Header Ads
Showing 147001 words to 150000 words out of 227252 words

Chapter 50 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

1428

Ads at the middle of Article

filin duniyar nan ba amma a yau ta tsani Baseera Babbar ƙawarta da take ji da ita a filin duniyar nan wanda bazata ce ga dalili ba.
"Of Couse in ba zaki iya fadi ba ni ina damar da zan iya fadi".
Juyawa tayi ta dubi Dr.Karami da ya gama shiga wani hali na ruɗani musamman yanayin da ya ga Baseera tayi masa ba karamin tayar masa da hankali yayi ba ya jefa zuciyarsa cikin tsanani ruɗani mai matukar firgita kwanya.
"Ta kasa fada maka abin dake damun zuciyarta, ta kasa fuskarta ka ta sanar da kai komai ko da yake kai ma da naka kunshin na sirrin zuciya a tsakaninku ban san waye ya dace na dora a mizanin masu cutar kai ba".
Baseera ta fadi fuskarta ba wasa tana kai komo a tsakaninsu sosai dukkannin su suka shiga ruɗani in maganarta wanda suka rasa in da ta dosa sosai zuciyoyinsu suka shiga harɓawa da lamari mai girma akan maganar sosai suka shilla duniyar nazari ko za su kwato kansu daga duhun da suka faɗa akan zancen nata amma sun kasa sai watsa mata idanu suke yi suna faman jan numfashi kwakwalansu na kara cakuɗewa da lamari mara sauki a zuciya da ruhi.
Taku tayi a hankali ta isa wajan Dr.Karami da ya saki baki da idanu yana kallon ikon mai duka shi dai aka ran kansa bai san ina ta dosa da maganarsa ba amma zuciyarsa nayi masa zargi akwai wani sirri da ta sani a tsakaninsu.
"Zuciyarka zata cuce ka in har baka yi wasa ba".
Ta fadi tana dubansa tsakar idanu kafun ta murmusa da wani irin yanayi.
"Kana sona Dr.Karami amma ka kasa sanar dani har ni akaran kaina na fahimta ya kamata ace baka yi wannan saken ba domin kuwa bana tsammanin zan soka domin ina da wanda nake so".
Runtse idanu yayi lokaci guda yaji wasu kibiyoyin tashin hankali sun cakar masa zuciya kafun lokaci guda yaji duk wani sashi na jinin jikinsa yana tsayawa cak! da gudana komai na jikinsa yaji yana narkewa da tashin hankali buɗe idanuwansa yayi lokaci guda ya sauke su wajan da Baseera take tsaye wacce a wannan lokacin ta rigaya ta juya ta doshi inda Mariya take tsaye tana kokarin mutuwa zuciyarta na ta faman kai kawo wasu kaifaffun wuƙaƙe taji suna soke mata kirji da zuciya da ruhinta take ji su na babbakewa lokaci guda.
Tsoro ne ya saukar masa lokaci guda ganin yarda Baseera ta doshi Mariya ya tabbatarwa kansa maganar da ta sanar dashi ita zata sanar mata tsoronsa daya taki fahimtarsa tsoronsa daya tayi masa fahimta ta baibai tare da yanke masa hukuncin akan wannan lamari ya tabbata komai kara kwaɓewa zai yi da hanzari ya fara kokarin takawa domin isa wajan domin sanin abin yi amma ina kafin yayi taku biyu ta isa wajanta har ta fara magana da ita mutuwar tsaye yayi lokaci guda zuciyarsa ta buga da wani tashin hankali gumi ya fara karyo masa mai dumin gaske komawa yayi da baya ya jingina da motarsa a daidai lokacin ya hango mota kirar Benz tayi Parking kuri yayi wa motar yana kallonta haka kawai yaji motar bata kwanta masa ba a zuciya har da mai ita karan kansa kafin ya gama guntun tunaninsa ya ga Dr.Aqeel ya bayyana ware idanu yayi sosai yana dubansa da mamaki wani kunci ne yaji ya zo masa wuya lokaci guda ya tsaya kafun zuciyarsa ta shiga bugawa da sauri-sauri kamar zata yo waje.
"Kin ka sa fahimta,na fada ki kina cikin yanayi na so amma kin ki yarda sai faman wahalar da zuciyar ki kikeyi na tabbata ba zaki taba samun WALWALAR ZUCIYA ba har sai ranar da kika gasgata na sani Dr.Aqeel kike so amma kin kasa sanar dashi hakan".
Wani irin duba Mariya tayi ma jikinta har rawa yake yi yana karkarwa bakinta ya shiga motsi ji take yi kamar ta shako wuyar Baseera ta turmushe ko ta samu sa'ida da wadannan banzayen lafuza da take fada mata bata san ya kayi ta san Dr.Aqeel take so ba bata san wa ya fada mata shi take so ba bata ya akayi har bakin Baseera ya iya tafka wannan saɓon mai girman gaske ba.
Numfashi ta ja mai tauri kafun ta dube ta sosai da idanuwanta rinannu.
"ya kamata kiyi saurin tuba ga Ubangiji tun kafin ya hukuntaki akan wannan saɓon da kikayi".
Ta fadi tana faman nishi numfashinta take ji yana fizga kamar zai rabu da gangar jikinta gabadaya duban Dr.Karami tayi lokaci guda taji zuciyarta ta sake bugawa kafun ta dubi Baseera da take faman kallonta fuskarta da murmushi.
"Karki sake zuciyata tayi gangancin fara ci miki mutunci karki ga laifina tun wuri ya kamata ki sauya maganar domin ba haka take ba".
Dafa kafaɗarta tayi tana faman sauke numfashi ita jarumtar ta fara rauni bata san ya zata sauke lamarin nan da ta dauko ba mai girman gaske kwakwalwarta ta fara kamawa da wuta batayi zaton abin ba zai zo mata da sauki har haka ba ta dauka lokaci guda komai zai sauya za su karbi muradan zuciyoyinsu ashe fatanta ba zai tabbata ba burinta zai nakasa a wannan matakin tun kafin aje ko ina kau da kai tayi wasu kwalla suka taru mata kafin ta mai da su daƙyar tana faman jan numfashi duban Mariya tayi sosai har yanzu tana kan bakarta taki yarda da burin zuciyarta.
Da dan hanzari Baseera ta juya ta koma inda Dr.Karami yake tsaye gabadaya abin duniya ya ishe shi tsoro yake yi yaji inda zance zai kwana shi da Mariya.
"BAR RAINA ALLURA...".
"...Domin kuwa karfe ce".
Kamar daga sama Baseera taji muryar ta sauke zancen da ta dauko da sauri ta juya Dr.Aqeel ne yake takowa a hankali fuskarsa da yanayi na ba yabo ba fallasa hannunsa da Key din motarsa ya faman kaɗawa sosai ya tunkaro su kallan kallo suka shiga yi shi da Dr.Karami kallo ne na wani irin hali mai kama da 'a cike nake da kai, kana son kawo mani tsaiko a lamari na.'
Harɗe hannayensa yayi a ƙirji lokacin da ya iso yana mai dubansu daya bayan daya kafin ya dire akan Mariya da tayi wujiga-wujiga da ita kamar wacce ta kwato kanta daƙyar daga bakin kura.
"Bana tunanin wannan tsayuwar da kukayi akwai mafita a cikin ta maganar gaskiya ya kamata ku sani ni Mariya take so domin duk abin da kuke zantawa da yarda ke Baseera kike yi na san so kike yi ki hada tsakaninsu amma kin kasa to ki sani Mariya bata da wani wanda yake son ta take sansa tamkar yani...".
"You don get Sense At All Dr.Aqeel ya kamata ka iya bakin ka tun kafin ya kai ka ga dana sani".
Cewar Dr.Karami yana faman hirji jin abin da Dr.Aqeel yake fadi gaba gaɗi cikin gadara da isa.
Murmushi ya saki yana mai watsa hannu sama kafun ya dubi Baseera.
"Bana zaton Mariya zata so Dr.Karami domin kuwa bai nuna son ba ni na fara nuna mata so don haka ni zata ansar wa so".
"Ba dole bane ka fara furta kalmar so ka yi tunanin kuma za a anshi naka son akan wanda ya so daga baya so ba ruwansa sai wanda ya burge zuciya ta aminta dashi zata so dadewa a so ba shi yake sanya a so mutun ba so a RANA DAYA yana iya samun gurbi sannan so yana iya wanzuwa zaman shekaru amma bai samun gurbi don haka ka sani GURBIN SO ba a ko wani waje ake samun sa ba sai inda ya dace".
Gabadayan su suka juya in da suke sauraron zantukan na fitowa Huzaif ne tsaye harɗe da hannu yana faman dariya mara sauti har da 'yar kwallarsa a idanu a hankali ya shiga takowa yana mai cigaba da cewa.
"Bana tunani don ka zo ka furta so kayi tunanin zaka samun GURBIN SO a zuciyar da ka furtawa so lokaci guda so daban yake sannan so sai inda ya ga ya dace zai shiga duk da dai shi kan shi so din ba ya lura da dacewa ko matsayi ko wata daukaka kafin ya farwa zuciya kana ganganci da kace so sai ya tsufa a in da ake furta shi yake samun gurbin zama ya kamata ka sauya tunaninka".
Ya fadi ya mai duban su kafun ya dubi Mariya da tayi firgai-firgai da ita kamar wacce take jira ace kes ta kurma da gudu bata san lokacin da hawaye suka fara zuba a idanuwanta ba dumin su kawai taji tunda Huzaif ya tunkaro ta take jin gabanta na tsananta faduwa da tashin hankali mai girma so take yi ta saki ihu ko zuciyarta ta daina tsalle tsalle da babbakewa da take yi zuciyarta ta take ji tana kumbura cikin kirjinta komai na jikin ta take jin yana daukar zafi kamar roba cikin wuta ji take yi tana narkewa da tashin hankali mai girma gaske bata san wani bala'i bane kuma yake kokarin samun gurbi a yanzu bata san wani irin tashin hankali bane zai sanyota gaba a wannan bigire ta shiga uku ita a duniyarta.
Saukar hannu taji a fuskarta ana dauke mata hawaye wani numfashi taja mai karfi kafin ta runtse idanuwanta ta buɗe su Huzaif ne yake dauke su da hankicif dake hannunsa dubansa take yi da idanuwanta masu kokarin rufewa da kwalla dubansa take yi gabanta na kara tsananta buguwa komai take ji ya kwance mata bata san ya za tayi ba zuciyarta take so ta buga ko zata mutu ta huta da wannan bala'in da take ciki kau da kai tayi lokaci guda ganin irin kallon da Huzaif yake jifanta dashi mai kokarin rikitata ta tsane shi tsana sosai amma bata san abin da yasa lokaci guda zuciyarta ta tuna mata da babinsa ba ta tuna mata da GURBIN da ta bashi a zuciyarta har yake kokarin buɗewa.
"Yaa Rabbi".
Ta furta can kasan makoshinta kafin ta dago kanta ta sake dubansa Dr.Aqeel ta hango ya tunkaro wajan kamar wani mayunwacin zaki sai faman hirji yake yi yana kara hura iska a hancinsa idanuwansa sun kaɗa sunyi yayi kamar anyi masa surace da Barkono hankali ta fara kokarin ja da baya amma ina kafafuwanta take ji kamar an turkesu a waje guda ko motsi basa yi.
"Wai kai ba wani iri mutum ne? shin baka san in da so ya dace bane da yarda bai dace ba na lura kai ma dan takife ne a harkar so ka daina tunanin za kayi wani tsawon rai a harkar so tun wuri ka tattare tashin balagar kyankyasan ka da kake ji dashi sannan kake ganin karan ka ya kai tsaiko har kake tunanin TASIRIN SO zai zauna akan ka ni ne nan wanda so zai yi wa rana ba kai ba".
"Me yasa kafi ye kaunar kan ka ne mai yasa kake son cutar da zuciyarka ne mai yasa kake son ajje GURBIN SO a zuciyarka bayan ka san wauta kake yi wa kan ka bana tunanin ka san meye so kafun ka shige shi a filin duniyarka...".
Duban junan su suke yi kamar wasu mayunwatan zakuna sai faman kallon kallo sukeyi wa juna mai cike da tsananin rigima da tsanar juna.
Bige hannun da Dr.Aqeel yayiwa Huzaif ne ya sanya shi tsagaitawa da maganar da yake yi yana mai murmushi a hankali kuma ya shiga duban Mariya kamar zai shige jikinta idanuwansa sarke da nata.
"Kice baki Kaunata ki fadi su ji ba kya sona".
Runtse idanu tayi tana jin zuciyarta na kara buɗe wasu kofofi har kashi uku wanda ta jima da kullesu gabadaya take jin su suna buɗe kan su da kan su dubansa tayi kafun ta daura hannu aka tana kokarin kurma ihu amma ina ihun ma yaki zuwa hawaye kawai suke mata ambaliya a daidai lokacin Baseera ta iso tana faman duban Mariya fuska a raunane.
"Da matsala Mariya ban san ya zan sanar dake ba amma maganar gaskiya Dr.Karami ba so na yake yi ba ke yake so nayi wannan shirin ne akan cewa ko za ki nuna kishi ki fito ki sanar masa shi kike so kika kasa fadi masa...".
Ji kake kau! hannun Mariya akan kuncinta ta shiga nuna ta da hannu tana faman tangaɗi kamar wanda ta sha barasa tayi makas gabadaya ta fice daga cikin hayyacinta.
"Kina tunanin zan so shi ne bayan kin ce mani kuna soyayya kina tunannin maganar da kika fadi mani zatayi tasiri akai na ne ki bar ni kawai naji da bala'in da kuka jefa ni a ciki na san dama duk ba kwa kaunata dama na sani rakiya nayi duniyar nan na zo ne don kawai a tarwatsa min zuciya na mutu kowa ya huta burin ku ya cika Shikenan..Shikenan zan mutu yanzu zan mutu yanzun nan...".
Kawai fadin maganganun take yi tana dariya idanuwanta na zubda hawaye da sauri Baseera ta isa gareta ta riketa sosai tana faman hade jikinta da nata wani kuka mai zafin gaske ta saki zuciyarta na faman a zalzala da zafin mai girman gaske.
"karki yi saurin yanke tsammani Mariya so ya gaji haka...".
Da sauri ta kwace kanta tana faman ja da baya tana sakin huci.
"So ya gaji haka fa kika ce? dama haka so yake da bala'i a cikin sa, dama haka so yake da kayan guba a cikin sa, dama haka so yake da masifa a cikin sa?. tabbas na yarda SO DA RAININ HANKALI yake, na tabbata so akai na ya fara haifar da masifa, na tabbata akaina so ya fara haifar da bala'i, na tabbata akai na so ya fara haifar da cuta mara magani, tun kafin aje ko ina so ya fara min haka to ina kuwa in na fara zama ina yiwa so biyayya...".
Goge fuskarta tayi kafun ta dubi Dr.Aqeel da Huzaif da suka zuba mata idanu cikin halin ta shin hankali.
"Kace kana so, kai ma kace kana so sannan kuma shima...".
Sai kuma tayi shiru tana duban Dr.Karami da ya zama wani butum butumi gaɓadaya ya kasa motsi a yarda yake tsaye kawai numfashi ke fita a jikinsa amma ya tabbata ba abin da yayi saura mai motsi a ko ina a jikinsa bai taba tsammani zai shiga tashin hankali irin na yau ba bai taba zaton zai ga bala'in rayuwa ba irin na yau sai yau ya kara ganin wautarsa da gangancinsa ya kara tabbatar da maganar hausawa nacewa 'BAR RAINA ALLURA KARFE CE' in ya cire rashin dacewa ya cire ganin kankata ya dauko ma'aunin so a yarda yake ya ajje a zuciyarsa da duk haka bata faruwa ba ga shi yanzu abin da ya raina yana kokarin haifar masa da CIWON RAI mara magani.
"Baseera ban san wata ƙaddara bace ta jingino mani wadannan mutanan ba, ban san mai yasa ALKALAMIN ƘADDARA da ya tashi rubuto min tashin hankalin rayuwa ba, ya jehomin ta hanyar so...".
Da sauri ta iso gareta tana mai rufe mata baki.
"Karki ce haka ki dauki komai a matsayin jarabawa sannan kuma ƙaddararki ta rayuwa...".
"zan dauki komai a matsayin ƙaddara amma ban da lamarin na domin na tabbata bala'i ne bala'i mai ansa suna bala'i domin na tabbata duk ikirarin da suke yi suka ce suna sona ba wanda yake tausayi na a cikin sun in da suna sona ba za su so su gannin cikin bala'i ba amma da yake su masu son kai ne ko wanne ya dauko tawagar rigunan bala'in sa ya jinginawa rayuwata".
A hankali ta fara taku tana kokarin barin wajan kafin ta tsaya ta juya tana duban su.
"UKU BALA'I kuka dasa min a rayuwa domin ba zan kira shi UKU ALHERI ba kuma ina so ku sani dukkan ku ina son ku ko wannan ku na saka shi a zuciyata yanzu abin da ya rage a tsakanin ku sai ku zo ku dandatsani kowa ya dauki kason sa".
Ta na gama fadin haka ta juya cikin sassarfa kuka na kara tunkodo mata zuciya hannayenta ta saka ta toshe bakin ta har ta fada cikin gida a zaure ta durkushe tana faman jan numfashi hawayen da take so su zubo mata sun ki zuwa kukan ma lokaci guda ya tsaya cak! kanta ta daga sama ta runtse hannayenta duk biyu ta dora a saman kirjinta tana faman haki kafun lokaci guda numfashinta ya dauke idanuwanta suka ƙaƙƙafe.
Ihu Baseera tayi lokacin da ta biyo bayanta taga halin da take ciki da sauri ta isa gareta ta kai hannu tana kokarin jinjingata amma ina lokaci guda ta bingire kasa ba alamun numfashi hakan ya kara sanyata sake kurma wani uban ihu tayi waje da gudu a daidai lokacin su su duka ukun sukayo cikin soro Dr.Karami har yana cin karo da Baseera da sauri ya rikota tana kokari faduwa ya fada cikin soron a daidai lokacin kuma Umma da Goggo Marka gami da Hafsat suka duro cikin soron ganin Mariya asheme ba alamun rai ya sanya kowa sakin salatin Dr.Karami yayi kanta yana kokarin daukarta Dr.Aqeel yayi saurin riko shi fizge kansa yayi yana yin kurin sake kaimata sura Umma dake tsaye ta shiga duban su su duka ba wanda bata sani ba da sauri ta isa wajan da Mariya take yashe ta durkushe tana mai dundubata kafin da dago ta dube su da hawaye a fuskarta.
"Yaa Allah".
Ta fadi tana mikewa kafun ta dubesu ba tare da wani firgici ba.
"Sai ayi kokarin yi mata suttura a kai ta gidanta ko saboda Allah yayi mata cikawa".
Ba wai Dr.Ƙarami da su Dr.Aqeel ba kadai ba hatta Baseera sai da numfashinta ya dauke.
Saukar ruwan da suka ji ne ya dawo da su hayyacin su Hafsat ce dauke da rusheshen baho tsaye tana faman yatsine fuska sai faman kallon uku ahu take jifan su dashi take yi gabadayan su a firgice suka dawo hayyacinsu sai faman kara kaina sukeyi a tsakanin su sun rasa abin yi ma Dr.Karami ya ja tunga ya tsaya yana mai da numfashi kafun ya dubi in da Mariya take yashe har zuwa lokacin dai jiya-i-yau ƙura mata idanu yayi sosai yana kallonta tun daga babban dan yatsanta har zuwa kanta gata nan sambal! Kansa ne ya shiga juyawa yana dawo masa da maganganun da Umma tayi da karfin gaske ya toshe kunnuwansa yana furta.
"Nooooo!".
Kafin lokaci guda ya sureta kamar wanda ya dauki 'yar tsana ya fice da ita daga cikin soron gidan dukkan su suka goya

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads