Header Ads
Showing 162001 words to 165000 words out of 193443 words

Chapter 55 - ZAIN ABEED Book 1 Complete Document by Nimcey luve Sarauta .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

ba kamar na Jaan ɗinta ba ƙatoto, da sauri ta zame jikinta suna haɗa Idanu da Junaid tayi saurin matsawa gefe, tare da nufar part ɗin ta, kanta a ƙasa a haka take tafiya karo tayi da Mutum, a firgice ta ɗaga kanta tsaye ta gansa sanye da farar jallabiya hannunsa na zubar da ruwa alamar Alwala yyi, idanunsa ta kalla ƙirjinta ya buga sbd wani mugun jaa data ga idanunsa yyi bata taɓa ganin idanunsa sunyi irin Wannan jan ba, fuskarsa ma tayi jajurr, tsaye tayi kawai tana Kallonsa shima Kallonta yake domin tun ƙwala ihun Naila na farko ya fito, yana fitowa kuma ya ganta kwance jikin Junaid, idanunsa ya ɗauke a kanta gently kuma ya ɗura hannayensa a kafaɗarta tare da matsawa sosai har sai da tayi ƙara kana ya matsar da ita gefe yyi shigewarsa, da Idanu ta bisa haka kawai taji kamar bata kyauta ba, jiki a sanyaye ta nufi part ɗin ta.... Bayan an idar da sallah Abeed ƙin shigowa gidan yyi sbd kada yaci karo da Junaid, duk da cewa it was an accident amma ya ƙara jin haushin Junaid fiye da baya... Mai martaba dake zaune a Parlo cikin farar jallabiya irin ta Abeed sai Ƙamshin Hugo boss yake shima, idanunsa maƙale cikin farin Glass ya kalli Sarah dake sanye da hijab, a hankali ya kalli Junaid ya kalli Yarima Yashim sai kuma ya juya ya kalli Zain a nutse yace "Ina warin naka?" Zain yace "Oops, yace basai ya zo ba duk abinda ta yanke is okay for him" Mai martaba ya jinjina kansa kana ya kalli Sarah da kanta ke ƙasa yace "Me kika yanke?" Shiru tayi Junaid ya kafeta da Idanu haka Yaa Yashim kasa Mgn tayi, Sairah dake zaune a hankali tace "Common Biyuni.." Du'a ma Kallonta take Amma idanunta akan t.v Ummi da Riya ma suna Kallonta, Mai martaba ya sake tambayar ta kamar zatai kuka haka ta ɗago kanta ta kalli Junaid, kana ta kalli Yaa Yashim a hankali ta mayar da Idanunta saman photon Abeed dake maƙale a parlon, duk da bata da tabbacin shine ko kuma Zain, amma ydda Zuciyarta ke bugawa tasan photon sa ne, clamly tace "Zan zauna da Uncle Abba.." Mai martaba yace "Waye Uncle?" Ita dai tai shiru bata jin zata iya faɗin sunan Abeed, Murmushi Mai martaba yyi kafin yace "Kina son sa ne?" Naila ta rafka salati tace "Yau naji masifa, wannan ai sai nace baƙin ciki kakewa Shalale, to a gsky duk wanda baya son auren nan sai nayi addu'a Allah ya kashe sa Uban kowa ya huta, wlh sai Mutum ya mutu kuma aure ya zama har abada, Nan nan ƙawata wani ruɓaɓɓe ya hana ta auren wanda take so, ai kuwa ya faɗi ya mutu akai aure kuji na faɗa muku, haihuwar farko ƴan biyar ya haifa Masa, Mai Ƙarya a ƙona shi a wuta, yanzu shekarar su ɗari ciff dayin auren fa, kunga kuwa Aure yyi albarka" Kallon Naila Zain yyi He wanted to stop himself from laughing, amma ya kasa yyi Murmushi yace "Lallai fa" A karo na farko Mai martaba ya kalli mahaifiyar tasa yace "Fiction story... But interesting" Naila ta tsuke baki tace "Ohhhu dai... Wlh ba dani kke ba mene haɗi na dakai to?" Zain yyi Murmushi yace "Back to business" Riya tace "Abba ko Yarima Yashim take nufi tunda dashi take Soyayya ko?" Naila ta riƙe baki tace "Rariya yaushe kika zama haka, Tab duniya mai yayi to ni dai ba zance komai ba" Zain ya kalli Riya yace "Abeed shine Uncle ɗinta, kuma mahaifi ok?" Mai martaba yaja numfashi yace "Yarima kayi hqr, and you too Junaid" Ummi tayi Murmushi tace "Ma sha Allah, Abeed Allah ya riƙa, amma Abeed nada ikon riƙe mata biyu fiye da haka ma" babu wanda ya kula Ummi, Zain ya miƙe suka haɗa Idanu da Du'a, kana ya kalli Sairah yace "Excuse me Maa" Sairah tayi shiru sai kuma ta miƙe tabi bayansa Du'a ta bisu da kallo, Abba da Naila suka bar parlon haka ma Du'a, Riya da Ummi suka bi Sarah da kallo, Amma ma tashi tayi ta bi bayan Mijinta, waje ya rage daga Sarah sai Junaid da Yarima Yashim, Yaa Yashim nata zaune can dai ya miƙe ya fita.. ganin haka yasa Sarah ta miƙe tana ƙoƙarin barin wajan Junaid yace "Sarah..." Cak ta tsaya Zuciyarta na bugawa a hankali ya Ƙarasa inda take yana binta da kallo kafin yace "So kin zaɓi Abeed matsayin miji kenan?" Da mmki take kallonsa yace "Sbd ya baki Kidney, right?" Sarah na binsa da kallo tace "ba iya kidey ba, rayuwa ya bani ai?" Junaid ya ware idanunsa yace "Ohh i See, but you're mistaken" Sarah kallon rashin fahimta ta kewa Junaid, Junaid ya matsa very close to her tana ƙoƙarin jaa baya yyi saurin riƙe hannunta yace "listen to me for God's sake, Believe what I'm going to tell you, I'm a doctor, ina cikin wanda sukai maki aikin Kidney" Sarah ba tace komai tana ta ƙoƙarin ƙwace kanta tace "Ka cikani Malam, banso" Ganin zata kwace Junaid yyi saurin janta corridor tare da rufe mata baki, rungometa yyi sosai a jikinsa yace "Abeed is not the one who gave you kidney... Trust me Sarah, Abeed ya raina maki hankali ne sbd ya sameki, i mean ur virgin, after that, he has no choice wanda ya shige ya aureki, sbd kada sunansa ya ɓaci,He is a singer that the world is proud of, tayaya kike tunanin zai bari asan shine yyi maki fyaɗe har kika samu ciki? One thing you don't know is ciwon haukansa yasa duk sarakuna suka hanasa auren ƴar ƴansu, Abeed mahaukaci ne, a yanzu zai Maki mugun duka a yanzu zai ce bai san yyi ba, may be bayan ke akwai yaran daya ɓata babu adadi" Sarah nan da jikinta ya ɗauki rawa ta kasa yarda da Abinda Junaid ke faɗa, wani ɓangare na Zuciyarta na son gasgata hakan, Ganin kamar ya fara samun nasara kuma ya ƙi bata damar motsawa sbd rungometa da yyi, a hankali ya zaro Wayarsa tare da shiga gallery, wani waje ya shiga photo nan Sarah suka bayyana tana kwace gadon asibiti ga Junaid a gefenta riƙe da hannunta yana saka mata drip, Murmushi Junaid yyi tare da nunawa Sarah Wayarsa yace "Look, nine wanda na baki Kidney ba Abeed ba.....




Zain Abeed isn't free it's 500 via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank via 08119237616 for evidence.... Dan Allah a daina fitar min da book😥 Iphone 13 nake son siya....


***********66*******


Saukar maruka Junaid yaji a saman fuskarsa, wanda ya gigita ji da ganinsa, wanda ya sanya yyi saurin yin shiru ba tare daya shirya ba, zafin marin da Sarah tayiwa Junaid,the reason why he stopped saying what he intended to say,He never thought she could say such a terrible thing to him, balle mari. kallon ta kawai yake kafin ya janye jikinsa daga gareta cikin damuwa yace "Ni kika mara? Have you absolutely lost ur mind Sarah?" Wani Murmushi Sarah tayi kafin tace "You have not seen anything, if you are going to get involved in something that has nothing to do with you, ka fita sabga ta data Mijina, ko an faɗa maka sbd kidney nake son sa? I love my husband, because he is my happiness, the father of my children, Age is just a number ni ba Shasha bace" idanun Junaid ya kaɗa yi jaa babu wanda ya taɓa marinsa a duniya sai Sarah, gashi zafin hannune da ita, cikin wata Muryar yace "I love you Sarah, even before you grow up, ki tausaya min dan Allah..." Frm head to toe Sarah ke kallon Junaid, kafin tace "My husband has good looks, money, knowledge, connections, and a good heart, ya fika komai" tana faɗin haka ta juya idanunta cike da hawaye ta nufi part ɗin ta, Abeed dake can tsaye a bakin ƙofa, bai san meke faruwa ba, haka kuma sam baiji abinda suke faɗa ba, yadai ga Sarah tsaye sai kuma ta taho, yyi baya da sauri, ba tare daya bari Sarah ta gansa ba, Junaid ya daɗe tsaye kansa har sarawa yake sbd marin Sarah ga Mgnar data faɗa masa, tayaya Abeed zai fisa kyau? The thing will never be impossible, dole ya nemu mafita,the solution that will make Sarah become his wife, waje ya nufa idanunsa rufe yana cikin tafiya yaji ance "Heyyy You.." tsayawa yyi Muryar kaɗai ta isa tasa yasan waye mai mgnar, walking slowly Abeed ya Ƙarasa kusa da Junaid fuskarsa kamar kullum a kame, wani kalar kallo ya kewa Junaid kafin yace "Stay away from my wife Junaid Abdullahi Abbas..." Junaid yyi Murmushi yace "Ko? Har taƙama kke Sarah matar kace?I will assure you that I will separate you from her, na aureta" Abeed ya shafa kansa yana sakin Murmushi kafin clamly yace "If you separate me from her, zan bar maka ita har abada,I gave you seven days" Junaid yace "Ni kuma zan tabbatar maka da hakan kafin cikar sati" Abeed ya ware hannayensa tare da ɗaga shoulders without worry yace "All d best.." yana faɗin hakan ya juya yabar Junaid tsaye bakinsa buɗe, Junaid ya jinjina kansa tare da shigewa part ɗin su.... Sarah na shigewa part ɗinta ta faɗa kan bed tare da fashewa da kuka, tun ɗazo kuka ke son kwace mata amma ta hana kanta yin hakan,cikin kuka tace "Why, why Uncle?" Sai kuma ta ƙara rushewa da kuka time ɗin data tuna yana shaye-shaye, Abeed dake tsaye bakin ƙofar bedroom ɗin ta cikin part ɗin yyi ƙasa da murya yace "Open d door Sarah..." Tana jin muryarsa ta ƙara rushewa da kuka Zuciyarta nayi mata zafi, maganganun Junaid nayi mata yawo a Zuciyarta, jin kukanta yyi yawa yasa Abeed yin ƙasa da murya yace "Open d door or else..." Cikin kuka Sarah tace "Bana son ganinka, Ban son ganinka betrayer..." Dam! Ƙirjin Abeed ya buga da ƙarfi cikin breaking voice yace "Betrayer?" Shiru tayi masa tana ci gaba da kukanta wanda kuma kukan da biyu take yinsa, bata jin duk abinda Abeed zai aikata zata iya rabuwa dashi, kawai zata koya masa hankali ya dawo cikin hankalinsa, muryarsa na rawa kamar ba Abeed ba yace "Please better half, sbd Allah da abinda yake cikin ki... Please Maamaa" tayi masa shiru sai shassheƙa take Abeed rasa ydda zai yyi, Sarah na neman rusa masa tunaninsa ya jima da sanin ita ce rauninsa, amma mene ya sa ta zaɓi ta ɗauki matakin haka, juyawa yyi dafe da kansa wanda yake jin yana Sarah masa, da ƙyar ya Ƙarasa parlo tare da kwanciya saman 3seater... It was not long before he went to the parlor, Zain ya shigo cikin parlon sanye da nightwear masu kyau da mmki yake kallon Abeed kafin ya Ƙarasa wajan deep frizeer ya ɗauki gorar ruwa guda biyu masu sanyi, wajan Abeed ya ƙara yace "Our water supply has run out, shine nazo nan... What's up na gnk a nan? Where's your wife?" Abeed idanunsa Lumshe ba tare da yace komai ba, ganin yadda ƙirjin Abeed ke ɗagawa yasa Zain clamly yace "Me tayi mk?" Sai a lokacin Abeed ya buɗe idanunsa da yyi mugun jaa sosai ya kalli Zain a hankali yace "Wa?" Zain yace "wawa, bbu ydda za'ai ba tare da wani abu ba kazo Parlo k kwanta" tsaki Abeed yyi bai ce komai ba, Zain yyi dry yace "Yaro ya fara shiga tarkwan mace" still Abeed bai kula Zain ba, hakan yasa Zain yace "Night,matana na jira na" sai da Zain yaje bakin ƙofa Abeed yace "Do u have any spare key?" he said in a worried voice, Murmushi Zain yyi yace "No, i don't.." yana faɗin hakan ya nufi part ɗin sa, Abeed kasa Bacci yyi He spent the night in her thoughts... Cikin dare zazzaɓi ya ishi Sarah ga wata yunwa da kwaɗayin fruits daya taso mata, bakinta sai rawar sanyi yake, a hankali ta murɗa key ɗin jikin ƙofar ta fito ko kayan jikinta bata sauya ba, amma ta cire hijab ɗin, a hankali take tafiya without making any sounds da zai nuna tana tafiya, gashi parlon duhu tana zuwa tsakiyar parlon taji an rungometa ta baya, baki ta buɗe zata ƙwalla ihu yyi saurin rufe mata bakin da hannunsa, a hankali ya jata can wani corridor, yana zuwa corridor ɗin ya kunna hasken wajan, Kallonta yyi ta rufe idanunta gam! A hankali yace "Me nayi maki?" Ita tai masa shiru taƙi cewa komai, yace "Na mki wani abu?" Still shiru tayi masa taƙi yarda ta kallesa yyi ƙasa da murya yana ɗago haɓarta yace "Look at me Saraahh.." ƙwace fuskarta tayi ya ƙara kamo fuskarta kamar jira take ta fashe masa da kuka, kwantar da kanta yyi a kiransa he couldn't feel ydda hawayenta ke jiƙa masa ƙirjinsa, shiru yyi Still holding onto her muryarsa a taushashe yace "I am sorry... Sorry wify" kukan ta kawai take rera masa yana patting bayanta yana jin ydda jikinta ya ɗauki zafi, clamly yace "Tell me now, me nai mki?" Ta girgiza kanta sai kuma ta fashewa da kuka tace "Daddy zani" ta faɗa tana kwaɓe fuska kamar baby, da Mmki yace "Daddy?" Ta ɗaga masa kai, sai kuma tace "bana son zama dkai Daddy zani" da sauri Abeed ya ɗago kanta yace "da nine baki son zama?" Ta ɗaga masa kai yyi ta Kallonta kafin a raunace yace "Kiyi hqr dan Allah...." Ita dai kuka kawai take ta kifa fuskarta a ƙirjinsa ƙamshin na ratsa hancinta, a hankali yace "Ok, idan na kai ki zaki bar kukan?" Ta ɗaga masa kai tace "Eh zan daina, amma kada kazo inda nake bana so" kasa ce mata komai yyi yana jin wani abu mai kama da tsoro zame ta yyi daga jikinsa yace "Jeki kwanta" ta maƙale kafaɗa yace "What?" Tace "Indomie zanci" baki sake yace "At this time?" Tai masa shiru tana ɗauke kanta can ya numfasa gaba ɗaya ya gaji bakinsa sai ciwo yake ya manta when last da yyi Mgn mai tsayi hk, yace "Ok muje kiyi" ta kwaɓe fuska tace "bana son ƙarnin ƙwan.." ya zaro idanu waje a Zuciyarsa yace "tab.." a fili yace "Bari muga" ya faɗa yana kama hannunta tare da zaunar da ita saman Kujera shi kuma ya nufi wani waje domin yama manta hanyar kitchen bai ma san dame dame zai haɗa ya bada indomie ba, cikin Sa'a yana shiga yaga kicthen ɗin.... He slowly looked at the kitchen, everything inside was beautiful and the smell was rising, jingina yyi daga door way yana tunanin abinda zai fara, gently ya ƙarasa shiga ciki a hankali kamar mai tsoro ya kunna gas kana ya ɗauki pot ya saka, bai san inda komai yake ba gashi tukunyar na kamawa, hannunsa ya saka akan tukunyar ai da sauri ya ɗauke yana yarfar da hannunsa tare da faɗin "Aucchhh... I burned my hand" Kallon hannun yayi sosai fatar wajan yyi jaa, yana tunanin rabonsa da ƙunewa tun farkon zuwansu New York Sarah ta kunna gas, bai taɓa ƙonewa ba sai a kanta, sauke tukunyar yyi tare da fita, yana fitowa suka haɗa Idanu da Sarah da sauri ta ɗauke kanta tana haɗe fuska, wajanta ya Ƙarasa Look at into her face, kafin gently ya durƙusa gabanta, hannunsa ya ɗura saman laps ɗinta, tayi sauri kwaɓar hannunsa, da Shock yake kallonta kafin ya sauke Ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya yace "Ohh sowie.." sai kuma yyi shiru ganin kallon da yake mata yasa ta sunkuyar da kanta ƙasa, a hankali yyi ƙasa da kansa yana ture sumarsa gefe, ta ƙarƙashin ƙafarta ya zura kansa tare da leƙa fuskarta, suka haɗa Idanu sosai ya hangi wani irin abu mai kama da tuhuma yana yawo cikin idanunta, ɗauke idanunta tayi fuska a haɗe, zame kansa yyi cikin low tone yace "Wait a moment.." yana faɗin hakan ya nufi part ɗin sa, gaba ɗaya baya jin daɗin zuciyarsa game da sauyin Sarah, He preferred her to offer to speak, her voice was filled with happiness and peace, yana shiga bedroom ɗinsa dake ta Ƙamshin Air-con ya ɗauki Wayarsa tare da fitowa, yana tafe yana shafa wayar yana searching, How will he cook indomie, Kallonta yyi ganin ta kwanta idanunta rufe, kitchen ɗin ya shige ya shafe kusan 1hr yana abu guda sai haɗa zufa yake, ya ƙone sama da waje goma gaba ɗaya hannunsa raɗaɗi yake, ga yankewar da yyi wajan yanka onion... Tunda ya fito daga kitchen ɗin hannunsa riƙe da plate yake kallonta, table yaja ya ajjiye plate ɗin kana ya nufi deep frizeer ya ɗauki gorar ruwa mara sanyi, a gefenta ya zaune ganin kamar bacci take yasa ya ɗan ranƙwafa daidai fuskarta hannunsa a saman fuskarta yana shafawa, gently kuma ya ɗura bakinsa akan hancinta yyi kissing, kana ya manna bakinsa akan jajayen laɓɓanta yyi kissing a hankali yana jin ƙamshin mint mai daɗi, slowly With full emotional ya manna mata kwantaccen sajansa mai sanyi wanda ya jiƙa da ruwa, sanyin sajansa yasa Sarah sauke ajjiyar zuciya tana kwaɓe fuska, cikin wani irin yanayi na buƙatar miji zuwa ga matarsa, ya ɗura bakinsa akan kunnanta tare da hura mata iska mai daɗi yana yawo da hannunsa a saman cikinta daya kejin ɗumi sosai na ratsa hannunsa, ga wani kumbura da ƙasan cikin nata yyi, a hankali yana sama da hannunsa zuwa ƙirjinta cikin wata kalar fitananniyar murya yace "Rayuwata...." Sosai kalmar ta daki zuciyar Sarah, taji kalmar “RAYUWATA" A ko wanne ƙofa na Zuciyarta, yana kissing fatar kunnanta yace "Look i made this for you... I made it Sarahh..." Idanunta ta buɗe bata yarda ta kallesa ba domin bacci ta keji sosai, hannunta zai kama ya miƙar da ita zaune da sauri tace "Don't touch me..." jinjina kansa yyi amma sam bai nuna mata baiji daɗi ba, plate ɗin Indomie ya ɗauka tare da spoon ya tsuna fuska tayi tana ɗauke kanta tace "Ban so.." d mmki yake

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads