Showing 36001 words to 39000 words out of 227252 words
Chapter 13 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt
kunya da sauri ta zubda sharar ta juyo domin komawa cikin asibitin taku kadan tayi da yake kanta a kasa yake sam ba ta lura da wanda yake gabanta ba gabadaya ta ji ta ci karo da mutum sosai ta tsoro zuciyarta lokaci guda ba wanda ta kawo mata sai Dr.Karami tunanin ya kawo mata wato yana biye da ita kenan lokaci guda ta sake tsora a ranta tana fatan Allah yasa bai ga halin da take ciki ba a dalilinsa.
Tunaninta ya tsaya lokacin da taji wani wari gami da kamshin tuarare sun haɗe waje daya sun ba da wani kamshi mara dadi don sai da taji zuciyarta ta fara tashi da sauri cikin tsananin haushi da takaici ta dago kanta ta sauke kan mutumin da ya kusan tafiya da numfshinta da sauri ta ja baya tana mai zare ido bakinta na ƙarkarwa sosai take kallonsa gabadaya take jin tsoro da dukan zuciyarta na karu yanayin da ta ga idanuwansa sun kaɗa sunyi jajir har wani launi duke sauyawa nan da nan ta shiga waige waige domin neman hanyar cetar kai sai dai sam hankalin mutane da suke kai kawo baya kan su da sauri ta ja da baya tana ambatar sunan Allah a zuciyarta lokaci guda ta ji wani irin takaici da haushinda ya sake turnuke ta kau da kai tayi domin ta fusakanci rainin hankali tsantsa yake son kawo mata sabo ya rainata ya raina girmanta ya ganta kankanuwa shiyasa ya sami lasisin da zai shigo rayuwarta ya yi abin da yake so saboda ya mai da ita marashin 'yanci in ba wai tanuna masa zahirin ta bane ta nuna masa ita ma mutum ce kuma ta san darajar kanta ba za su zauka lafiya.
"Na rokeka da Allah da Annabi ka fice daga rayuwata amma ka ki ji ko to bari in hadaka da Iyayenka kila a dalilin su ka bar ni".
Ta fadi tana kara tsuke fuska sosai idanuwana kansa amma sam bata ga yanuna wani alamun yin wani abuba sai ma kara wani yaƙe yake yi saman fuskarsa haka kular da ita sosai.
"ban san mai nayi maka ba, ban san mai yasa kake kokarin shigowa rayuwata ba, ban dan abin da ka gani a duniyata ba har kake kokarin shigowa na rokeka ka fita harkar ta bana bara ma da kai ko miskala zarratin".
"Mariya!".
Sautin muryarsa da ta doki kunnuwanta sosai hakan ya kara tsinka mata zuciya amma hakan bai sanya tsoro ya bayyana a fuskarta ba.
"karka sake kiran sunana kuma ina mai rokon ka da karka sake batar sunana mai so ka ajje sunan Mariya a matsayin wanda baka taba sani ba ko a Mafark...".
Gabadaya taji hannunta cikin nasa ya sarƙe waje daya ba ta san lokacin da ta saki fakar dake hannunta ba cikin tashin hankali tana kokarin kware baki ta kurma ihu taji ya saka dayan hannunsa ya rufe mata baki nan ta kara hargitse tana faman zille-zille domin kwatar kai amma ina ta kasa domin ji take kamar wacce aka daure da sarƙa idanuwanta suka kara yo waje sai faman nishi take yi amma ko a jikinsa sai ma faman murmushi da yake yi idanuwansa na kara hargitsewa waje guda a hankali ya zare hannunsa daga bakinta hakan ya ta damar sakin ihu amma ba mai sauti ba ganin irin alamu da yayi mata alamun shiru.
"kin fiye tsiwa Mariya".
Ya fadi yana kara sarke hannayensu waje daya yana murzawa kadan sosai take jik wani iri a jikinta ko wani sashi na hanyar jininta take jin yana tsayawa cak! da aiki sosai sumar wucin gadi ta ziyarceta a hankali ta fara rintse idanuwanta tana jin tashin hankali na samun ma sauki a kowa ni sashi na jikinta zuciyarta na kin abin da yake mata tsanarsa take ji sosai da sosai tana jin haushinsa na samun matsuguni a zuciyarta.
Sosai wani sashin zuciyarra ta shiga biya mata karatu.
'Ke fa mace ce akan mi zaki tsaya wani namiji gardi yana rike miki hannun kin san illar haka kuwa shin ko kin manta kalamansa da yake fadi miki a haduwarku ta farko'.
Sosai zancen zucin ta yayi tasiri a ko ina na sashin jikinta abin zuciyarta take sanar da ita a yanzu shi kawai ke amsa kuwwa a kunnuwant sosai take jin tana da karfin gwuiwar aikatawa in dai ita kadai ce hanyar da zata kwai kanta da mutuncinta.
Tun da Mariya ta kulle idanuwanta ya zuba mata idanu sosai yake kallonta sosai yake kallon fuskarta da laɓɓanta da suka tsuke waje daya sun yi jajir da su hancinta dan madaidaici mai tsayi idamuwanta da suke rufe haƙa suka kara bayyanar da girmansu yake sosai yake jin zuciyarsa na sauya salon wasu lamurka sosai yake jin komai na kwance masa sosai yake kallonta tana burgeshi.
Mariya da ta buɗe idanuwanta a daidai lokacin shi kuma ya shigar da laɓɓansa cikin bakinsa yana lasa ba ta san lokacin da ta daga hannu ta sauke masa zara-zaran yatsunta a kan kuncinsa ba ji kake Tasss!!.
"ji ba yar iskan ba ce ka sani ni 'yar mutunci ce kuma iyayena masu mutunce ne sun san daraja da kimata ba wai sun haifeni bane don kowa ni dan duniya ya zo wajena ya yashe ka sani ni da kake gani nafi karfin ka wallahi bar ganina karama wanda yake baka lasisin zuwa gareni da mugun nufinka to ka sani nayi maka nisa wallahi na wuce da saninka ni ba irin 'ya'yan da ake ribata bane har a bata masu rayuwa don haka ka kiyaye".
Ta karashe cikin yanayi na rashin tsoro ko abin da zai je ya dawo a da sauri ta fizge hannunta tana tsartar masa da yawu ta wuce abin ta.
gabadaya komai nashi yaji ya tsaya na jikinsa sosai ya ji sa wata duniya wacce mai san ta mene ne ba sosai sosai yaji kansa na juyawa sosai yaji komai ya kwance masa gani yake yi kamar bashi ba gani yake yi wannan lamarin da ya faru kamar ba gaske ba gani yake yi ko a mafarkinsa ban yi tunani haka ta kasance ma dan yatsansa ya saka a baki sosai ya ciza shi kamar zai tsinkeshi zafin da yaji ya ziyarce shi ne ya sanyashi sauri buɗe idanunsa ganin lamarin gaske ne bai san lokacin da wasu kwala suka taru masa a idanu ba da sauri yayi kokarin mai da su yana mai dafe kirjinsa ba abin da yake hangowa sai hannun Mariya lokacin da ta daga ta sauke a fuskarsa ba abin da kunnuwansa ke jiyo masa sai yarda sautin marin ke sauka a kan fuskarsa.
Sosai kalaman da ta furta suke dawo masa sosai yake jin wani irin yanayi na zarya cikim gudu suna samun masauki a ransa sosai yake jin wani katon abu mai nauyi na samun masaukin a zuciyarsa da kasan ruhinsasosai yake jin wani irin abu maɗaci da bauri na sarƙe masa harshe sosai kalmar MUTUNCIN tana dashi yake amsa masa kuwwa a ko wacce dakika gyaɗa kai ya shigayi gabadaya ya kasa motsawa lokaci mai tsayi ya dauka a haka har zuwa lokacin mai gama tantacce abin da ya faru dashi gskiya bane.
"Uhm ai ita dama WUYA MAKARANTAR KARE ce wallahi".
Abin da muryar Khairiyya ta fadi kena tana dosa in da yake sosai take masa wani irin kallo na raini da takaicin abin da ya faru sosai take jin ɗaci a ranta musamman yarda taga komai ya faru akan idom ta ba abin da y kara tsikar mata da zuciya sai Yainyar da ta gani wai akanta Huzaifa yake zaucewa ta rasa ma mai ya dace tayi ji take kamar ta tsinke shi da mari amma ina! ba za ta iya ba a hankali ta fara riko hannunsa ta na murzawa sannu a hankali ta fara jansa tamkar rakumi da aƙala har suka isa wajan motar gidan baya ta buɗe ta turashi cikin wani irin yanayi kamar wanda akayi wa dukan shan gishiri.
Sai da ta kare masa kallo sosai da sosai tana kallon yarda ya rintse idanuwansa kirjinsa na harbawa da sauri-sauri kamar zuciya zata fasa ta fito kau da kai tayi jiki a sage ta koma gidan gaba wajan zaman direba ta shiga ta tada motar cikin wani irin yanayi ta fizgi motar har sai da kura ta tashi ta fice daga harabar Asibitin.
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA HUDU.
Hannu bibbuyu ta zabga tagumi idanuwanta kan Mu'azzam. sosai take kallonsa tana jin wani irin abu na sauka kan zuciyarta da ruhinta, sosai take jin wani abu mai kama da ruwa yana kwaranya a ko wani sashi da loko na ma'ajiyar zuciyarta, komai take ji yana yi mata wani iri sosai take jin kauna da so mai girma na saukar mata akan kaninta ba abin da take nisawa a ranta sai yarda duniya lokaci guda take shirin juye mata da wata irin ƙaddara mai girma a rayuwarta. sosai take jin duniyar na wargajewa da dukkan wani farinciki mai girma, da ta san tana samu cikin kankanuwar rayuwarta.
Ya za tayi kenan in ta rasa wadannan madogaran rayuwarta ta mai duniyarta za ta kwaso mata in ta rasa wadannan mutane masu matukar muhimmanci a duniyarta.
Wasu hawaye masu zafi matuka taji suna sauka akan fuskarta da can cikin zuciyarta da ruhinta.
Ta sani kuma ta dade jimawa cikin duniyarta ba ta da sa'a a rayuwarta domin kuwa sosai ta fuskata ƙaddara mai kaifi ce ta fado mata da abubuwa masu matukar tashin hankali da yankewar farinciki Babanta ya tafi ya barta ga Ummanta bata da lafiya ga karamin kaninta wanda shi ƙaddara ta sunkuto shi cikin wannan duniyar mai dauke da kwamatsai rashin dadi ina ma tana da dama ina ma tana da iko ina ma ta san zai fado duniyar nan a haka da bata yarda ba da bata amince ba ina ma ace ana tuntuba kamin a sako dan'uwa duniya da ta roki ubangiji bai sako kaninta ba sai dai ba yarda ta iya komai na Allah tabbatacce ne a duniyar dangin rai kana naka yana nashi.
Hannu ta sanya tana mai dauke zafafan hawaye da take jin su a ko ina na sashin zuciyarta tana dauke su wasu na biyo bayan su tana jima cikin wannan yanayin kafin ta motsa ganin Mu'azzam yayi barci ta kai shi makwancinsa ta kwantar bayan tayi Hugging din sa a ko ina na fuskarsa sosai take jin kauna mai girma a tsakanin ko ina na sassan jikinta akan shi sosai take hango wa a duniyar nan bata da kowa dangin yan uwa sai shi dole ta kula dashi dole ta so shi domin shi kadai ne take zaton zai shafe duk wani daci da kunci da ukuba da take ji a zuciyarta na rashin yan uwantaka.
A hankali ta fara takawa har inda Umma take kwance ta na barci hankali kwance kallo daya zakayi mata ka tabbatar akwai alamun warakar natsuwa a tare da ita. Idanuwanta sosai ta buɗe akanta tana kallonta kamar wacce aka ce in ta dauke idanuwanta za a gudu da ita zuciyarta taji tana wani amsawa da wasu abubuwa mabambanta wanda ita kanta ba za ta ce me nene ba.
Wani murmushi ya subuce mata kalaman Dr.Karami suke mata yawo a kunne a jiya bayan ya zo ya duba Umma.
****
Kallonta yake yi sosai yana yawatawa da idanuwansa masu wani irin yanayi mai matukar kashe jikin wanda ake kallo sosai take jin kallon nasa na shiga duk wani sassa na jikinta yana haifar mata da wasu abubuwa wanda ba ta san a mizanin da za ta ajje su ba sosai take jin bugun zuciyarta sosai take jin yarda zuciyar ta ta take tsalle a duk wata dakika daya na kallon da Dr.Karami yake yi mata ta rasa mai yasa take jin haka ta rasa dalili lokaci da dama ana kallonta mutane masu muhimmanci a idanuwanta amma bata jin haka sai a kansa shi kadai kwallin kwal!.
"Mariya".
Yarda Dr.Karami ya ambaci sunan sai taji aduniyar rayuwarta bata taba jin wanda ya kira sunan da wani irin yanayi mai matukar amsa kuwwa a kwakwalwa da kashe jiki da sanya zuciya tsalle tsalle kamarsa ba sosai take jin duk wani sashi na jikinta na wani irin amsawa da narkewa kamar ana narka roba a wuta wani numfashi take ja mai matukar girma wanda take ji kamar in har batayi jarumtar jan sa ba numfashin katsewa zaiyi daga gareta kanta a kasa tana faman wasa da kasar rigar atamfar ta da take jikinta wanda kallo daya zaka yi mata kasan taji jiki sosai da sosai.
"kin fiye kunya da yawa. Ya kamata zuwa wannan lokaci ki saki jikin ki da ni domin an zama daya".
Wani irin kuwwa taji maganar tasa ta nayi cikin kwakwalwarta ji take kamar kasa ta tsage ta zurma ciki sam bata son yarda Dr.Karami ke mata amma kuma ta na son ta zauna dashi sosai a waje daya domin mutum ne mai saukin kai da kokarin kwantarwa da mutum hankali.
A hankali take daga kai domin ita dai ba ta san mai zata ce dashi ba bama ta san yarda kalaman nasa su ke zuwa ba cikin kwakwalwarta ita dai kawai sautin muryarsa take jin na amsa amo nata.
"kin ga dai yau kuna cikin kwana na Arba'in da takwas kin ga kenan yau saura kwana goma sha biyu su cike KWANA SITTIN da nace in Allah ya yarje mana komai zai daidaita a wajan Umma. Shin ya kike ganin jikin nata me kike karanta game da ita?".
Ya dasa aya yana mai dubanta sosai cikin idanuwansa yana faman murmushi yana gyada kai sosai yake jin Mariya na samun masauki a zuciyarsa da duk kan wani sashi na jikinta sosai yake jin ta tamkar uwa daya uba daya suke sosai yake jin wani abu mai girma yana samun waje a filin zuciyarsa yana zama wanda a kullum yana jin yarda yake daɗuwa ba wai raguwa ba murmushi ya sake yi.
"ban san mai zan ce miki ba, ban san ya kike rayuwarki bs, ban san mai yasa ba ki sakin jiki da mutum ba, ban san mai yasa kike gujewa mai...".
Sosai yaji kalmar da zai fadi tayi nauyi a bakinsa ta danne harshensa da wani gingimeman abu mai girma sosai yake buɗe idanuwansa akanta wani irin bugu yake jin kirjinsa nayi bai san mai zuciyarsa take kokarin yi ba bai san abin da take kokarin dauko masa ba wanda sam bai yi tunanin haka ba.
A hankali take dago kanta tana kokarin ajje idanuwanta akansa cikin yanayi na TUHUMA tana jin yarda zancen da yake yi ya yanke wanda take jin alamun akwai dalili kamar wani abu ne daban ya hana shi furta abin da yake kokarin cewa ko da dai ita akaran kanta ba ta san ina ya dosa ba kallo daya tayi masa ta kau da kanta jin yarda jikinta da zuciyarta sukayi wani irin tsalle.
Girgiza kai ta shiga yi tana tura laɓɓanta cikin bakinta tana tsotsa kamar wacce ta samu alawa ta rasa mai zata ce masa bata san abin da ya dace ta ce dashi ba sosai take hango wasu abubuwa da suke rikirkita mata lissafin kwakwalwarta a idanuwansa sosai take jin abu mai girma game dashi sosai take hango kwarjini da haiba na dandatsa ko ina na cikin idanuwanta in ta dube shi can kasan makoshi ta fara kokarin furta wani abu a hankali laɓɓanta suka shiga motsawa.
"Ban san yarda zan fuskance ka na ce da kai komai ba, ban san da harufan da zan yi amfani wajan cewa da kai komai ba amm...".
Da sauri taja numfashi gami da tafiya da sauran abin da tayi niyyar cewa.
Sosai ya ware idanu yana kallonta yana ganin yarda take datse laɓɓanta kamar wacce take tsoron furta wata kalma mai muni gareshi.
"Fadi mana ko ya kike zo da maganar ki zan fahimta ba zan ajje ta a mizanin da bata dace ba".
Ya fadi yana kara ware idanunsa sosai akanta wani matsayi yake jin ta na kara samu a gareshi sosai yake hango natsuwa da kula da kai tatttare da ita a hankali ya mike kan kafafuwansa yana duban in da Umma ke kwace tana barci Mu'azzam kusa da ita murmushi yayi kafin ya juyo ya dubi Mariya da take tsaye kikam! kamar wacce aka dasa gabadaya ta gama tafiya cikin wani irin yanayi, ba abin da take roko a ranta illa Dr.Karami ya tafi ko ta samu damar jan numfashi mai dauke da iskan Rahama.
"na tafi Mariya tun da yau na lura azumin magana kike yi".
Yana gama fadin haka ya fara taka kafafuwansa kamar da gaske tafiyar yake yi so yake yi ta dago ta kalle shi haka kuwa akayi tana jin tafiyar tasa tayi nisa gabadaya ta dago da idanuwanta aiko sai suka sarke da nashi ba ta san lokacin da ta saki kara ba gami da ja da baya tana runtse idanuwanta sosai ta sanya tafukan hannunta ta kara rufewa wata irin kunya take ji tana yawatawa a dukkan sasssan jikinta ji take kamar kasa ta tsage ta shige.
Sosai ta bashi dariya ganin yarda tayi a hankali ya taka ya fice daga dakin yana faman sakin murmushi wanda shi kansa mamaki yake yi komai na Mariya na burge shi sosai da sosai.
****
"Yaa Allah!".
Abin da ta furta kenan tana sakin murmushi gami da dafe kai bata san abin da ya shiga kanta ba gabadaya take jinta wani iri sosai take jin ta a wani irin yanayi in tana zaune ko suna tare da Dr.Karami rintse idanuwanta tayi gami da jan numfashi wani kamshi ne taji numfashin nata ya jawo mata ya kai mata cikin hanci a dan firgice ta ware idanuwanta tana Ambaton Allah tsoron ta daya Allah yasa ba Dr.Karami bane domin ko tantama bata yi wannan kamshin nasa ne amma bisa mamaki ba kowa da ta gani ajiyar zuciya tayi tana dungurin kanta domin ta tabbata sharrin tunani ne kawai da na zuciya suke mata haka.
*****
Dakiku masu dama ta dauka cikin motarta kafin ta fara kokarin buɗewa ta ziro kafafuwanta zuwa waje nan ma sai da ta ajje dakiku sannan ta fara kokarin ziro da gangar jikin zuwa waje ta mike kan kafafuwanta sosai take yawatawa da idanuwanta izuwa wajen da