Showing 27001 words to 30000 words out of 296907 words
Chapter 10 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT
sakanni,sai kuma ta saki murmushi
"Wai widad?,aikin musaddiq ne wallahi"
"Musaddiq din muhsin wai?,dama sune?"
"Sune,a nan hajjaa ke barinsu,idan ta taso daga makaranta take daukansu,widad kam ai bata da hayaniya ko kwaramniya,shaqiyancin musaddiq dinne,yasan yadda take tsoron kyankyason ya saka mata shi" kai ya jinjina kawai ba tare da yace komai ba,sai a sannan hankalin hajiya kuma ya dauku ga fuskarsa,ya akayi har ya shigo gidan tun yamma bai nemeta ba,fuskarsa ta nuna akwai damuwa tattare dashi
"Allah dai yasa lafiya" ta fada bayan sun gaisa,furzar da iska yayi daga bakinsa,ya motsa baki zaiyi magana ta datsi numfashinsa
"Kada kacemin babu komai" shuru ya ratsa falon na wasu sakanni,sai ya buda baki a hankali yana gayama hajiyan zancan tafiyarsa kaduna da hafsat tayi tutsun ba zata je ba.
Ran hajiyan ya dan tabu,tun ba yau ba tasan matsalar dake cikin gidanshi,ba yau ta fara gani da fuskanta ba,saidai batason shiga lamuran gidansa sam,hakanan a matsayinta na uwa bata da abinda zata masa illa addu'a da kuma bashi shawara na gari
"Kayi haquri ka tafin,kada ka matsa mata,duk sanda ka samu sarari ka dinga zuwa kana ganinsu,ta wani fannin tana da hanzarinta daya kamata a duba,ko don karatun mariya(mimi) da yanzu ta farashi kada ya samu tangarda,zama da iyali dan haquri ne,mahaifanku dukka haquri sukayi damu har zuwa sanda Allah ya rabamu,komai yayi farko kuma yana da qarshe" ajiyar zuciya ya saki,maganganun hajiyan sai suka sake kwantar masa da hankali da sanya masa nutsuwa,kalmominta masu tsada ne da baiwa zuciya da kuma ruhi nutsuwa,take yaji gaba daya dukka wani kwadayinsa na tafiya kaduna da hafsat din yakau a take
"Na gode hajiya" ya fada yana bude abincin data saka aka kawo masa,ya fara ci a hankali suna hira da hajiya,hirar da ako yaushe ita ke debe masa damuwa.
Basu jima suna hirar ba babban yayansa ya shigo,wannan yaja hirar tasu,har yakai qarfe tara na dare,sai da zai tafi yace ya saukeshi a hanya,ya ajjiyeshin sannan ya wuce gida shima.
Tun k'arfe takwas da rabi duka yaran sukayi bacci,ta kwashesu ta kaisu dakinsu ta kwantar dasu,ranta a jagule,kishi fal ranta,zuciya nata mata saqe kala daban daban kan inda ya tsaya din,don ba kasafai yake kaiwa dare haka a waje ba,koda zaikai din yana kiranta ya gaya mata zai kai dare din,tunda babu ta yadda aikinsu baya kamawa.
Dakinta ta wuce bayan ta rage hasken falon,tanaso qwarai tayi wanka amma kuma tana gandar zuba ruwa a jikinta,saita zarme da zama gefan gadonta kawai taja wayarta ta fara chart.
Batasan lokaci ya ja haka ba sai data ji qarar shigowar motarsa,ta sauke wayar tana duba lokaci,sai taci gaba da chart dinta,don tasan yawanci bai fiya dawowa shi kadai ba,kuma idan hakan ta kasance sai ya sallamesu kafin ya shigo cikin gidan.
Duk da yasan babu lallai ya samu kowa a falon amma bai fasa yin sallama ba,ya dan bi falon da kallo,babu laifi,bai wani kacame can da yawa ba,duk da bai masa tsari yadda rai da zuciyarsa sukeso ba,kai tsaye dakin yaran ya wuce,ya tura qofa ya shiga,wutar dakin tana kunne,yabi yaran da kallo,ba alamun an musu wanka da zasu kwanta bare ayi maganar brush,kowanne cikinsu yana da kayan bacci qasa da kala goma goma,amma bazaice ya gansu dasu sau biyar ba,baima san inda take kaisu ba.
Yadan jima a kansu yana musu addu'ar daya tabbatar bata musu ba,ya shafesu da ita,ya sake gyara musu kwanciyar ya lullubesu sannan ya kashe wutar dakin ya fito yaja musu qofar.
Yana fitowa tana fitowa a nata dakin,kallon kallo sukayi a tsakaninsu,tanason ta karanci har yanzu ranshi na abace ne ko ya haqura?,duk da ba yau suka saba irin wannan ba,yayin da shi kuma yake kallon dressing din jikinta,kayan daya fita ya barta ne dasu,wanda tun safe suke jikinta,duk da yalwar suturu da take dasu masu tsada da kyan gaske,to amma fa idan ka gansu a jikinta wani babban sha'ani ya tashi da zata shiga dangi ko qawaye tayi bajinta
"Sannu da zuwa" ta fada tana dan basarwa"
"Yauwa,ya gida ya yaran?"
"Alhmdlh" ta amsa masa tana mamaki,a yadda ya fita bata taba kawo saukarsa a nan kusa ba,amma sai taga kamar babu abinda ya faru
"Anan zaka ci abincin naka?" Ta tambayeshi sanda taga yana takawa yana barin wajen
"Zan danyi wanka,kamar nan da minti goma ki kawomin sashena" dan yatsina fuska tayi can qasan ranta tana mita,bayan wahalar girkin da tasha kuma sai ya sanyata wahalar diban cooler din abinci ta bishi dasu?,me yasa bazai zauna a nan yaci ba?,bata amsa masa ba har ya fice,sai ta juya ta koma daki abinta taci gaba da charting dinta.
Da sauri ta miqe sanda taji agogi ya buga,minti goma sai data ninkasu wajen sau hudu,ta qara ya zama minti arba'in da kusan biyar ba tare data ankara ba,ta jefa wayar gefe ta miqe tana gyara daurin dankwalin atamfar dake kanta sannan ta fito tana gyara daurin zaninta daya dangale tana qoqarin daidaita tsahonsa.
Har ya gama shirinsa tsaf ba ita ba alamunta,ba wani yunwa yake ji ba ya riga da ya take cikinsa wajen hajiyarsa,don haka bai wani damu ba can,dama kuma idan da sabo ya riga ya saba,sai ya dauko luggage dinsa ya fara shirya kayan da zai tafi kaduna dasu.
Ya gama hadasu tsaf ya debo wasu takardu nasa yana dubawa,sai ya koma kan sofa dake dakin ya zauna yana dubawa cikin nutsuwar nan tasa.
*_RIGIJI GABJI!_*π₯π₯
*_WANI KAYA SAI AMALE_*π₯π₯π₯
*FITATTUN ZAFAFAN DA BABU NA BIYUNSU*π₯π₯
*JERIN GWANON LITATTAFAI ABOKAN TAFIYAR JUNA MASU MABANBANTAN LABARAI DA FASAHA*
*_'YAN BIYAR DIN NAN NE FA_*
*_SARAKAN LABARUN_*
*NISHADI*
*CAKWAKIYA*
*GWAGWARMAYA*
*BARKWANCI*
*TSANTSAR DARASIN RAYUWA*
*TARE DA*
*ZAZZAFAN SALO NA SOYAYYA MAI RIKITA TUNANI DA TSUNDUMA MAI KARATU CIKIN TAFKIN SHAUQI*
*SUN SAKE SHIRYAWA TSAF,DAUKE DA WANI TARAGO MAI CIKE DA LABARAI MASU ZAZZAFAN ZAFI!!!*
*KIN SHIRYA MADAM?*
*MAZA ANTAYA NAKI KUDADEN KIBI SAHUN AYARIN MATA MASU AJI TA HANYAR BIYAN KUDIN NAKI KARATUN WADAN NAN LITTAFAI KAMAR HAKA*
*DAUD'AR GORA* Billynabdul
*KI KULANI* Missxoxo
*IDON NERA* Mamuhghee
*RUMBUN K'AYA* hafsat rano
*A RUBUCE TAKE* Huguma
*ZAKI IYA BIYA KAI TSAYE TA WANNAN ACCOUNT DIN*
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiki tura shaidar biyanki ta wannan number
09033181070
*MASU TURA KATIN MTN KO VTU KUMA ZASU TURA WA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANSU*
09166221261
*Muna godiya da ci gaba da zabin zafafa biyar a koda yaushe*ππΎππΎ
*Arewabooks:huguma*
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Page 15
Qwayar idanunsa ya daga kan takardun yana dubanta sanda take shigowa dauke da kwanukan,ya sauke boyayyar ajiyar zuciya yana qarewa dressing dinta kallo,baisan sai Yaushe hafsat zata canza ba,baisan me zaiyi da zai canza ta ba,duka wani burinsa a kanta ya dade da tarwatsewa,wani lokaci sai ya dinga gani kamar ba hafsat dinsa ba.
A gabansa ta ajjiye abincin sannan ta koma gefansa ta zauna tana maida idanunta ga takardun da yake dubawar shima
"Ga abincin" ya daga takarda daya yana juya bayanta ba tare da ya kalleta ba
"Shi zai zubamin kansa da kansa?" Jim ta danyi sannan ta tabe baki,wani lokaci ya fiya jin kai da izza,hutsu ne na gaske,sai yayi kamar ya sauko ko ya canza sai kuma ya sake hargitse mata,ita kanta tana sarawa kanta yanda take haqurin zama dashi,sai ta sauka tana zuba masa ta ajiiye gabansa tana komawa mazauninta.
Sai daya qara minti kusan biyar sannan ya ajjiye takardun ya sauko,tana ta satar kallonsa,tana son masa maganar motarta data fara bata matsala tana shakka,dazun sun rabu ba ta dadi ba,yanzun kuma taga yana hada kaya,ta tabbatar kayan tafiya KD ne,wala'alla ya haqura ne ya janye qudurinsa?,idan hakanne ita tafi mata nono fari,saidai tafi kowa sani,shurunsa bashi da sauqi,mataki ne zai dauka daga baya ta ruwan sanyi,koma dai yaya ne idan har ya janye din shikenan its buqatarta ta biya,a hakan ta daure dai tayi gyaran murya kadan.
Ya jita sarai yayi kamar baiji ba,sai data gaji da gyaran muryarta sannan ta magantu
"Wai kayan tafiyar kake hadawa?"
"sune" ya bata amsa a taqaice
"Allah yasa a koma a sa'a,mudin ko weekend ma dinga zuwar maka,kaga bazai shafi karatun mimi ba" ta fada har qasan ranta tana jin ta fada ne kawai don ta wanke kanta,bawai don zata iya wannan jigilar ba
"Yayi" ya amsa mata a taqaice kawai,don baison doguwar magana.
Shuru ya sake ratsa tsakani,tana ta tauna yadda zata gaya masa zancan motar,don so take kafin bikin qawarta din nan ya sauya mata,taje a hajiyar ta da sabuwar mota,ba wannan qaramar motar da kowa ya sanya da ita ba
"Nace ba" ta fada a darare
"Uhmmm,kikace me?"
"don Allah ba.....abban mimi motata...wallahi matsala take ta bani,sannan ma tayi tsufa da yawa,kada kunya na dinga shigarta bayan mutane sunsan matsayinka" shuru kamar bazai amsata ba,yaci gaba da cin abincinsa,yayin data kasa ta tsare ta kafeshi da idanu tana jiran ta cewarsa,har sai data gaji da jiran amsa ta sake magantuwa
"Bakace komai ba abban mimi" plate din hannunsa ya ajjiye,ya waiwayo ya dubeta
"Bani da kudi a yanzu" fuska ta dan bata
"Abban mimi baka da kudi fa kake fada?,ko allowance dinka ya isa ka canza min babbar mota bama qarama bafa"
"Kudina a yanzun bana canza mota bane,ina da abu me muhimmanci da ya fishi" daga haka ya miqe yaci gaba da aikinsa hankali kwance,cikin bacin rai taci gaba da zama wajen,tana ta baqin rai ita kadai,zantukan yayarta take tunawa
"Kada fa kiga mijina ya canzamin mota ki dauka kema wannan mijin naki me ra'ayin riqau zai canza miki mota ta sauqi,mafi kyau ki haqura da maganar zancan mota yanzun,nasan halinsa sarai ba canza mikin zaiyi ba" a sannan baki ta tabe tana dan kada qafarta
"Kiyi haquri umman walida,amma banjin yadda abbas ke kashemin kudi da yadda yakeji dani kina samun haka wajen baban walida....."
"Ke kinga dakata,karki gayamin baqa mana" ta dakatar da ita,duk da cikin wasa suke maganar
"Kowa ya san abbas yana jiqaki,amma kuma duk cikinmu babu wadda juya miji ke mata wahala irinki koba haka bane?" Ta fada tana duban sauran sisters dinta dake wajen,dariya suka danyi suna gasgata maganar maman walida din da suke kira da anty balaraba,wannan ya hasalata,ta kuma ci musu alwashin kawo sabuwar mota don ta nuna musu ta isa da mijinta kamar kowacce mace.
Har yaci qarfin aikinsa tana zaune a wajen bata sake tofa tata ba,ta tattara fushin duniya ta azama ranta,me yasa koda yaushe abbas din sai ya kunyatata yakejin dadi?,kafin ya kammala aikin ta tattare tabar masa wajen,sai kawai tayi komawarta sashenta,tayi kwanciyarta acan.
Shima daya gama komai kwanciyarsa yayi,bai wani tsaya bi ta kanta ba,bayason rainin wayo da kuma rashin hankali,ta kuma fi kowa sani abinda baya tolerating kenan.
Washegari haka tayita kumbure kumburenta,sai ya nuna baisan ma abinda takeyi ba,ayi masa laifi kuma a fishi fushi?,yayita hidimarsa da yaransa,yana kuma yin breakfast ya shirya zai fita,mimi ta maqale masa sai ta bishi,ya kaita gidan hajiya,hafsat din nata danqara masa mata harara amma yarinyar batasan tana yi ba,ya shiga dakinsu ya shiryata da kyau cikin sabbin kayanta dake danqare a cupboard ba'a sanya musu,baisan uban me takeyi da kayan ba,yasan dai wani lokaci takan diba ta rabar,duk cikin fariya da alfaharin shi din wuyansa ya isa yankan da yake danqaro musu suttura ya ajjiye.
Yana fita ta bishi da tsaki ta kuma miqe abinta saman doguwar kujera tana gunaguni,duk yadda take sonshi yana sanyawa yana fita a ranta gaba daya,bata isa ta sashi yayi abu ba sai abinda yayi niyya ya kuma tsarama kansa,kallo ta kunna abinta tana daga kwance,nawwara da yau suka samu albarkar wanka tun safe tana ta kaikawo tana wasanta qasan carfet,har bacci ya dauketa ta bingire a nan.
Har biyu ta buga tana kwance tana kallo bata da niyyar tashi ta kintsa gidan,sai da taji sallama daga qofar falo sannan ta miqe tana sauke qafafunta qasa.
"Anty ummee,ni banma dauki murya ba wallahi"
"Ina zaki dauka kin tasa tv a gaba" ta fadi tana duqawa ta dauke nawwara daga qasa ta maidata saman kujera sannan ta zauna daga gefanta tana cewa
"Yanzun da banzo ba a qasa zaki barta har tayi barcinta ta tashi" baki ta tabe,bacin ranta da ya dan lafa yana motsa mata
"Hmmm,a qufule nake anty ummee,ubanta yaja mata,shi ya qunsan takaici"
"Ke kam damuwarki da abbas bata qarewa,gashi dai baki rasa komai ba amma ko yaushe cikin complain?"
"Na rasa ya zanyi dashi anty ummee,dan bada umarnin nan da mata kewa miji ni bansanshi ba" baki ta tabe tana jingina sosai da kujera
"Ke kikaso hafsa" bata motsa daga wajen ba ta zayyanewa anty ummee din komai,itace wadda take bi a dakinsu,uwarsu daya ubansu daya,sai data gama tas sannan ta dubeta
"A cikin banza ma ke banza ce wallahi hafsat,ke ko asiri kike fa saikin hada da kissa da kisisina yake ci maka yadda kakeso,ke dan makircin nan na mata ma ace baki iya ba?,ko da yake ko an doraki ma sauka kike" ta qarashe maganar tana yaada kanta gefe cike da takaicin 'yar uwartata.
Matsowa tayi sosai kusa da ita
"Zanyi wallahi anty ummeee" sai data qare mata kallo sannan ta zauna sosai tace da ita
"Ki tattara kayanki ki bishi kaduna kamar yadda yakeso,yaran idan ta kama ko gida ko hannun hajiyarsa basai ki barsu ba?,bama mimi bace ita kadai?,idan kuka tafi can daga ke saishi,ba 'yan uwansa akusa ba 'yan sanya idanu,Allah ne kadai yasan nawa zaki tatsa daga jikinsa,masu aikin damarar nan fa ba qaramin iya soyayya sukayi ba,amma ke gaba daya komai naki a rikice?ki bishi ki kwantar da kai,dadin yadda kika faranta masa ma wallahi baisan sanda zai sauya miki motar ba babu wanda yaji ba wanda ya gani" Fuska ta bata,don ta dauka wata mafitar zata bata ba wannan ba,sai itama anty ummee din ta zuba mata idanu tana dubanta
"Ba zakije ba kenan?" Cikin tsuke fuska tace
"Ni anty ummee,kaduna fa wa na sani wa ya sanni?"
"To ai shikenan saikiyita zama bauchi ki tsanana uwar da zaki tsinana" ta fada tana buga cinya. Shuru tayi na wasu sakanni tana nazari,yayin da anty ummee ke qarewa qawataccen falon nata kallo yadda ta barshi komai a zaune da duwawunsa,babu tsari bare kintsi
"Shikenan anty ummee,an gwada aiki da shawarar taki,zanje"
"Yadaifi miki" ta bata amsa sannan ta maido dubanta kanta
"Yanzu kika tashi a barci ne wai?" Kai ta girgiza tana dubanta
"A'ah,me kike gani?"
"Bakiji bashi bashin da jikinki yakeyi ba?,sannan wannan uwar bolar da kika barwa falonki ta mece?" Shinshina jikinta ta soma yi,sannan ta bata fuska,don ita bataji komai ba
"Ni ba abinda jikina yakeyi,hancinki ne dai,falo kuma wallahi yara ne suka bata su da ubansu kafin su fita,don jiya da daddare fes na shareshi kafin na kwanta,yanzu kuma ina shirin tashi na sake gyarawa kika shigo"
"Allah ya sawwaqe" kawai tace da ita,tasan halinta ba yau ba ba jiya ba,koda ta tsaya gaya mata qarancin tsaftarta ma uzurin yara zata yita kawo mata,kamar ita tafi kowa haihuwa a duniya.
Suna taba hira tana gyara falon har ta gama,ta shiga kitchen tana tunanin me zata dafa harda abbas din,don ba zata iya girki biyu ba,tayi yanzu tazo tayi musu na dare?,sai kawai ta dora.taliya da miya,suka wuce uwar dakan hafsat din anty ummee na sake jaddada mata muhimmancin binsa kadunan,tare da dabaru na kissa na yadda zata samu yadda takeso.
Ita ta tayata suka hada kayanta dana yara,don tasan iya wannan sai ya zame mata aikin gabas,cikin kayan nata taga wasu night gown,tasan kudinsu saboda ta gansu wajen wata qawarta kwanaki da tayo order dinsu
"Kai....wadannan nighty din fa?"
"Sunyi kyau ne?" Ta amsata tana zuge qaramar jakar data zuba undies dinsu
"Sosaima,ke bakisan kudinsu ba?" Baki ta tabe
"Bana ce ba gaskiya,shi ya siyomin su kwanaki,ni kuma Allah ya gani bazan iya sanyasu ba,kamar waga kafira,shi yayita wani aiki kamar dan iska dan iska,ko kunyar yaranshi biyu baya ji" galala anty ummee ke kallon hafsat din,idan tayi wani abun kamar batayi karatu ba,ita yanzun just shekara ashirin da takwas zuwa da tara har tayi tsufan da bazatayi gyara ba?, Amma da yake itama kayan takeso sai bata bata shawarar komai ba,ta ninke abinta ta sanya a jaka,ita tasan darajarsu.
Da ta tashi tafiya ta sake tambayar wasu designers turare da ya siyo mata,guda uku ne,guda biyu dubu ashirin da bibbiyu ya siyosu,guda daya dubu talatin,hakanan yake,mayen qamshi ne,shi yasa baya siyan banzan turare,ko su mimi zai siyawa turare baya siya musu na qaramin kudi,bata damu da su ba shi yasa.batasan daraja ko tsadarsu ba,tace ta dauka wanda takeso,ta kuwa dauke dan dubu talatin dana ashirin da biyun guda daya tayi tafiyarta,dama yawa yawan zuwanta gidan abinda ke kawota kenan,don ta qaru da 'yar uwarta,duk da tana bata shawarwari na gaskiya a wasu lokuttan,rashin daukan shawara ke damun hafsat din,data fara saita tattara ta zubar,tafi ganewa yawan qorafi da kai k'ara.
*_RIGIJI GABJI!_*π₯π₯
*_WANI KAYA SAI AMALE_*π₯π₯π₯
*FITATTUN ZAFAFAN DA BABU NA BIYUNSU*π₯π₯
*JERIN GWANON LITATTAFAI ABOKAN TAFIYAR JUNA MASU MABANBANTAN LABARAI DA FASAHA*
*_'YAN BIYAR DIN NAN NE FA_*
*_SARAKAN LABARUN_*
*NISHADI*
*CAKWAKIYA*
*GWAGWARMAYA*
*BARKWANCI*
*TSANTSAR DARASIN