Showing 84001 words to 87000 words out of 227252 words
Chapter 29 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt
na lura har yanzu baki san kaifaffan ALKALAMIN ƘADDARA ba a duniyar rayuwar dangin rai".
numfashi taja tana jin yarda zuciyarta ke kara matsewa waje gudu da tashin hankali mai girma.
Sakanni ta kwashe kafun ta sake numfasawa.
"ƘADDARARMU CE haka Mariya ya kamata ki san wannan duniya tamkar makaranta take rayuwar da muke yi jarabawa ce mai matukar muhimmanci bai kamata tun yanzu ki karaya da wannan rayuwar ba bai kamata ace tun yanzu ki nuna kosawarki akan ALKALAMIN ƘADDARAnki ba ki sani duk wani rai da yayi saura a filin duniyar nan yana DA SAURAN KALLO ita fa rayuwar nan dama uku ce farko tsakiya karshe misali farko shine haihuwa ki san wannan tsakiya kuma baki san abin da ALKALAMIN ƘADDARA zai dauko miki ba karshe kuma mutuwa ce wanda take tamkar riga a jikin ko wani bawa kullum tana makale dashi har ranar da zata dauke shi".
Sosai Mariya kukan ta ya ragu tana duban Umma da jin irin kalamin da take sanar da ita cikin murya mai laushi da kokarin kwantar da hankali gareta sosai take jin zuciyarta na sassautawa komai na raguwa HAWAYEN ZUCIYA da take jin suna kona mata ko ina na kirjin ta suna raguwa.
"Mariya ki koyi rayuwar zaman duniya DUNIYA MAKARANTA CE mai girma wacce tafi ko wacce makaranta dake cikinta ba abin da ba a koya a cikinta na dadi da akasinsa sannan a makarantar duniya akwai fannoni masu zafi kuma akwai masu sauki kamar yarda kike ganin salo a makarantun da kike zuwa kamar jarabawa ce in kayi karatu ka jajirce sai ka samu nasara amma in ka saka wasa a lamarin sai ka rasa gane kan komai".
Gyara zama tayi sosai tana duban Umma bayan ta tankwashe kafafuwanta kamar mai shirin cin abinci hannayenta a haɓarta ta zuba mata ido.
Murmushi Umma tayi kafun ta sake motsa laɓɓanta da salo na rarrashi.
"Na shiga cikin yanayi na cuta bayan na warke na rasa miji na kafun nan kuma ga halin da nake ciki tare da Goggo Marka kin ga duk wannan ALKALAMIN ƘADDARA ta tuni ya rubuta su da izinin Rabbil izzati za su faru dani tun kafun na zo duniya".
"UKU BALA'I kenan".
Mariya ta fadi can kasar zuciyarta da wani irin yanayi mai zafin gaske domin ita dai ba abin da za ta kira wannan lamarin sai haka ba ta hango alheri a cikin su ba sam! balle ta ce musu UKU ALHERI.
"Karki dauki wannan a matsayin bala'o'i ki dauke su a matsayin jarabawa da kuma abin da ALKALAMIN ƘADDARA ya rubuta miki TUN FIL'AZAL da sahalewar ubangijin".
Da sauri Mariya ta dubi Umma tana ware ido gani take yi kamar ta jiyo abin da ta ke zantawa da zuciyarta.
"Sannan ki sani ba ko wacce Ƙaddara ba ce take samun bawa hka kawai sai da sanadi ko sila sannan kuma akwai abubuwa da yawa da suke faruwa a filin DUNIYARMU wanda da yarda mu da sanadinmu komai ke faruwa damu sosai muke daukan wasu abubuwa da suke faru damu mu jinginawa ƙaddara bayan da saka hannunmu komai ke faruwa shiyasa ake so komai DAN'ADAM zai yi a filin rayuwar duniyarsa ya dinga dubawa yana daurawa a MIZANIN HANKALI kafun ya aikata shi, saboda gujewa kuskure domin KUSKURE DAYA TAK! yake saka mutum a da na sani".
Sosai jikin Mariya yayi sanyi hawaye kadan-kadan suka shiga zubo mata ji take yi kamar JIRWAYE Umma ke yi mata da zantukanta ba wanda ta tuna a wannan lokacin sai Dr.Karami da fushin da yayi da ita ta tabbata ita ce sila ita ce sanadin faruwar komai amma kuma ai ba ta san sanadi ba ba ta san abin da ya sa yayi fashi da ita ba har haka.
"Kan Uban can ke! Habeeba".
Kamar daga sama sukaji Goggo Marka ta lailayo ashar ta kudunma ta daura da fadin haka sosai gabansu su duka ya fadi.
"Yaa Rabbi?".
Umma ta fadi tana mai sakin wani murmushi mai ciwo a zuciya.
"Ni za ku mai da 'yar iska ko".
Ta sake fadi tana fadowa cikin dakin hannun ta rike da zanin atamfa da ya sha jiki kallo daya zaka yi masa ka gane mugunta da aka yi masa reza ce aka saka aka kekketa shi ketawa wanda baza ta bari a sake morarsa ba.
"Uban waye yayi mani wannan mugun abun?".
Ta fadi tana mai duban Umma kafun ta sake idanu akan Mariya da tayi mata kuri da idanu tana jiran Sharrin da zai biyo baya don ta lura TUTAR MAKIRCI ce ta motsa.
"Da ku fa nake yi ku ka yi mani carko carko da ido kamar kwarto ya fada dakin suruka ya rasa dan kamfansa".
Ajiyar zuciya suka saki su duka zuciyarsu da wani irin yanayi mai sanya ɗaci a kasan zuciya da ruhi.
"in ban da bakar mugun ta da bakin sharri yanzu Mariya saboda an koya miki bakin hali irin na dangin uwarki shine zanin nawo kika kama ki ka kekketa sabo mugun abu".
'Yaa Salam!'.
Umma da Mariya suka fadi a zuciyoyin su
Ba su an karaba sai kawai saukan mari Mariya taji a kuncin ta ji kake kau!.
"Dan uban uwarki Lamiɗo ne ya saka ki yi mani mugun halin nan ko billahillazi sai kin biyani in ba haka ba na dake ki dukan shan gishiri".
Tana gama fadin haka ta jefa mata zanin a fuska ta juya tana watsa wa Umma wani makirin kallo da tukuicin tsaki sannan ta fice daga dakin.
Hawaye suka ciccko a idanun Mariya ta shiga gyaɗa kai ganin irin kallon da Umma take yi mata mai kama da TUHUMA.
"BA NI BA CE".
"Na sani".
Umma ta fadi tana mai sakar mata murmushi kafun ta kau da kai tana dauke Kwallar da suka kawo idanunta farmaki...
*KAMALA MINNA*😘😘😘
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR.
💕 *_Ki Karba. ki Koya, Idan Kalma So Ta Amsu Yarda Ke Tabbatar Da Kauna._* 💕
-Usaini Danko.
A hankali take sauke jakar dake rataye a kafaɗarta cikin yanayi na sanyi jiki idanuwanta na kan kayan da ta gani zube tsakar dakin tana yawatawa idanuwanta akan su cikin yanayi na son sanin daga in da suka fito domin wani irin bugu taji gabanta yayi lokacin da idanuwanta suka sauka kan kayan.
Motsa laɓɓanta tayi da take jin suna cijewa kamar ba sa son ta motsa su.
"Umma wadannan kayan daga ina kuma?".
Ta fadi har zuwa lokacin idanuwanta na kan kayan ta dubi Mu'azzam da ya koma gefe ya tasa choculat gaba yana faman gabza.
"Uhmm!".
Ta sake fadi tana mai duban Umma da tayi tagumi fuskarta da yanayin damuwa dago idanu tayi ta dubi Mariya da gabanta ke ci gaba da bugawa kamar zuciyarta zata faso kirji ta fito.
"Uhmm baki hadu da Yayan naki bane?".
Cikin yanayi na rashin fahimta take duban Umma da son nuna bata sani ba gyaɗa kai tayi a hankali tana mai samun waje tana zama don ji take yi kamar kafafuwanta ba za su iya daukarta ba sosai yanayin ta ya canza lokaci guda ta shiga tura laɓɓanta cikin baki tana cizawa gabanta take ji yana kara tsinkewa gaɓadaya tun da ta tashi yau take jin wani iri a jikinta kasala da rashin son magana duk su ne suka zama abokan hirarta ko da taje makaranta yau haka ta wuni sukuku Baseera ba yarda ba tayi ba akan ta fadi mata abin da ke damunta amma fir! ta nuna ita ba abin da ke damun ta kawai ba ta jindadin garin ne yau.
Lamarin yayi tsamari yanzu don sosai da sosai take jin faduwar gabanta na daɗuwa.
Wani numfashi Umma ta ja tana fesarwa kafun ta dubi Mariya da tayi sakato da baki tana dubanta alamun son karin bayani.
"Ban san mai kike nufi ba Umma. Wani Yayan nawa ne ya zo?".
Murmushi Umma ta saki mai dan zurfi don ta lura Mariya a dan ruɗe take kamar wani abu na damunta.
"Hashim mana".
'Yaa Allah'.
Mariya ta fadi tana mai kai hannayenta duk biyu tana dafe kanta idanuwanta lokaci guda suka dan kaɗa domin yanayin da take ciki ta kosa ta ji inda Umma ta dosa da zancen domin har yanzu a duhu kanta yake ta rasa gane in da lamarin ya dosa.
Duban kayan ta sake yi tana mai yarfe hannunta da ta cire daga baki kamar wacce ta taɓa wuta.
"Ban gane ba Umma waye haka?".
Wani irin kallon Mamaki Umma take bin ta dashi cikin yanayi na rashin zaton maganar Mariya din sosai take dubanta da yanayi na bata so abin da Mariyar tace ba numfashi ta ja kafun ta motsa laɓɓanta a raunane.
"Yaa Allah mai kike nufi Mariya ba dai har kin manta alheri ba ba dai zaki ce dani kin manta dashi a filin duniyar rayuwarki ba haba! mana yaushe har yaushe hakan zai faru ina! fada min shekaru nawa kuka dauka da rabuwarku dama akwai wannan rana Yaa Salma Haba mana Mariya karki saka zuciyata ta buga mana karki canza mana daga yarda na sanki".
Sosai rauni ya bayyana a muryar Umma bakin ta na rawa har ta dire furucin ta tana duban Mariya da wani irin yanayi mai dauke da daci sosai a zuciya fuskarta lokaci guda ta shiga sauyawa tana rinewa da wani irin abu mai girman gaske.
Tsoro ne sosai ya bayyana a idanun Mariya lokaci guda idanuwanta su kayo waje sosai tana duban Umma da su yanayin da ta ganta a ciki da bacin rai yayi matukar daga mata hankali ba kadan ba da sauri ta mike kanta na wani irin dokawa kamar zai rabe biyu gaban Umma ta karasa ta durkusa kwalla suka cika mata idanu lokaci guda laɓɓanta suka shiga ƙarƙarwa kamar wacce ruwan sama yayi wa dan banzan duka.
"Don Allah Umma...".
"Ya isa haka mana Mariya".
Umma ta tare ta a zafafe tana mai daga mata hannu da wan irin yanayi mai bayyanar da bacin rai kafun ta ja numfashi mai zafi ta dubi Mariya wacce a lokacin hawayen su fara digo mata.
"Ban san haka ki ka koma ba, Ban san yaushe ki ka fara canza halayenki ba, Ban san mai yasa kike kokarin daukar hali na manta Alheri ba, sosai nayi mamaki sosai naji wani iri a raina ban yi tsammanin hakan ba ko A MAFARKINA".
Shiru tayi tana maida numfashi kafun ta dora da cewa,
"Nayi tunanin dama akwai abin da kikayi masa a lokacin baya kafun ya tafi na daɗe ina zargi haka banyi zaton samun haka ba a gareki Mariya Yaa Allah".
Rikicewa Mariya tayi lokaci guda kamar wata zautacciya tana duban Umma cikin yanayi na bayyanuwar tsoro a idanuwanta.
"Wallahi ban san wanene ba, ban san akan wa ki ke magana ba don Allah Umma kiyi hakuri ina nan a yarda kika san ni ban sauya halayena ba komai na nan a yarda kika sani na daga halayena na san ALHERI ban mantawa da wanda yayi mani shi".
"Bana tunanin haka, ba yarda za ayi ki ce mani baki manta da shi ba na yarda domin ga shi nan kin nuna na gani don haka...".
"Umma Please mana".
"Kin manta Dr.Karami ko Mariya kin manta mutumin da ya yi...".
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Astagfurullah wa'atubu'ilai".
Abin da tayi saurin ambata kenan tana mikewa tsaye hannunta a goshin ta wani irin hajijiya take ji anayi da ita komai taji yana kwance mata a lokacin runtse idanu tayi komai taji ya na dawo mata a shekara daya da rabi da suka gaba komai take ji kamar yanzu yake wakana fatanta Allah yasa ba fushin nasa bane har yanzu ba ta san ya za tayi ba in bai yafe mata ba bata san wani hali zata shiga ba in bai yi mata afuwa ba.
'Yah Dr.Karami ya zo'.
Ta ambata da wani irin yanayi a zuciyarta wani irin bugu taji zuciyarta tayi a hankali ta sauke hannayenta tana dafe kirjinta da su Umma take duba kafun ta dubi kayan da suke jibge tsakar dakin Mu'azzam da ya gama shan sharafin sa da chocolut duk ya bata jikin sa ya tashi yana takawa a hankali kamar mai tsoron ya fadi saboda rashin kwarin tafiyar tasa.
"Da gaske Umma? Yaa Allah! Yana ina Umma don Allah yana ina fada min".
Yanayin da take magana da rawar jiki wani murmushi mai kauri yana samun mazauni a fuskarta zai tabbatar maka kamar ba a hayyacin ta take ba jin komai tayi a hargitse a daidai wannan lokacin.
Sosai Umma ta dube ta tana shirin gasgata yanayin da Mariya take nunawa na rashin sanin Dr.Karami ya zo da farko ta dauka rashin hankali zata nuna mata kamar ta mance dashi shiyasa gabadaya taji wani iri a ranta matuƙa domin kuwa a duniyar nan bai kamata ace Mariya ta mance Dr.Karami ba ko da kuwa shekara nawa zai yi ya dawo.
"Ya koma".
Ware ido tayi tana duban Umma.
"Yaa Hayyu Yaa Kayyum! me yasa yayi mani haka Umma mai yasa ya tafi ba tare da ya tsaya mun ga juna ba shin ya mace shekara da muka dauka har da rabi ba tare da mun sanya juna a idanu ba bai kamata yayi min haka ba haba! Umma mai yasa ba ki ce yaje makaranta ba ko kuma ya jirani na dawo".
Muryarta tayi rauni kamar mai son fashewa da kuka a hankali ta fara kokarin zubewa kasa domin jin komai take yi yana sauyawa komai take jin ya narkewa na jikin ta kafafuwanta take jin su kamar ba za su iya daukar gangar jikinta ba.
'Ban san laifi na ya kai har haka ba, ban san abin da na aikata yayi tsamari haka ba, ya kamata ace ka tausaya min kayi mani uzuri akan abin da ban san na aikata ba haba mana! haba mana!'.
Zuciyarta ta shiga fadin kalamai kamar mai shirin zaucewa sosai take jin wani irin zafi na tururi suna wanzuwa a zuciyarta da kasan ruhinta.
Ba ta san ya zata fassara yarda take jin wannan lamarin ba bata san ya zata fassara yarda take jin akan yanayin da Dr.karami ke nuna mata ba sosai zuciyarta da dukkan jikinta ke shiga tashin hankali mara yankewa.
Cikin yanayi na rashin fahimta Umma ke dubanta fuska na bayyanar da tausayin da take ji akan 'yarta ta ta sani dole ta ji ba dadi ta jima da lura da yanayin Mariya akan Dr.Karami shakuwa ce mai girman gaske Allah ya halitta a tsakaninsu wacce rabuwarta take da matuƙar hatsari a junansu musamman Mariya da ta zurfafa lamarin ta bashi matsayi mai girman gaske a filin zuciyarta.
"Assalamu alaikum! Wai ana sallama da Mariya".
Kamar daga sama suka jiyo amon muryar yaro daga tsakar gida.
Umma ta dubi Mariya ita ma ita take kallo.
"Waye?".
Umma ta fadi da sanyin murya har lokacin idanuwanta na kan Mariya da tayi fakare tana zazzare ido fata take yi Allah yasa Dr.Karami ne.
"Wani ne a cikin mota".
Zabura Mariya tayi ba tare da wani jinkiri ba ta sa kai za tayi waje.
"Mariya!".
Umma ta fadi da sauti tana mai tsayar da ita Cak! ta tsaya jikin ta sai faman rawa yake yi kamar wacce aka kaɗawa gangi.
"Ban so abin da kikeyi haba mana Mariya sai kace wata karamar yarinya ko wacce bata da kamun kai meye haka yanzu ke da wannnan yanayin zaki fita shin kin san ko waye yake kiran ki kin san yarda zaki taddashi ba kya tsoron kallon da zai miki na rashin kamun kai ban yarda ba don haka dawo".
Ji tayi kamar ta daura hannu aka ta rusa ihu don takaici da haushi hana ta fita da akayi domin zuciyarta sai tsalle take yi tana sanar da ita ta fita shine ya zo nemanta.
Jiki a sanyaye hawaye na kokarin zuba mata ta samu gefe ta zauna tana wasa da hannayenta.
"Ke haka zaki girma ko da rawar kai ana yabon ki sallah alwala zata gagari ki wannan wacce irin wauta ce sai kace ba 'ya mace ba ki ke irin wannan haukar to ba zan lamunta ba kin ji ko tun wuri ki daina hakan tun kafun ya zame miki jiki ai kewar mutum ba hauka bane...ba ma wannan ba yanzu dake ki barin jiki zuwa ganinsa ki na da tabbacin shine".
Kasa takara yi da kai tana girgizawa zuciyarta na kara matsewa a filin kirjinta so take yi kawai ta ganta a wajan nan.
"Maza tashi ki wanke wannan fuskar taki".
Ba musu ta mike tayi waje ji take yi kamar ta zura da gudu amma tana tsoron bacin ran Ummanta don haka tana wanke fuskar ta dawo ta zauna tana ajje numfashi kadan-kadan.
"ki goge fuskarki ki tashi ki tafi".
Umma ta fadi da Umarni a zuciyarta cikin yanayi na daure fuska sosai. Ba musu mafiya tasa ta goge fuskarta har tana muttsuƙa ɗan basilin kafun ta mike bayan ta zare kayan makarantar dake jikinta ta saka doguwar jallabiya da hijab sannan ta sa kai ta fice.
A hankali take taku tana jin gabanta na dokawa duk takun daya sai taji ya karu sosai a haka har ta isa soro nan ta ja burki ta tsaya tana mai da numfashi a hankali ta shiga kokarin daidaita kanta.
Motarsa dake girke gefe guda take sauke idanuwanta akanta sabuwa ce fil! sai daukar idanu take yi kamar yanzu aka gama ƙerata bakin glass din ta mai duhu wanda ya boye sirrin komai na cikin motar sosai taji gaban ya doka lokacin da ta fara takawa cikin sanyi jiki zuwa wajan motar ba abin da take ambata a zuciyar sai sunayen Allah.
"Yaa Rabb!".
Ta furta lokacin da wani kamshi mai karfi ya daki hancinta har sai da ta kusan dauke numfashi gabanta yayi wani irin bugu ta shiga ware idanu cikin yanayi na tsoro a fuskarta hannayenta biyu ta saka ta dafe goshinta da take ji kamar zai fice gefe daya wani irin abu ne taji zuciyarta ta buge ta dashi da bata yi tsammani ba dago idanunta tayi ta na saukewa akan motar a daidai lokacin shi kuma ya buɗe murfin yana zuru kafafuwansa masu dauke da wani haɗaɗɗen takalmi sau ciki mai kalar baki sai daukar idanu yake yi.
Gabanta ya cigaba da dokawa tana kara ware idanu so take yi ta karyata zuciyar da idanuwanta da suke kokarin wanzar mata da abin da ba tayi zato ba ko kadan a daidai wannan lokacin ba ta fada abin dake shirin faruwa a yanzu ya faru ba haka take so ba bashi tayi KUDIRI ta gani ba a daidai wannan lokacin.
"Dr.Aqeel".
Ta fadi da wani irin yanayi mai zurfi a