Showing 87001 words to 90000 words out of 227252 words
Chapter 30 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt
zuciyarta da gangar jikinta numfashi take kokawa dashi da yake kokarin yanke mata tashin hankalin ta take jin ya karu ba kadan ba ba ta shirya ba bata shirya karbar wani tashin hankalin ba bayan wanda take ciki mai yasa zai mata haka mai yasa zai katse mata hanzarin ta mai yasa ya zo a daidai irin wannan lokacin da bai dace sam dashi ba mai yasa?.
A hankali ya gama fitowa yana mikewa kan kafafuwansa idanuwansa na kan Mariya dake tsaye kamar wacce aka dasa kwankwarar motsi ba tayi illa numfashinta da yake fita da sauri-sauri fuskarta a haɗe kamar hadarin dake shirin zubda ruwa a hakan kuma take yaƙe wanda yafi kuka ciwo.
Murmushi a fuskarsa mai girma duk da glass din da ya mannawa idanuwansa hakan bai hana ta hango tsakar idanun nasa ba kau da kai tayi da sauri tana jin yarda zuciyarta ke bugawa cikin wani irin yanayi mai girma in ba ta manta ba rabon ta dashi yau kusan wata shidda kenan tun wani zuwa da yayi da wani lamari mai girma da ta kasa fahimtarsa tun daga lokacin ya dauke kafarsa da zuwa gidan su da sunan ya bata lokaci tayi tunani akan lamarin da ya zo mata dashi Alal-hakika ta mance da wanzuwansa duk da dai tana jin sa a ranta amma abin da ya zo mata dashi tuni ta ajje shi gefe domin ita a tunanin haukar ta ba zai dawo ba tsokanar ta yake yi a sigar wasa amma ganinsa a yanzu ya dawo mata da komai tsoronta daya ya tuhumeta bata san mai zata ce dashi ba bata san ma ya za tayi da maganar ba domin ko a MIZANIN HANKALIn ta da ta daura bata ga komai ba.
"Mariya".
Ya fadi yana kara ƙawata fuskarsa da murmushi sanye yake da Suit light Blue wanda tayi matukar amsar jikinsa sosai hannu rike da hula mai kama da malfa baka haka takalmin kafarsa baki ne sai kyallin sabuntaka yake yi.
Tun daga kafafuwansa ta fara kallonsa har izuwa kirjinsa sosai shigar tasa ta burgeta ba kadan ba sai dai turaren da ya fesa ne yake hawa mata kai sosai ji takeyi kamar zata yi amai.
"Dama kai ne?".
Ta fadi tana mai tura laɓɓanta gabadaya cikin bakinta cikin wani irin yanayi na karfin hali.
Dubanta yayi cikin mamaki da kuma tuhuma yana sauke glass din idonsa sosai yake kallonta yana karantar yanayin da yake ganin ta a ciki sosai ya fuskanta kamar da matsala a tattare da ita lakari da yanayin da yarda ta nuna na rashin hayyaci a tattare da ita kuma ga idanunta da fuskarta a haɗe kamar hadari.
"Ba kiyi tsammani ba ko?".
Ya fadi yana daga mata gira da murmushi a fuskarsa kafun ya sake cewa,
"Akwai wanda kikayi tsammanin gani kenan ba ni ba?".
Ya sake jeho mata tambayar da ta sanya cikinta kaɗawa domin gabadaya a tsora ce take.
"Uhmm!?".
Ya sake fadi yana mai jingina da jikin motarsa bayan ya rufe.
Shiru ya gifta a tsakaninsu ba wanda ya sake cewa komai Dr.Aqeel dubanta yake yana jiran cewarta yana harɗe hannayensa a kirjinsa
Ita kuwa gabadaya ba ma ta san ya take ba komai nata a kwance yake laɓɓanta sai motsawa suke yi alamun ta na son cewa wani abu amma ta gagara idanunwanta har zuwa lokacin a kasa suke.
"Dr.Karami ya zo ko?".
Da sauri ta dago kai tana dubansa jin abin da yace idanunwanta take yawatawa a nasa wani abubuwa ne masu matukar girma take gani suna fitowa suna doso ta daga idanuwansa da sauri ta janye idanunta tana faman kokawa da numfashin ta da ke kokarin kufce mata.
"Uhmm nima yanzu na dawo makaranta Umma ke fada min amma ba mu hadu dashi ba".
Ta karashe tana yarfe hannaye kamar wacce ta taba wuta.
Sosai ya fuskanci ruɗanin da take ciki sosai ya gane in da yanayin da tashi ya dosa wato Dr.Karami tayi tunanin ya kira ta shi yasa ta fito cikin yanayi na hanzari amma ganin sa da tayi ya sanya komai nata kwancewa.
"Shi kika son gani ko Mariya, Dr.Karami kika so ki gani bani ba, na sani domin na gane hakan a tattare dake".
Sosai yaji wani irin abu mai girma ya tokare masa zuciya. Ya fuskanci Mariya hankalinta da natsuwarta suna tare da Dr.Karami tun da yake zuwa bai ta ganin rawar jiki ko wani ɗoki ba a game da ita amma yanzu ya gane in da tafi wayo sai dai kuma ba zai yarda da hakan ba.
"Mariya!".
Ya fadi da wata irin murya mai girma da zurfi da abubuwa masu yawa a ciki.
Ita kanta wani yanayi taji da salon da ya kira sunan nata komai taji ya zama kamar ruwa na jikinta yana narkewa zuciyarta ta yi wani irin zillo da wani abu mai girman gaske wanda ta jima tana a jiyarsa a zuciyarta a tsakaninta da Dr.Aqeel wanda har izuwa wannan lokaci bata san menene ba.
Sosai ya gyara tsayuwarsa don ji yake yi kamar zai tiku da kasa kansa yake ji yana sara masa da wani irin yanayi mai zafi bai san haka zata faru ba da bai bata lokacin sa ba da ya san haka zata kasance da ya mika bukatarsa tun wuri sosai da sosai zuciyarsa ta jima tana gargaɗin sa akan yayi abin da ya dace amma yayi ragwanci shi a tunanin sa ya raina yanayin Mariya bai san ba a nan lamarin yake ba yana cikin filin zuciya domin ita zuciya ba ruwanta da kankanta ko girma in ta nuna so da kulawa a abu to tabbas hakan ne.
Nisawa ya yi kafun ya furzar da wani huci mai zafi.
"Mariya wai shin mai ke damun ki ne ko dai ni din ne ba kya bukatar gani a filin rayuwarki?".
Ya fadi da wani irin yanayi mai zafi da nuna bacin rai hakan ya sanya Mariya saurin dagowa tana dubansa lokaci guda wani haske mai kama da kibiya ya fito daga idanuwansa ya sauka a nata.
'Yaa Rabb!'.
Ta furta jin yarda zuciyarta ke amsawa da wani irin yanayi mai girman gaske.
Girgiza kai ta shiga yi alamun ba haka bane.
"haka ne ma na gashi nan kin nuna min tun da na zo gabadaya na ga sauyawarki komai naki ya canza kamar bakya maraba dani ko na lura bani kika yi tsammanin gani ba nayi miki shigar sauri ".
"Kayi Hakuri Dr.Aqeel".
Ta fadi da rauni a muryarta kamar zata saki kuka laɓɓanta take motsawa alamun ta na so ta sake cewa wani abu amma zuciyarta taki bata dama.
"Ba maganar bada hakuri bane Mariya so nake yi ki buɗe baki sannan ki dube ni muyi magana so nake yi komai ya kasance a wannan lokaci so nake yi duk wani SIRRIN DAKE RAINA ki ji shi a yau so nake yi komai da yake cikin zuciya ki ji shi da kunnuwanki so nake yi ki bani dama na shigo rayuwarki mu kasance a INUWA DAYA".
A razane ta dago kai tana dubansa gabanta na daɗa faduwa ji take yi komai na duniyarta a lokacin yana wurgi da ita ta ko wani fanni ba ta san mai Dr.Aqeel yake kokarin dauko mata ya jeho mata a filin duniyar rayuwarta ba bata san wani irin tashin hankali bane yake kokarin jeho mata.
Tsoron ta ya karu sosai ta shiga gyaɗa kai wasu kwalla ne taji su na taruwa a idanuwanta wanda bata san dalilin su ba sosai zuciyarta take matsewa da zancen Dr.Aqeel wanda ba ta san yarda zata fassara yarda suke kasancewa a zuciyarta ba.
"Mai zai hana ki karba Mariya sannan ki koya kuma tun da nasan baki iya ba baki taba yi ba wannan shi First time dinki a cikin wannan lamarin ya kamata ki bani dama da yarda na tabbatar miki na san zaki karba kuma ki koya a lokacin da kika bani hadin kan ki na bayyana miki SIRRIN DAKE RAINA".
Zuciyarta taji ta yi wani irin harbawa gabadaya ta dago mata kirji sama hannu tasa ta dafe kirjin nata ji take yi kamar ta kurma ihu ko ta samu sa'ida amma ina ba za ta iya yin haka ba bata san mai ALKALAMIN ƘADDARARTA ke kokarin dauko mata ba da ya jona ta da Dr.Aqeel da wannan lamarin mai girman gaske.
"Ban san me kake nufi ba, ban san ina zancen ka ya saka gaba ba don Allah Dr.Aqeel...".
"Haba mana Mariya me yasa zaki fadi haka mai yasa kike kokarin dauko abin da kika san ba zan taba yarda dashi ba na sani kin ji ni sa rai kuma kin fahimta kawai karba ne ba zaki yi ba saboda baki yarda dani ba".
"Yaa Allah! haba mana Dr.Aqeel mai yasa kake fadin haka mai yasa kake kokarin kasa fahimta ta da ganga bayan kuma kasan ba haka lamarin yake ba".
Sosai yaji jikinsa yayi sanyi da maganganun Mariya dubanta yake yi da wani irin yanayi mai girma a zuciyarsa kafun ya nisa.
"Mariya mai zai hana mu fahimci junamu mu bai wa zuciyoyinmu damar fahimtar tsakanin su hakan ne kadai zai sanya lamarin da muke fuskanta ya zo mana da sauki a filin duniyar nan ta mu".
"Ta ya ya kake zaton haka zai kasance bayan kasan ni ba kowan kowa bace a duniyar nan".
"Ba abin da nake so naji daga gareki ba kenan Mariya ki daina kauce hanya yakamata ki tsaya a mataki daya wanda zai kawo mana mafita a tsakaninmu".
Shiru tayi tana tunanin abin da za ta ce dashi zuciyarta ta rabu gida biyu hankalinta ya karkata izuwa wajan Dr.Karami shi take bukatar gani shi take bukatar sanyawa a idanunta a wannan lokaci tafi bukatar dashi da kowa so take yi su gamu da juna ba ta san wani matsayi ya ajje ta ba bata san ko har yanzu ya na fushi da ita ba zuciyarta ta na sanar da ita har yanzu yana nan kan bakarsa tun da har ya iya zuwa bai neme ta ba kuma ya san inda zai same ta amma yayi birisda ita dan hakan tana cikin TSAKA MAI WUYA domin ta lura da Umma ita kanta ta nuna bacin ranta nunawa da tayi bata gane Dr.Karami ba to ina ga kuma ta san halin da suke ciki a tsakaninsu na bacin rai da ta sanya shi.
So take yi ta gujewa tashin hankalin da Dr.Aqeel ke kokarin turata a ciki domin kuwa zuciyarta gabadaya ta hargitse kwanyarta sai tururi take yi.
"Ki bani lokaci mana a lokacin da ke cikin rayuwarki na sani zaki fahimce ni nan gaba kadan".
Gƴaɗa kai take yi cikin rashin abin cewa bata san abin da zata ce dashi ba ta sani Dr.Aqeel yayi mata HALACCI bai kamata ta watsa masa kasa a ido ba bai kamata ta mance ALHERI da yayi mata ba a filin duniyar rayuwarta ba ma ita kadai ba har da iyayenta sai dai zuciyarta ba ta san matsayar da zata ajje shi ba bata san a wani matsayi yake ba a cikinta.
"Shikenan".
Ta fadi da wani irin nauyi mai girma a zuciyarta domin ita dai ba ta san mai zata ce dashi ba bata so ta fadi abin da zai sanya shi bacin rai ko ya tafi da fushin ta a zuciyarsa bata so ayi na biyu kamar Dr.Karami.
Gyaɗa kai kawai yayi yana mai sakin yaƙe sosai ya fuskanta Mariya na bukatar lokaci sosai take matakin koyon komai da yake nuna mata zai yi kokarin don ganar da ita komai yarda ya kamata ba ya so yayi sake a cikin wannan lamarin.
"Sai anjima ki gaida su Umma".
Ya fadi da murya mai sauti wanda tayi matukar tasiri a zuciyar Mariya ta saukar mata da kasala.
Tana kallon shi ya shiga motarsa ya bar layin tana bin sa da kallo har ya bacewa ganin ta kafun ta ja raunannan jikin ta ta koma cikin gida zuciya cike da rikici mai yawan gaske...
*_KAMALA MINNA_*😘😘😘
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA ASHIRIN DA SHIDA.
Ta jima sosai cikin soron gidan nasu tana jan numfashi, yanayin da take jin kanta a ciki a wannan lokacin ba zata iya cewa ga yarda yake ba ta san dai tana cikin wani irin yanayi na rashin natsuwa gami da ciwon rai.
Bata san ya zata yi da Dr.Aqeel ba bata san mai ya kamata tayi masa ba zuciyarta take jin tana shiga wani irin mataki mai raunin gaske yana haifar mata da yanayi na shiga ruɗani sosai take jin wani fili a zuciyarta ya na baiwa Dr.Aqeel matsayi da kalamansa wanda take jin su sun fi komai daga mata hankalin a wannan rana.
Hannunta daya ta saka cikin baki tana cizawa kafun ta fiddo shi tana yarfewa fuskarta na ya mutsewa da wani irin yanayi mai girman gaske a gareta. Ta jima kafun ta fara jan kafafuwanta da take jin su kamar ba nata ba kamar ba jikinta suke ba sosai take jin gajiya a cikin su ji take yi kamar za su watsar da ita kasa a hankali ta kai hannunta ta dafa bango tana tafiya a hankali har ta karasa shigewa cikin gidan.
"Na ce karuwanci kike koyawa 'yarki tana bin gardawa kamar wata karya kin ce ba haka ba yanzu me ne ne wannan Iyee nace yanzu menene wannan ai duk wanda ya ga wadannan kayan ya san da walakin goro a miya ba yarda za ayi a dauki wannan uba uban kayan a baku su haka zikau ba tare da kuma an ci ribar ku ba".
Maganganun da suka shiga dukan kunnuwan Mariya kenan a daidai lokacin da ta iso tsakar gidan ta tsinkayo muryar Goggo Marka cikin dakin su wani tashin hankali ne taji zuciyarta da kwanyarta sun dauka lokaci guda sun tsaya cak! da aikin da sukeyi lokaci guda duk wani magudanan jinin ta suka tsaya komai nata take jin sa ya sauya ji take yi kamar ba a duniyar nan take ba ji take yi kamar ba RAI DA RUHI a gangar jikinta juwa taji ta fara daukarta lokaci guda ta durkushe a wajan cikin wani yanayi tana mai jan numfashi da k'yar yana fizgar kansa shi kuka take so tayi amma zuciyarta da idanuwanta sun ki bata damar haka sai zafi da raɗaɗi da take jin sunayi kamar zasu tayar da kan su daga gareta.
Hannayenta ta saka a saman kirjinta tana shafawa domin ji take kamar ya tarwatse gabadaya idanuwanta a runtse a hankali ta fara kokarin tashi tana jin yarda kirjin nata yayi mata wani irin nauyi da abu mai girman gaske wanda take jin yana rinjayarta.
"Kin ce 'yar ki makaranta take yi ita ga wacce ta fi kowa son ilmi ko yanzu tsakanin ki da Allah Habeeba wannan shine makarantar da take zuwa don na tabbata a hanyar fitar da take yi ne ta hadu da wanda yayi mata wannan hidimar kuma na tabbata ba haka kawai bane sai da ta biyasa kafun ya bayar".
'Yaa zuljalalu wal'Ikram Ya Hayyu Yaa Kayyum'.
Abin da take jin wani sashi na zuciyarta na fadi kenan har ta iso bakin kofar ta tokare hannayenta a saman goshinta ji take yi kanta kamar zai tarwatse idanuwanta a runtse ta shiga ajje numfashi mai girma gaske wani abu taji ya zo mata makoshi ya tsaya tana jin yarda yake kartar mata ko ina na kirjinta har zuwa makoshi.
"Haba mana Goggo Marka ta ya kike tunanin zan jefa 'yar da na haifa a cikina cikin wannan mugun yanayi ribar mai zan samu a ciki".
Muryar Umma ta tsinkayo ta fadin haka muryarta cikin yanayi mai kama da kuka da sauri ta dago kanta ta ware idanunta kafun ta dage labulan dakin tsaye ta hango Goggo Marka sai faman tsaki take ja tana jifan Umma da mugun kallo jin motsi ne ya sanyata juyowa ganin Mariya ya sanya ta sakin wani murmushi na mugun kafun ta shiga tafa hannayenta.
"Uhmm a hakan kamar gaske musa a baki fir'auna a zuci".
Ta fadi tana yatsine fuska kafun ta dan rangwafa inda kayan suke tana bincike kafun ta shiga ware wasu a gefe guda sai da ta ware masu isarta sannan ta sunguma tana duban su Umma.
"To mu ma dai bari mu ci albarkar kacin bariki ko kin san ko ina kayan alheri suke dadi gare su Allah ya karo mana irin su masu kyautatawa".
Ta na gama fadin haka tayi hanyar yo wa waje Mariya da tayi sumar tsaye bangazar da taji anyi mata ya dawo da ita hayyacinta a rikice ta dubi Goggo Marka sannan ta dubi Umma wacce ta zabga tagumi hawaye sai shatata suke yi a fuskarta bakin ciki da takaicin duniya duk sun cike mata zuciya gabadaya ta hargitse sosai fuskarta ta ke nuni da tsananin tashin hankalin da take ciki ganin Mariya na dubanta ya sanyata saurin dauke hawayen da suke zubo mata tana sakin wani yake wanda yafi kuka ciwo.
Wani irin kuka ne Mariya taji yana zo mata a daidai wannan lokacin hannu ta saka ta toshe bakinta tana karasawa cikin dakin durkushewa tayi gaban Umma da wani irin yanayi na tashin hankali mai girman gaske laɓɓanta na rawa ta shiga motsa su.
"Na Shiga Uku wanna wacce irin rayuwa ce take kokarin tunkaromu a daidai wannan lokacin wannan wani irin yanayi ne mai sanya ciwon rai ya sanyo mu gaba".
Hannu Umma ta daga mata alamun tayi shiru kafun ta fara magana cikin yanayi na rauni.
"Ni ban ga abin shiga uku ba don haka ki daina ambatar mana Uku a nan kin ji ko kina dai bata hawayenki ki share su domin in har kika ce zaki cigaba da zubda su to na tabbata zaki shekara dubu a haka in dai kina cikin wannan rayuwar duniyar nan".
Fakare tayi da kunnuwa ta zubawa Umma idanu kamar wacce taga bakuwar fuska kafun ta shiga jan hanci kamar zata fizgeshi daga fuskanta.
"Haka nake nufi domin kuwa in har kace ba zaka dauki abin da ALKALAMIN ƘADDARA ya kawo maka rayuwa ba to kana tare da tashin hankali mai girman gaske".
Hawaye suka sake balle mata domin ji tayi komai ya kwance mata zuciyarta na wani irin zugi da raɗaɗi.
"Amma Umma..".
"Haba mana Mariya".
Tayi sauri katseta kafun ta ja numfashi da take jin sa da wani irin yanayi mai zafi gaske.
"Ina kika baro shi".
Runtse idanu tayi jin zuciya ta bugu kafun ta ciza laɓɓanta tana jin wani abu mai nauyin gaske na