sassan nata,yau din tana jin tsanar gidan sosai fiye da ko yaushe,cikin qafafunta takejin kamar ba lallausan carfet take takawa ba,kamar qayoyi ne zube a sassan nata gaba daya,haka ta dinga qoqarin dannewa ta fara gyaran sassan nata tayi ta kammala ta samu waje ta kwanta,wata muguwar kasala da nauyin jiki suna mamayeta,wanda a kwanakin nan sai sake gaba abun yake,har abbas din yace muddin sukaje hajjin suka dawo babu wani sauyi to ko bataso dole taje taga likita.

Kamar wancan karon,wannan karon ma har bacci yadan fara fusgarta taji kamar an soma shaqeta,ta farka da sauri tana ambaton sunan Allah,sai numfashin ta ya ware ya koma dai dai,ta miqe a hankali tana sauke ajiyar zuciya,tana jin kamar ta fice a gidan kota yaya,sai ta zura slipper dinta kawai ta bude qofarta ta fito.

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks: Huguma*

Page 100

A hankali take taka harabar gidan,tana jin kamar magnet ke janta zuwa waje,har ta kusa da gate din ta taka wani dan qaramin dutse mai tsini,zafin da ya soketa ya sanyata furta

"Subhanallah" ta tsugunna tana dub qafar,Allah ya taimaketa bata huje ba,banda zafi da radadin da takeji kawai,koda ta dago sai ta tsaya tana duban qofar fita daga gidan dake kulle,tare da tunanin meye ya fito da ita a wannan daren?,saita girgiza kai ta juya tana komawa ciki.

A hankali yake takowa zuwa dakin solar na gidan,don ya duba yana tunanin kamar sale bai kulle ba,cike da mamaki yake kallonta sanda take takawa zata koma sashenta,to daga ina take?,da alama ma bata ganshi ba,sai ya canza akala ya dosheta.

A tausashe ya kamo lallausan tafin hannunta ta baya,tadan firgita kadan sannan ta waiwayo suka hada ido,ta saki waya ajiyar zuciya mai nauyi

"Ina kikaje haka"

"Babu ko ina,kawai na gaji ne" qarara ya karanto zallar gajiya da qin da takewa garin na bauchi a idanunta,sai ya jinjina kai

"Muje kidan motsa,dama kin fara qiba ba dole ki dinga gajiya haka kawai ba".ya fada cikin salon tsokana yana lakuce mata kumatu,sai ta shagwabe masa tana tabe baki kamar mai.shirin sakin kuka,sakato.yayi yana kallonta tana sake tsumashi,don dama duka.yau din baiga wannan narkakkiyar shagwabarta ta ba,sai tsomoshi da shigar data dinga yi a sunan data dinga yi,duk sanda zai.shigo kuma sai yayi tozali da ita,ya dinga jin kamar ya dauketa subar gidan ya samu ya rage zafi,amma sanda yaga yawan jama'ar dake sashenta dole ya haqura ya hadiye,hafsat kuma ko a yanzun a dakinsa ya barta,ko kwana daya bata yarda ta bariwa widad din ba.

Sassanyar iskar daren dake kada jikkunansu ta dinga haifar musu da wani yanayi cikin zukatansu,kada ma abbas din yaji labari,ya sake matsowa ya.kama hannunta suna ci gaba da strolling

"Jibi zamu wuce,gobe ki kammala komai naki" da mamaki take dubansa har batasan murmushi ya subuce mata ba,bata dauka zasu koma da wuri haka ba,saboda taji yana cewa babu cinkoson aiki sosai,ya waiwaya a hankali ya sauke mata narkakkun idanunsa

"Oh......murna ma kikeyi?" Nata fararen idon ta juya,lallausan murmushin dake qara fidda quruciyarta ta saki tana maida dubanta gefe

"Dole ne ai......zan sake da uncle dina" murmushi mai dan sauti ya saki yana kallonta cikin mamaki,sannan cikin tsokana yace da ita

"La la la.....eh lallai zan gayawa uncle muhsin,yarinyarsa tasan dadin mijinta" ya fadi qasa qasa dab da fuskarta,sai ta saki dariya tana zame hannunta daga nasa cikin jin kunya

"Don Allah uncle karka fada" ya bita da sauri yana son cimmata yana sake tsokanarta kan sai fa ya gaya masa.

Kamar yadda yace din kwana daya suka qara suka tattara suka koma kaduna abinsu,hafsat din tana ta cika tana batsewa,don ko fitowa batayi ba,daga daki sukayi sallamarsu suka gama.

Ajiyar zuciya mai nauyi widad ta sauke sanda motarsu ta fita daga qasar bauchi tahau ta kaduna,har sai da abbas din ya juyo ya kalleta.

*********Cikin wata muguwar zabura ta farka tare da miqewa zaune saman gadonta tana rarraba idanu,gumi sharkaf ya jiqa mata ilahirin rigar atamfar da take jikinta yana zartarwa cikin jikinta,kadan ya rage ta danne baby yusra dake bacci a gefanta,ji tayi kamar alqiyamarta zata tsaya,wannan wanne irin mafarki ne mai muni mara dadin gani?,me mafarkinta yake nuna mata kenan,widad dauke da baby tana miqo mata ita?,me hakan yake nufi?.

Wayarta ta jawo tana dubawa kamar me neman wani abu,a sannan tayi ido hudu da number abbas,waddda itace kira na qarshe a jerin lambobin da aka kirata ko tayi kiran,awanni hudu da suka wuce,yake gaya mata jibi zasu iso bauchin,duk da sai da suka kusan dan samun sabani saboda a maganarsa ta fahimci da widad din xasuzo,abinda duk duniya ta tsana kenan a yanzu,take kuma neman hanyar da zata kawo qarshen faruwarsa.

"Anya ba ciki ne da yarinyar ba?" Wata zuciyar ta gaya mata,saita hau girgiza kai da sauri kamar hauka sabon kamu,kai kace ita da wani suke magana a dakin

"Inaaa,inaaa,bazaiyiwu ba" ta fada a fili,ba zata taba barin haka ta faru ba muddin tana raye,cikin abbas ace ya tabbata a jikin wata?,da kuwa lallai ta rako maya duniya,ta kuma cika hasararriya,iya qiyasta hakan kawai da tayi sai taji kamar zuciyarta zata tsinke tabar qirjinta,haka fa na nufin ya hada shimfida da ita?,ya santa a matsayin diya mace

"Aah..... a'ah" ta sake fada tana girgiza kai da sauri.


Ji tayi kamar ta kirashi tace su taho gobe,lallai kuma yazo da widad din, saboda tanason ganewa idanunta,shin da gaske ne abinda zuciyarta ke raya mata?,ko hasashe ne hadi da shirmen mafarki?.

Wanann daren sai ya zame mata baqin dare,don tunda ta farka ta gagara komawa,saidai ta zauna idan ta gaji takai ta kawo har asuba ta risketa a haka.

********Sau biyu yana duba agogonsa sannan ya maida dubansa ga qofar fitowa daga sassanta,kusan minti goma tace tana zuwa,amma har yanzu bata fito ba,bata saba hakan ba,ba halinta bane,duk sanda zasuyi tafiya ko zasuje waje bata fiya bata masa lokaci ba,idan yace qarfe kaza kome takeyi ta kammalashi kafin wannan lokacin.

Fitowa yayi daga motar hannunsa sanye a aljihun wandon yadin cashmere mai asalin kyau da tsada,wanda ya karbeshi qwarai,ya tunkari sassan nata yana fatan samunta lafiya.

Saman kujera ya sameta zaune,tayi likimo a ciki kamar bamai shirin tafiya daga kaduna har bauchi ba,sai daya isa kanta sanann ta daga idonta ta kalleshi,saita miqe cikinmu mutuwar jiki tana sauko da qafafunta qasa hadi da gyara rufin veil dinta tana cewa

"Sorry uncle,yanzu nakeson fitowa"

"Me ya sameki?" Ya tambayeta kansa tsaye yana tsare sosai da idanu,qas tayi da kanta,batason gaya masa amai tayi kuma jiri take ji,batason hankalinsa ya tashi

"Me yake faruwa dake ne?,ki gayamin gaskiya,karki yadda kicemin ba komai,jiya da daddare na ganki,tashinki nawa kina shiga toilet,na tambayeki kuma kikacemin lafiya qalau" yadda yayi tambayar cikun seriousness sai ya koma mata ASP abbas sosai,miskilin nan mai tsare gida da baiwa masu laifi tsananin tsoro,dole ta buda baki a hankali tace

"Amai nayi,sai jiri,sai kuma fitsari da nakeji,idan naje yi kuma sai naga dan kadan,marata tayi kamar an saka dutse" shuru yayi yana kallon fuskarta,wani abu ya darsu a ransa,amma sai wata zuciyar ta kawar,don ba haka ya saba gani ba,ya miqa hannnunsa a hankali ya taba wuyanta ya janye hannun jin babu zazzabi

"Subhanallah,amma shine kike ta cewa ba komai baby?" Kai ta langabe batace komai ba,sai qishirwa dake damunta,kamar ya gane me take nufi,ya isa fridge ya ciro mata ruwa mai madaidaicin sanyi ya bude ya miqa mata,tana tsaka da sha ya nema gefanta ya zauna yana murza agogon hannunsa

"Banajin tafiyar nan zata yiwu......"

"......don Allah uncle" tayi saurin katsar numfashinsa,tunda taji zasuje ayi mata vaccination na tafiyarsu wadda duka duka saura kwanaki biyar ta matsu suje din,ido ya lumshe yana dariya

"Bance wai an fasa ba,nima inason zuwa naga hajiyata,bazata yiwu ya mota ba,bari na duba mana rocket ko zamu samu koda evening flight ne" ido ta rufe tana dariya,kunya kuma tana kamata na yadda tayi saurin yanke masa hanzari

"Kayi haquri uncle"daga kansa yayi daga danna wayar ya kalleta yana murmushi,bai taba zaton bada haquri abu bane mai sauqi wajen diya mace ga mijinta ba sai daya zauna da widad,kalmar haquri kalma ce mai matuqar tsada da wahalar furtawa a wajen hafsat,tsahon shekaru bakwai,adadin lokuttan da ta taba buda baki ta bashi haquri tsaf zai iya qidayesu da yatsun hannunsa.

Kafin su fita daga gidan zuwa airport ta qarfafa jikinta,duk don wai ya sake yadda ba wani ciwo take ba,ya kuma janye maganarsa na suna sauka yau din gobe zai kaita a dubata.

Sau uku tana kiransa wayarsa a kashe,ta qagu su iso tayi ido hudu da widad din kamar yadda ummanta tace ta fara tsaiwa ta tabbatar da gaske da cikin?,ta duba idan taga wani

Ads At the End of Article
Sidebar Ads

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads