Showing 93001 words to 96000 words out of 227252 words
Chapter 32 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt
hakan ya bashi damar sake kare mata kallo kafun yace.
"Ina son magana dake Mariya ki bani lokaci ko ya ya ne".
"Please don Allah Huzaif ka barni da naji da abin da yake damu na bani da lokacin da zan iya zama naji abin da zaka fadi don Allah ka kyale ni".
Ta karashe tana kokarin buɗe motar ta fice.
"Mariya!".
Cak! ta tsaya ba tare da ta karasa ficewa ba a hankali ta juya ta dubeshi ganin yanayin da yake ba karamin faduwa gaba taji ba da sauri ta fice daga cikin motar har tana kokarin faduwa ko tsayawa dubansa bata yi ba ta doshi gidan su Baseera cikin yanayi na rashin hayyaci sai faman hada hanya take yi kamar wacce ta sha kaya maye...
*_KAMALA MINNA_*😍😍😍
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI.
Mariya ta jima tsaye bakin get domin daidai kanta, sosai ta shiga tashin hankali komai taji yana kwance mata. tsayuwar ta a nan shine kawai take ganin mafita domin in har ta cigaba da tafiya zubewa zatayi warwas a kasa, domin kuwa kafafuwanta take ji suna harɗewa kamar an narka roba.
Numfashi take ja ta na saukewa kafun ta sanya hannu tana kwankwasa Get din a yan sakanni mai gadi ya iso sai da ya leko ta 'yar karamar kofar dake jiki ya ga wacece sannan ya zo ya buɗe karamar kofar yana bin Mariya da kallo fuskarsa da fara'a da alamun ya santa dama.
Gaidashi tayi kafun ta juyo ta dubi in da Huzaif yake abin mamaki tsaye ta hango shi ya harɗe hannayensa idanuwansa na in da take tsaye saurin dauke kai tayi tana mai cusa kanta cikin gidan bayan ta gaida baba maigadi.
Huzaif ganin ta shige cikin gidan hakan ya sanya shi dukan jikin motarsa da wani irin yanayi na tashin hankali mai girman gaske.
Zuciyarsa yake ji tana wani karta masa kamar an saka kaifaffiyar wuka ana yayyagawa idanuwansa sun kad'a sun yi jajir kamar wanda akayi wa surace da barkono hannayensa ya daura saman kansa yana dafewa ji yake yi kamar zai tarwatse komai yaji yana kwance masa duniyar yake ji ta ishe shi ba san mai ya dace yayi ba bai san abin da ya kamata ace yayi a daidai wannan lokacin ba akan Mariya.
Ya sani zuciyarsa ba karamar wauta da ganganci tayi masa ba wanda bai san ya zai yi ba in har Mariya ba ta dubeshi ta anshi abin da ya zo mata dashi ba dole filin duniyar rayuwarsa ya kasance cikin tashin hankali mai girma.
A hankali ya fara taka kafafuwansa kamar wanda kwai ya fashewa a ciki yana jan numfashi da yake jinsa kamar zai gushe masa isa yayi ya bude motar ya shiga sai da ya shafe mintina kansa haɗe da sitiyari domin ji yake yi kamar ba zai iya tukin ba gabadaya a haka ya ja motar yana mai ficewa daga cikin unguwar domin dai ba zai iya tsayawa ba don ya tabbata Mariya ko ta fito ba hawa motar tashi za tayi ba a yanayin da ya ga ta nuna akwai alamun tashin hankali da bacin rai mai girma tare da ita yana zaton laifin sa ne kuma ba na kowa ba da wannan tunanin zucin ya bar unguwar gabadaya.
Da Sallama ta shiga cikin babban falon yanayin ta kawai zaka kalla kasan akwai abin da ke damun ta a zuciyarta.
Sakanni ta shafe kafun a ansata a bata izinin shiga
Tunda ta saka kafarta cikin falon ta lura akwai mutane da yawa a ciki ba kamar daba da take zuwa ta samu Mami kawai ko Baseera amma yau abun ya sauya da alamun anyi bak'i.
Ba ta san ta karasa cikin falon ba sai da taji muryar Mami nayi mata sannu da zuwa da sauri ta gayyato natsuwa ta azawa kanta sosai ta shiga cikin wani yanayi ganin duk mutanan dakin ita suke kallo a hankali ta fara takawa ta isa cikin falon sosai tana mai zubewa ta gaishe da Mami sanna ta gaida mace da namijin da taka gani wanda kallo daya tayi musu ta gane suna da alak'a da Mami domin ga kama nan da suke yi da Baseera musamman ma namijin.
"Mariya ke ce a gidan namu yau?".
Gyada kai tayi tana faman yake don ta san da biyu Mami tayi mata magana na kin son zuwan ta gidan nasu sai dai Baseera taje nasu Mami ta sha turawa Mariya ta zo amma sai taki zuwa amma kuma ba laifin ta bane Umma ce ta nuna rashin yardarta don bata son shige-shigen nan musamman gida irin na su Mami masu farcen susa sai ayi wani tunanin daban ko wani abu ke kawo ta.
"Uhmm Mami dafatan na same ku lafiya?".
"Lafiya lau Mariya ya su Umman da Mu'azzam".
"Duk suna lafiya Umma tace na gaishe ki sosai da sosai".
"Madalla ina ansawa".
Daga nan ba wanda ya sake yin magana Mariya na son tambayar Baseera don bata ganta a falon ba amma duk sai taji ta kasa nauyin mutanan dake zaune take ji.
"Yusra yau dai Allah ya hadaku da 'yar gidan mutuniyar taki ga Mariya nan da ake tayi miki kwakwazo akanta".
Wacce aka kira da Yusra din da sauri ta dago kanta daga kan waya fuskar da fara'a kallo daya za kayi mata ka gane JINI DAYA suke da Baseera matashiya ce wacce ba zata haura shekaru talatin a duniya ba da alamun ma tana da aure akan ta domin akwai jariri wanda bai haura wata shidda ba a gefenta yana barci.
"Masha Allah ashe dai Aku mai magana ba tayi karya ba Mariya Sannu ko ya su Umma?".
Mariya dake sunkuye da kai ta dago tana duban Yusra sosai tana mamakin yarda take yi mata magana cikin sakin jiki da fara'a da alamun dai wannan a jini su yake dukkan su ita ma Mami haka take haka ma Dady da wuya ka ga fushin sa gyada kai Mariya tayi tana ansa ta kafun ta sake gaishe ta fuska ita ma a sake.
"Mutuniyar taki tana sama dakinta tun dazu ta shiga ban san abin da take kintsawa ba".
Murmushi Mariya tayi kafun ta mike ta bi hanyar da za ta sada ta da dakin Baseera.
"Ba ki ji ba Mariya".
Mami ta fadi hakan ya sanya Mariya saurin tsayawa ta juyo ta na duban Mami.
"wadannan duk yayin Baseera ne wannan shine Babban su Babban d'ana kenan su nan sa Tareeq ita kuma wannan Yusra tana aure a Abuja shi kuma Tareeq yana karatu ne a kasar waje".
Gyada kai take yi tana faman sakin murmushi tunda Umma ta fara yi mata bayani mai da kanta tayi kan su tana kara dubansu.
Da sauri ta isa wajan Yusra kamar wacce aka tura ta isa wajan jaririyar dake kwance ta shafa mata kai kafun su hada ido da Yusra ta sakar mata murmushi.
"Dauke ta mana".
Kamar abin da take jira kenan ta sanya hannu ta dauka tana faman sakin yake ita ana ta ganin murnushi take yi kamar wanda aka matsawar baki.
"Yah Yusra yariyarki mai kyau kamar Mu'azzam din mu ya sunanta?".
Dariya Mami tayi kafun ta dubi Yusra da ta kafe Mariya da ido ganin yarda take barin jiki akan 'yar ta duk sai taji Mariya ta kwanta mata a zuciya sosai da sosai.
"Mariya wai dama kina magana haka".
Mami ta fadi cikin mamaki.
Da sauri tayi kasa da kai alamun jin kunya tana kokarin juyawa ta haye sama.
"Sunanta Nawwara".
Yusra ta fadi da tausassan murmushi a fuskarta.
A hankali Mariya ta juyo ta dube su kafun ta sauke ganin ta kan Tareeq wanda ko kallon ta bai yi ba tun da tashigo har ga Allah taji zafin yanayin da ya nuna mata bata son mutum irin haka mai shariya duk hakan ta dauke shi a matsayin wulakanci ne a filin rayuwarta.
Dago kai tayi da zumar barin wajan caraf! suka hada ido da Mami rausayar da kai tayi da alamun ita ma Mami ta lura da halin-ko-in-kula da Tareeq ya nuna don haka tayi mata alamu da ido tayi hakuri kar ta damu.
A hankali taja jiki ta bar falon tana jin Yusra na yabata a kan yanayin da ta nuna mata akan Nawwara da ita kanta.
A baje ta same ta tsakar gadonta duk ta warwatsa littattafai kamar wacce aka yi wa dole sai ta karance su a lokacin. Mariya bata san lokacin da ta saki dariya ba tana isa cikin dakin sosai.
Dariyar ce ta fargar da Baseera da sauri ta daga kai ganin Mariya ya sanya ta sakin wata kara tana dirow daga kan gadon gabadaya tayo kanta ganin haka ya sanya Mariya matsawa gefe don ta san karamin aikin ta ne tace zata rungume ta kuma ga jaririya a hannunta.
"Uhm Uhm yau anyi kyan kai kenan, Mariya yau kece a gidanmu?".
Ta fadi tana galla mata harara kamar idanunta za su fado kasa.
"Uhmm ni fa matsala ta dake wani lokacin hankali yawa yake yi miki yasin baki ganni da Yarinya bane zaki fado kai na".
Yatsine fuska tayi kafun ta dubi Nawwara.
"Hala Adda Yusra ce ta hadaki da wannan 'yar ta ta mai shegen kuka kamar gyare?".
Ware ido Mariya tayi.
"Nawwara din ce mai kuka".
"Yo eh mana ba ta gajiya da kuka yanzu ma don tana barci ne amma yasin ta tashi ko Hmm sai kin mai da ita wajan uwarta nima abin da ya koro ni daga falon kenan kukanta tun dazu take abu guda kamar cin kwan makauniya".
"ikon Allah gani da gajiyawa yo ke duk abin da kike yi ba a gaji dake ba sai kece zaki ce kin gaji irin wannan son kai haka har ina".
Dariya Baseera tayi tana mai jawo ta ta zaunar da ita bakin gadon kafun ta juya ta isa wajan da dan madaidaicin firij dake can gefe lemo ta dauko mata da gorar ruwa gami da Cake ta kawo mata da kanta tayi saving din ta amma sai bari Mariya tace ta bari zata dauko ta gode a hakan ma.
Sun jima cikin wannan yanayin Baseera sai fama ratata zance take yi kamar wata rediyo cikin maganganun nata ne wata magana ta so narkar da Mariya daga in da take zaune.
"wai shin da zaki shigo baki ga wata hadaddiyar mota ta fice daga layin nan ba?".
Baseera ta fadi tana mai daukar Nawwara daga jikin Mariya, kaɗa idanu tayi kamar mai tunani kafun ta gyada kai alamun eh ta gani domin ta lura da mota da Baseera ke magana akanta.
"Dr.Karami ne ya zo muka gaisa...".
Daga wannan batun Mariya ba ta sake sanin in da kanta yake ba gabadaya taji ana juyata kamar waina a tadda tashin hankalin da take ciki taji ya karu sosai sai yanzu ta gane faduwar gaban da tayi dazu da taga motar ashe Dr.Karami ne.
Sosai kan ta ya kulle komai taji na tunanin ta ya tsaya cak! Ba abin da ke dawainiya da ita sai mamaki da al'ajabi ta yarda Dr.Karami gabadaya ya sauya yake gujewa haduwarsu ba ta san ya ya za tayi ba ita kam! Ba ta san mai yake nufi da ita ba.
"Yace ma jiya a gidanku ya wuni tun muna makaranta yaje ashe".
Gyaɗa kai kawai Mariya take yi tana faman jan numfashi kirjinta take ji yayi mata wani irin nauyi mai girman gaske numfashin ma da k'yar take iya jan sa.
Jin shirun yayi yawa ya sanya Baseera dubanta sosai da sauri ta ware ido ganin yanayin Mariya dafa ta tayi cikin yanayi na sanyin jiki.
"Me ke faruwa ne wai lafiya kike kuwa Mariya naga gabadaya lokaci guda kin sauya ne me ke damun ki".
Wani numfashi mai zafi ta ja ta fesar kafun ta dubi Baseera da idanunta masu kwalla cikin rauni ta fara magana tana cizon laɓɓanta.
"Kin san kuwa har yau ba mu hadu dashi ba".
Ta karashe kamar zata rushe da kuka jin zuciyar ta take tana zafi da raɗaɗi kanta na wani irin sarawa kamar zai rabe gida biyu.
Ware idanu Baseera tayi gami da dafe kirji.
"Na Shiga Aljanna".
Wani murmushi Mariya ta saki wanda ya fi kuka ciwo kafun ta ja numfashi wanda ya haifar mata da wani irin ciwo a zuciya dama duk gangar jikinta.
"Ni kuma na shiga Uku Bala'i Baseera".
Zabura Baseera tayi ta mike gabadaya kan kafafuwan ta jikinta lokaci guda ya shiga rawa kamar wacce aka jonawa wayar wuta Nawwar dake hannunta har kokarin faduwa take yi duban Mariya take yi cikin wani irin yanayi na ban san in da kika dosa ba dubanta take yi da wani irin yanayi mai dauke da rauni da tausayi dubanta da take yi da wani irin tashin hankali mai girma da ya ziyarci zuciyarta dama dukkannin jikinta.
A hankali ta shiga jan numfashi tana mai kokarin kwantar da Nawwara don ta tabbata in ta cigaba da riketa zata iya watsar da ita ba tare da ta sani ba ba abin da ya kara daga mata hankali sai hawayen da ta gani a idanun Mariya suna zuba.
"Yaa Rabbi!".
Ta fadi tana zubewa bakin gado kamar wata kayan wanki tagumi ta zabga tana ganin ikon Allah wai uwar miji da cin kazar amarci.
"Mariya wai shin me ke damun ki ne haka wallahi kin ta yar min da hankali ba kadan ba".
Nisawa tayi zuciyarta na wani irin harbawa kafun ta ciji laɓɓanta.
"Ban san mai Alkalamin ƙaddarata yake kokarin rubuta mani ba, ban san wani irin tashin hankali ne yake kokarin shigowa rayuwata ba a daidai wannan lokaci Baseera ina cikin matsala, matsala babban wacce ban san maganin taba zuciyata zafi take yi ruhina raɗaɗi yake yi kwanyata ta cushe da tashin hankali mai girma ji nake yi kamar bani ba a filin duniyar nan ji nake yi kamar komai ya sauya a jikina...".
"Ya isa haka".
Baseera ta fadi jin muryar Mariya ta fara rawa tana kokarin sakin kuka.
Ruwa ta tsiyaya cikin glass cup din dake ajje kan farantin da ta kawo mata lemo akai a hankali ta dauka ta mika mata ba musu ta ansa ta kwankwade kamar dama can kishin ruwan take ji wani numfashi taja wanda ya sanya Baseera dubanta da sauri tana mai ware idanunwanta akanta domin gabadaya ta tsorata da yanayin da ta ga Mariyar a ciki.
Sun shafe mintina a haka ba wanda ya sake magana a tsakaninsu sai ajiyar zuciyar Mariya kawai sautin ki tashi ita kuwa Baseera kafeta tayi da ido gami da zabga tagumi domin ta rasa ma mai ya dace domin sosai da sosai kanta ya dau caji ba kadan ba.
"wai shin har yanzu fushin da Dr.Karami yake yi dake ne duk ya sanya ki cikin wannan halin ko me ne ne?".
Baseera ta fadi da wani irin yanayi mai girman gaske a zuciyarta muryarta tayi laushi sosai.
Girgiza kai Mariya ta shiga yi cikin rashin fahimta Baseera tace.
"To me ke damun ki wai shin?".
Sai da taja numfashi mai ciwo kafun ta dubi Baseera.
"Sun sako ni gaba Baseera ban san ya zan yi ba ina cikin tashin hankali".
"Yaa Allah! sun sako ki a gaba fa kika ce su waye haka me kuma suke nema dake?".
"kina dai kallon yarda nake cikin tashin hankali akan Dr.Karami to ban gaba dawowa hayyacina ba shi kuma Dr.Aqeel ya sako ni gaba da wani lamari wanda ban san ya zan fassara miki shi ba bayan haka ga kuma Huzaif shima ya dauko mani wani tashin hankalin yana kokarin jonawa min a filin rayuwata".
"Uhmm ni fa ban gane ba ban san ina kika dosa ba?".
Girgiza kai tayi tana jin yarda zuciyarta ke wani irin harbawa da wani tashin hankali mai girman gaske.
"Dr.Karami fushi yake yi dani wanda ban san dalilin fushin ba".
"wai shin Mariya na tambaye ki mana ke tsakanin ki da Allah zaki ce baki san laifin da kikayi masa ba har yake gudun haduwarku anya kuwa Mariya ya kamata ace kin yi tunani ya kamata ace kin zauna kin yi nazari kin binciko abin da ya haifar da wannan lamarin a tsakaninku".
Shiru Mariya tayi kamar mai tunano wani abu na daban kafun ta nisa ta dubi Baseera.
"kisan Allah tun ranar da muka fara haduwa dake har period dina ya zo to tun ranar rabona da samun fuska daga Dr.Karami tun ranar muka rabu wanda har yau ban sake sakashi a idona ba".
Zaro idanu Baseera tayi tana dafe kirji.
"ke Mariya da gaske kike don Allah?".
Murmushi Mariya tayi mai ciwo kafun ta gyada kai alamun eh.
"Mun shiga Uku anya kuwa Mariya ba wani abu a kasa tsakaninki dashi kuwa?".
"Ke ma dai Baseera ta ya ya zan yi wa Dr.Karami wani abu don na bata masa rai ai Alheri bai ce haka ba amma dai ban sani ba ko a cikin RASHIN SANI wanda ake cewa YAFI DARE DUHU nayi masa amma kuma ai ya kamata ace ya nuna min eh ga abin da nayi masa sai in bashi hakuri ba wai ya zauna yana fushi dani ba kuma bai son ganina kin ga kenan abin da nayi masa ba sauki gareshi ba...".
"ki daina cewa baya son ganinki Dr.karami yafi kowa a filin duniyar nan son ganinki domin kuwa ni zan yi shaidar haka".
Cikin rashin fahimta Mariya take dubanta kafun lokaci guda taji wani lamari ya tunkaro zuciyarta har ya kai cikin kwanyarta da sauri ta mike ta shiga zarya cikin dakin kafun ta tsaya cak! tana tura dan yatsar ta cikin baki tana yawata idanuwanta a sassa na cikin dakin kamar mai son tuno wani abu na daban.
"Ya akayi Mariya ko kin tuno wani abu ne na daban".
Gyaɗa kai tayi kafun ta dubi Baseera.
"Ina zargin wani abu guda domin daga shine koma ya canza tsakanina da Dr.Karami".
Da sauri Baseera ta mike jin abin da Mariya take fadi.
"zo ki bani labari zo ki sanar dani komai na san za a samu hanyar mafita".
Hannunta ta janyo ta zaunar da ita bakin gado tana mai dubanta.
"Bani labari Mariya sanar dani komai".
Sai da taja numfashi sosai tana jin yarda zuciyarta ke kara matsewa waje daya da wani irin yanayi na damuwa matsananciya.
"bana zargin komai sai su Dr.Aqeel da Huzaif domin ranar da muka baro gidanku mun tadda Huzaifa a kofar gidanmu yanayin da naga Dr.Karami ya nuna kamar bai so ba kuma daga lokacin ko kallona bai sake yi ba bayan haka na fito daga motarsa ina kokarin shiga gida sai ga Dr.Aqeel shima ya zo to a wannan lokacin zan