Showing 3001 words to 6000 words out of 296907 words
Chapter 2 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT
jefa key din a aljihu ya kuma soma takawa yabar wajen.
Da kallo ta bishi tana tabe baki gami da jifansa da harara,har sai da ya bacewa ganinta sannan ta dauke dubanta daga wajen,a hankali take tattare kayan tana maidawa cikin ledar,qasa qasa take magana ita daya
"Wallahi banaso,bayarwa zanyi,ni ba wani aurensa da zanyi,dan iska kawai" dif maganar tata ta yanke,sai kuma tahau zaro idanu cikin tsoron kada wani ya jita,sai data tabbatar babu motsin kowa sannan ta qarasa kwashe kayanta ta kuma fito.
Isowarta farfajiyar gidan yayi dai dai da budewar gate din gidan,qaramar motar qirar 406 ta danno kai ciki,sai ta dakata daga yunqurin isa sassan anty madinan tabi motar da kallo,sai kuma ta saki murmushi har dimple din dake kwance saman kumatunta hagu da dama ya lotsa,saita cilla da gudu gudu sauri sauri zuw wajen motar,cike da zumudi da kuma murna.
Sanda ta isa daura da motar tuni mamallakiyar motar ta kasheta tana yunqurin fitowa
"Anty dina sannu da zuwa" waiwayawa tayi sashen da widad din take tana niyyar dauko jakarta daga back seat na motar
"Widad rigimammiyar ummu,ya na ganki a gida kuma?" Murmushi tayi tana leqen cikin motar da alama akwai abinda take nema
"Anty secondry zamu tafi fa,muma mun zama manya kin manta?"
"Au anyi haka fa,kice zamu sake samun qarin 'yammata cikin gidan namu....."
"Anty wai ina aysar ne?" Ta tambayeta cikin katsar numfashinta
"Gashi nan a daure" ta fada tana nuna mata shi a kujerar dake kusa da tata cikin baby car seat,zagayawa tayi da hanzari
"Don Allah anty kwantomin shi"
"A'ah widad......ke kanki yaushe ummu ta daina goyaki?, barshi yanzu zan fito na kunceshi" bata rai tayi,wai me yasa kullum suke maidata baya,bayan ita kanta tasan girma take?,to idan ma har yanzu yarinyace ita a wajensu me yasa suke mata zancan uncle mahfood?,dole daga bisani anty dina ta ciro yaron ta miqawa widad shi,sannan suka nufi sassan mahaifiyarta tana ankare da widad din.
"Ke kuma wanne tsautsayin ne ya sanyaki daukar yaronki ki bawa wannan yarinyar?" Cewa momma mahaifiyar anty dina bayan shigarsu babban falon sassan nasu.
Kafin anty dina tace komai widad din ta rigata magana
"Momma Allah na iya fa,gash.i nan ma ni na daukoshi tuyn daga parking space" ta fada tana turo baki,wanda ke sake nuni da zallar quruciyarta,abinda ya sake batawa momma rai,taja tsaki tana miqa hannu gami da yunqurin karbar yaron
"Miqomin shi nan,me kika iya?,yarinyar da ko pant dinta har yanzu batasan ta wanke ba" momma din ta fada tana jifanta da harara,zallar quruciya ya hana widad fahimtar kuma,bugu da qari kuma,akwai wata irin wankakkiyar zuciya da take da ita,ba kasafai ta fiya damuwa da abubuwan da suke faruwa cikin gidan ba,duk da ta soma girma,hankalinta ya fara fahimtar wasu abubuwan
"Allah na fara koya momma"
"Naji,jeki da Allah" ta fada tana sake harararta kamar idanunta zasu fado,sai dauke dubanta daga fuskar momma din tana nufar hanyar kitchen dinta.
Wata tsawa ta kwatsa mata,wadda sai data sanyata ta kusa tuntube da kujerar dake gefanta
"Ina kuma zaki?" Ta fada tana fidda idanu
"Wajen Aafiya zani"
"Kiyi mata me?" Ledar hannunta ta daga tana nuna mata
"Kayan kwalliya na kawo mata ta zaba"
"Uhnnnn,salon kije kisa ta bata aikin dana sakata,to zauna nan har sai ta fito,kada ki shiga ku hadu ayimin shirme" narkewa tayi tana duban momma din,da alama tanason ta roqeta ne ta barta ta shiga,tana kuma tsoron tsawarta,don ba abinda ta tsana sama da tsawa da kuma fada.
"Ki barta mana momma,idan yaso tana shiga saita fito kada ta zauna" dina ke fada qasa qasa,saboda tausayi da widad ta bata,waiwayowa momma tayi ta kalleta tana dan juya aysar a hannu kamar zata masa rawa
"Wannan yarinyar?,tsab zasu iya barnatar min da guri,kuma baka da damar yi maya fada balle duka,tunda tana da uwa a bakin murhu"
"Kiyi haquri momma,yanzu zata fito"
"Naji,amma indai ta shiga din duk barnar da tayimin ke zaki biya"
"Na yarda" sai.anty dina din ta daga kai ta dubeta
"Shiga kikai mata kizo na aikeki sassan anty madina"
"Tohm" ta amsa da zumudinta tana shigewa,deena ta bita da kallo,bata fiya yin fushi ba don mutum ya bata mata ko ya tsangwameta,bata sani ba ko tsabar quruciya ce?,ko sai nan gaba zata fahimta komai idan hankali ya gameta?.
*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*
*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥
0022419171
Maryam sani
Access bank
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*_A RUBUCE TAKE!!!_*
(k'addara ta)
Page 03
*MAAB LUXURY HOME*
*_idan kaji gangami akwai labari_*
*_SABUWAR DUNIYA CE_*
*ALFAHARIN UWAR GIDA*
*FARINCIKIN AMARYA*
*MAIDA TSOHON GIDA SABO*
*DUNIYAR QYALE QYALE*
*KAYA NA ALFAHARI DA TAQAMA*
*_Ba iya kyawun idanu suka tsaya ba,harma da ingancinsu da kuma qwarkonsu,ka dade kana mora kana kece tsara a tsakanin tsararraku da sauran mutane_*
*nasan zaku tambaya ina ne nan?*
*MAAB LUXURY HOME*
😊 *Kai daga jin sunan ma babu tambaya*
*_duniyar qawata muku gidajenku ku ganku kamar a wata nahiya ko wata duniyar_*
*Suna kawo kayan kitchen rankatakaf manya da qananu*
*Kayan gado dana parlor*
*Kai...suna kawo kowanne nau'in kayan ado na cikin gida*
*Karkiyi qasa a gwiwa kuma kada kiyi sake ma dafe,maza garzaya ki nemesu a*
_adress dinsu dake No 22 Ahmadu bello way,kano state_
*Ko kuma kuyi order din kayanku kuna daga gida ta shafinsu na instagram*
@maabluxuryhome
*Facebook*
@maabluxuryhome
*Ko ku nemesu ta lambar wayarsu kamar haka*
08034631010
*Kyau inganci da rahusa shine takenmu*😊😊🤝🤝🤝🤝
____________________________
Koda ta shigan bata zauna ba kamar yadda anty deena tace tayi sauri,ta sameta tana yankawa momma albasa,sai zabga gumi taje gami da hawaye,duk da cewa kitchen din kitchen ne irin na zamani,da ya wadatu da iska da manyan windows,dukka a qoqarin momman na koya mata girki,kada ta tashi kamar widad,wadda bata cas bare as a gidan,abinda ya damu wasu cikin gidan,yake kuma basu haushi sosai,suna gajun gatan da ummu ke nunawa widad din yayi yawan da ya kamata ta rageshi ta sanwa wasu cikin jikokinta.
Budewa Aafiya kayan tayi tana cewa
"Zabi duk abinda kikeso a ciki" kanta ta leqa cikin ledar tana cewa
"Ummm,yar gatan ummu,inda nice nace mata ta siyon kayan nan qi zatayi,sai tace naje na tambayi yayuna maza"
"Yaaya mahfood ne nima ya kawomin" daga kai tayi ta kalli widad,dududu itama Aafiyan ba zata wuce sa'ar widad din ba,saidai ta danfi widad din girman jiki kadan
"To me yasa ba zakiyi amfani dasu ba?" Tura baki tayi tana tsuke fuska
"Banaso,ni bana son sa,banason ana min zancensa,ki dauka anty deena zata aikeni" ido ta fidda
"Yaushe tazo?"
"Yanzu" saita ajjiye wuqar tana zura hannu a ledar,ta zabi abinda takeso tana cewa
"Aiko na godde wlh,bari nayi sauri na gamawa momma aikinta na fito" tana dan lila ledar ta fice abinta ba tare data tsaya sauraronta ba,ta samu anty deena a falo,ta bata leda tace ta kaiwa anty madinan,ta amsa ta fice da dan guntun gudunta.
Ta dan samu yaran sassa sassan gidan da dan dama a sashen anty madinan,kasancewarta mai fara'a haba haba dasu da jan kowa a jiki,kowa nata ne,hakanan kowa yana jin dadin xama dasu,bayan sa'anninta masu kamar shekarunta data samu,harda yayyensu da ake dab da bikinsu,kuma suna tare da anty madinan,da alama akwai abinda take koya musu,sauran sa'annin nata suna daga gefe sun buda tasu chamber din.
Bayan ta miqa mata ledar sai ta kalleta
"To wannan dayar kuma fa?"
"Kayan kwalliya ne na kawowa su rafi'ah"
"A ina kika samu kayan kwalliya masu yawa haka?" Basma cikin 'yammatan dake shirin amarcewa ta fada tana dubanta bayan ta dago kanta daga danna wayar da takeyi,kanta tsaye ba kwana kwana ko damuwa tace
"Yaa mahfood ne ya kawomin"
"Shine kuma zaki rabar?" Anty madina ta tambayeta tana bada hankalinta sosai a kanta,kamar zata saki kuka tace
"Banaso anty wallahi,ni banaso"
"Barta don Allah ta rabar,miqomin na zabi nawa" basman ta sake fadi tana miqa hannu,ba wani damuwa tattare da ita ta miqa mata ledar ta qara gaba tana cewa
"Anty basma idan kun gama su na'ima zasu zaba" anty madina data bita da kallo tana kallon zallar quruciya ta saki ajiyar zuciya
"Allah ya zaba abinda yafi zama alkhairi,baaba mahfood dai kam to"
"Uhmmm,wai laifin widad kuke gani?,ni nafi ganin laifin baaba mahfood din ai,kamar maye,yarinya tun tana 'yar tamilo kake faman mata hidima,jikinka da aljihunka basu huta ba,ta fara wayo ta nuna baka so basai ka haqura ba,dui gidan ita dayace 'ya?,ko ita kadai ce jika?" Kai anty madina ta girgiza
"A'ah fa basma,har yanzu widad akwai quruciya tattare da ita,ai ba'asan maci tuwo ba sai miya ta qare"
"Uhmmm,anty madina,yarinyar nan fa daurin gindi ta samu,Allah kuwa,kuma sai yaushe?,bayan mu kadai ne muka haura zuwa SS,mu dinma gashi SS one kawai aure ya tashi,bare su da jikinsu da alama mai saurin girma ne,Allah yasa su gama JS ma"
"Allah ya shiga lamarin" anty madina ta amsa mata
"To Ameen"basman ta fada tana maida kanta ciki ledar,don tuni marwa ummee da nujood suka gama zabar nasu,anty madina nata musu tsiyan girma ya fadi,raqumi ya shanye ruwan 'yan tsaki,su da za'a kawo musu akwati me zasuyi da toshin qanwarsu.
Widad kam bata sake bi takan kayan ba,a nan suka gama gantalewa,duka ta rabar,dan abinda yayi saura ya gangarar dashi anan wajen anty madina,tayi komawarta sassansu.
Sanda ta koma tuni abbanta ya tafi,sai ummu kawai
"Ina kikakai kayan?" Ta tambayeta tana tallafe da kuncinta tana dubanta,maimakon ta amsa saita narke fuska,ta kuma shige cikin kujera abinta ta lafe taba mus mus da baki,juyin duniya ta gaya mata inda takai kayan taqi,dole ga qyaleta,tasan indai cikin gidanne zata ji.
Tun tana zaman likimo har bacci yayi awon gaba da ita,bata tashi ba sai kusan azahar,sanda latifa ta kammala abincin rana,ta kuma tattaro panties da undies din widad din zata wanke.
Sai datayi sallar azahar kamar yadda ummu ta horar da ita,ta karba abinci,saita zagaya baya inda latifan ke mata wankin,ta zauna tana ci suna hira da latifan...
***********
Kamar kowacce safiya a ranakun makaranta,school bus din gidan ke tattara kan duka yaran gidan zuwa makaranta,wanda kusan yawancinsu makaranta daya suke zuwa,wadanda kuma suke mabanbantan makarantu sai ta miqa su sannan ta dawo gidan zuwa lokuttan tashinsu.
Daga can sassan ummu widad ce zaune saman kujera,sanye da sabbin uniform dinta kamar yadda komai nata a ranar yake sabo a matsayinta na dalibar da ta shiga secondry school a ranar,ummu na zaune daga qasan carfet hannunta riqe da plate tana miqawa widad din plantain din ciki
"Maza maza kici kafin 'yan azalzalar nan su biyo sawunki,idan ba haka nayi miki ba haka zaki tafi,yanzun latifa zata kawo miki lunch box dinki" fuska a nake a kuma sakalce take duban ummu
"Wallahi na qoshi ummu,ya isa haka"
"A'ah,qarashe wannan dai" ta fada cikin nuna kulawa,hakanan ba don taso ba ta daga cup din hannunta dake cike da tea tana shanye ragowar na ciki,dai dai lokacin basma ta shigo,sanye take da kayan gida,kasancewar ita din a yanzun sai daina zuwa,saboda kusantowar bikinsu,bawai don sun gama bane,haka al'adar gidan take,alhajin salim mai fata tsoho mai ran qarfe,kaka kuma uba ga ahalin gidan wannan sbine tsarin da ya dora dukka yara da jikokinsa,mutane da yawa 'yan bani na iya da kuma 'yan gaza gani kance
'Gidan me fata ai da wuri suke aurar da yaransu,da sun ga mai kudi sai su cire yarinya daga makaranta,basa ko gamawa,don sunga suna samun masu danshi ne,suma masu kudin da shegen kwadayi,suna ganin kyawawan mata sai su rude' duk da wannan jita jita na dawo musu kunne amma sunyi banza da zantukan mutane,abu daya tsoho kuma dattijon ya sani shine,mutuncin mace dakin mijinta,hakanan duk wadda tayi katari da samun mijin dake da ra'ayin karatu tana ci gaba da karatunta ne cikin dakin mijinta.
"Goyon kaaka,sai a fito ko?,kin tsaida mutane kina bata musu lokaci" ta fadi tana harararta,ganin yadda ummu ta zauna dafa'an tana bata abinci kamar wata yarinyar goye,waiwayowa ummun tayi tana danqara mata harara
"Ke kuma da bake za'ayi tafiyar wa ya sakoki a maganar?"
"Yo fisabilillahi ummu saita makarar da kanta fa makarar da wasu?" Tayi maganar tana miqa hannu gami da fusgar sabuwar school bag din widad din dake ajjiye kusa da ita,kafin su sake cewa komai.muryar dattijon ta ratso falon
"To....to,ya akayi?" Ya fada yana qarasowa a hankali zuwa cikin falon,kafin ya samu waje ya zauna yana dubansu.
Russunawa basma tayi ta gaidashi,dai dai lokacin latifa ta qaraso dauke da lunch box din widad din
"Gashi an gama" ta fadi tana ajewa gabanta
"Ko muje motar na rakaki dashi" latifan ta sake fada tana kuma dauke lunch box din daga gabanta,tabe baki basma tayi sannan tace
"Tabdi!,gigin primary,kina shiga dashi ansan burbushin primary ce,meye hadinki da wani lunch box tsabar sangarta?,Allah latifa ke kike sake taya ummu ana sakalta yarinyar nan" ta qarashe maganar tana hararar widad din
"Wato kedai anyi babbar banza ko?" Alhj salim ya fada yana duban basma
"Allah alhaji bata sanin ta fara girma"
"Wuce ku tafi ga iliya can yana horn" ya fada yana daga musu hannu,sai a sannan widad ta sauko daga kan kujerar,ta maida takalmanta suka fice ummu tana muta addu'ar dawowa lafiya.
Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta tabbatar da fitarsu,ta maida dubanta ga alhj salim din
"Yaran nan sam basu da zurfin hankali,ta yaya zan banzatar da widad ta gaza samun kulawata?,yarinyar da tun tana watanni a duniya mahaifiyarta ta tafi ta barta?,idan ban kula da ita ba waye zai kula da ita?" Murmushi dattijon yayi yana qarashe janye ragowar carbin da ya rage a hannunsa sannan ya ajjiyeshi gefe
"Iya tasu fahimtar kenan,amma duk da haka saboda gudun ci gaba da samun sabani da yadda suke jin haushinta ganin kamar kinfi sonta,kiyi qoqarin boyewa da rage wasu abubuwan"
Dan sunkui da kanta ummu tayi
"In sha Allah" ta amsa masa cike da ladabi,duk da bata da tabbacin yiwuwar hakan.
"Kunun za'a kawo maka ko dumame?"
"A fara kawomin kunun da qosai tukunna" ya amsa mata yana gyara zamanshi sosai saman kujerar,ta yunqura ta miqe zuwa kitchen da kanta,duk da tsufanta hakan bai hanata yi masa tasa hidimar da kanta ba,koda zata bawa latifa tata hidimar tayi mata,amma ta alhajin ita keyi.
Awannin da tayi a makaranta a ranarta gane banbamcin secondry school da primary,sosai makarantar tayi mata dadi,lokacin tashinsu da yayi tun a cikin motar suke hayaniya,labarin sabon aji da kuma sabuwar makaranta
"Don Allah kuyi mana shuru,kun cika mana kunne ha'an" ramziyya wadda take cousin a wajen widad ta fada,ita din gaba take dasu,don a qalla ta basu shekara kusan biyu,ita dinma wannan shekarar ta shiga js three,kuma akwai yiwuwar shekara mai zuwa a karba kudin aurenta kamar 'yan uwanta,dole suka rage hayaniyar,saita maida hankalinta ga iliya driver
"Ko ka wuce damu gidan baaba mahmud?,muga lefen najwa tunda yau babu islamiyya"
"To shikenan,babu laifi" ya amsa mata.
Kicin kicin widad tayi,ko kusa ko alama bata qaunar zuwan gidan nasu,koda hutun makaranta akayi kuwa,gidan ba gurin zuwanta bane,zata iya cewa banda mahaifinta bata da kowa a cikinsa,sai yayanta wanda.ba kasafai kake samunsa cikin gidan ba,yawancin lokutta yana makaranta,duk da yadda mahaifinta ke nacin ta dinga zuwa din amma ummu ta hana,idan ta kama saidai ta wuni ta dawo.
Tun daga harabar gidan matan gidan suka fara jiyi hayaniyarsu,babu wadda ta motsa,don kowacce dan data haifa kadai shine nata,har suka qaraso cikin ainihin babban falon gidan
"A'ah,kada dai kucemin daga makaranta kuke?" Ta tambayesu tana tafa hannuwa cike da yaqe da kuma riya,saboda mai gidan na nan,daga inda yake din kuma zai iya jiyo komai
"Ga alama kuwa umma" najwa dake fitowa daga dakinsu ta fada tana dariya gami da qoqarin daura dankwalinta
"Lefe mukazo gani" widad ta fada tana dan dariya,ganin yau yau umman ta sake mata fuska,ramziyya ta harareta
"Shegen son kallon kayan lefe,caraf ta bada amsa"
"Da gaskiyarta,gaba su za'a kawowa ai" umman ta amsa bayan ta qwalawa me aikinta kira kan ta zubo abinci, murmushi widad tayi maganar tana bata mamaki da dariya,yanzun wataran itama sai a ciko akwatuna da kayan lefe ace nata ne?.
A nan suka ci abincin rana suka kuma baje suka kalli kaya son ransu,alhaji mahmud ya fito a shiryensa,suka hau gaisheshi ya amsa musu cikin fara'a da jin dadin ganin 'ya'yan 'yan uwansa,ya bisu da kyautar dari bibbiyu sababbi,duka harda widad din bai banbantata da kowa ba a cikinsu,sannan ya fice yabar gidan.
"Ni kunzo a dai dai ma,ku taimakamin na fidda kayan da zan kai dinki" ramziyya ce ta dinga tayata zabin,widad na hade mata su waje daya
"Basuyi yawa ba wadan nan kayan anty najwa?, duka zaki kai dinkin?" Inji widad dake zaune daga gefe
"Saina ma qara wasu,kin manta haka amare keyin dinki da yawa?" Kai ta jinjina kawai tana ci gaba da kallonsu,bayan sun gama najwa tace
"Ki kwana anan widad,saiki rakani nakai dinkin,gobe saina maidaki gida".
Cikin murna da zumudi ta amsa da to,ko ba komai zata yita kallon kayan lefen dake burgeta sin ranta,don haka ta baiwa su Aafiya jakarta suka wuce mata gida da ita.
Sanda ummu taji shigowarsu sai tayita sanya idanu taji shigowar widad din amma shuru,har ta gaza daurewa ta aika latifa sassan