Header Ads
Showing 96001 words to 99000 words out of 227252 words

Chapter 33 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

1408

Ads at the middle of Article

iya cewa komai ya faru domin daga lokacin ko kalma daya ba ta sake shiga tsakanina da Dr.Karami ba sosai na tsoro ta da irin kallon da yake mani a lokacin ko dai dai ban san tsananin bacin rai ba amma lokacin na lura da yanayin da ya shiga na bacin rai sosai domin har sai da fuskarsa ta nuna".
Hawaye ne suka zubo mata da sauri ta sanya hannu ta na shafe su Baseera ce ta dafa mata kafada tana girgiza kai alamun ya isa haka ta daina zubda hawayen.
"Meye tsakaninki da Dr.Karami".
Kamar daga sam taji Baseera ta watso mata tambayar wanda hakan ya bata mamaki sosai nan tayi fakare da jajayen idanuwanta tana duban Baseera cikin yanayi na ban gane in da kika dosa ba.
"Bakomai".
Ta kokarta ta fadi amma tana jin yarda zuciyarta ke karya ta ta akan abin da tace ita a karan kanta ta sani akwai wani abu mai girma tsakanin ta da Dr.Karami amma har zuwa wannan lokacin ba ta san menene ba, ba ta san yarda zata fassara yarda take ji game dashi ba...
"Shi kuma Dr.Aqeel fa?".
Kamar daga sama ta tsinkayo muryar Baseera ta sake fadi.
Sosai ta shiga dubanta a wannan karon tana kallon idanun Baseera da yanayin da fuskarta take nuna alamun maganar da take yi da gaske, ba alamun wani wasa a ciki kan ta shia gyaɗawa kafun ta ja numfashi.
"Ban san me zan ce miki ba akan sa, amma dai shima...".
"shima ba komai din ko?".
Baseera ta katse ta da sauri tana mikewa kan kafafuwanta girgiza kai tashiga yi tana faman sakin yake mai kama da ciwo sosai a zuciya da ruhi take ji, taku biyu zuwa uku tayi kafun ta tsaya waje guda ta juyo ta fuskani Mariya sosai hannayenta sarke a kirjinta kallon sosai tayi mata kafun ta fesar da wata iska mai zafi.
"Huzaif fa shi kuma a wani mataki yake a gareki?".
Runtse idanu tayi tana mai tallabe kanta da take jin yana dauko mata wani lamari a bangarori duk ukun ba tasan me yake kokarin tarwatsa mata kwanya ba sosai tajin komai na kwance mata tunani ne barkatai taji suna kawo mata farmaki.
"Yaa Allah! ban san abin da zana ce dake ba Baseera komai nawa ba ya kan mizanin natsuwa da zan iya warware miki".
"Eh dole kice haka mana kuma dole komai ya rikice miki ki kasa gane in da komai na filin duniyar ki ya dosa".
Duban ta take yi cikin rashin fahimta sosai ta kasa gane maganganun da Baseera ke yi a hankali taja numfashi kafun ta fesar da iska mai zafi.
"Da gaske nake sanar dake ban san komai ba".
A hankali Baseera ta tako ta iso gareta kafadarta ta kama ta girgiza sosai idanuwansu suka sarke a juna.
"kisan me yake faruwa dake?".
Girgiza kai tayi.
"Kin san abin da yasa kika shiga wannan matsalar ko ma nace matsaloli?".
Nan ma girgiza kai tayi izuwa lokacin jikin ta ya fara sanyi gabanta na tsananta bugawa tana jin yarda zuciyarta ke harbawa da sauri-sauri.
Murmushi Baseera ta saki tana mai gyada kai kallo daya zakayi mata ka gane kallon tausayi da rauni take jifan Mariya dashi sai da ta ja numfashi sosai ta fesar kafun ta dauki gorar ruwa ta bulbulawa cikinta zuciyarta taji ta dan sarara da tashin hankalin da take hangowa Mariya a rayuwa ba ta san ta ya zata fara sanar da ita halin da take ciki ba ba ta san ta ya ya zata fahimtar ita ba tare da ta shiga tashin hankali ba ba ma wannan ba sosai take ji a jikinta abin fa ba sauki mutuwar arne.
Tana numfasawa zuciyarta na kara mata kwarin gwuiwa akan kawai ta fahimtar da Mariya ita ce hanya daya da take gani komai zai gyaru har a samu mafita.
"Mariya ba zan boye miki ba a yarda na fahimci lamarin nan gabadayan wadannan mazajen da kike gani su uku kishi ne a tsakanin su".
Wani irin duba na razana Mariya tayi mata tana sauke hannun da Baseera ta daura mata a kafada ta shiga ja da baya a hankali tashiga motsa laɓɓanta.
"Ban gane kishi suke yi a tsakanin su ba a akan mi suke kishi".
"AKAN SONKI duk kan su son ki suke yi so kuwa mai tsanani ko wanne a tsakanin su akwai kalar so da yake yi miki tun kafun wanann lokacin...".
Sulalewar da Mariya tayi ne kasa tare zaman yan bori ya sanya Baseera dubanta tana tsaigaitawa da maganarta ta.
Hawaye ne shaɓe-shaɓe ta hanga idanuwan Mariya suna zuba ta hade hannayenta duk waje daya ta daura a kai lokaci guda ta hade jikin ta waje guda kamar mai jin sanyi ko wacce za a rabata da wani abu nata.
"Na Shiga uku".
Ta fadi tana mai bajewa kan Capet din dake malale tsakar dakin kamar wacce aka tsikara kuma ta mike zumbur tana duban. Baseera da wani irin yanayi.
"Ban yarda ba wallahi wannan ba gaskiya bane hauka suke yi wallahi hauka suke yi haba mana Baseera kamar ni za su ce suna so ki dube ni fa guda nawa nake a filin duniyar nan suke kokarin kashe ni da raina wannan wani irin Bala'i uku ne nake ciki ni Mariya".
Haka ta saki baki tana sambatu kamar wata zautacciya kafun ta durkushe ta saki wani irin kuka mai zafin gaske da jefa zuciya cikin wani irin raɗaɗi na tashin hankali wanda ba tsammanin yankewarsa.
Baseera dake tsaye bata san lokacin da idanunta ita ma suka shiga zubda kwalla ba wani kuka ta ji ya zo mata da sauri ta sanya hannu ta toshe bakin ta tana karasawa wajan Mariya ita ma ta zube nan suka rugumi juna suka shiga rera kuka aka rasa mai rarrashi wani daga cikin su....


*_KAMALA MINNA_*😍😍😍
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I


NA


KAMALA MINNA


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*


​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.

BABI NA ASHIRIN DA TAKWAS.


A hankali ta turo kofar dakin ta shigo tafiya take yi cikin natsuwa da kuma yanga da ta zame mata jiki da wuya kaga Areefa na tafiya da sauri-sauri a,a sai dai ka ga tafiyar ta kamar mai koyo duk hakan na cikin salo da take amfani dashi cikin filin duniyar rayuwarta sanye take da doguwar Riga Gown wanda tayi matukar amsar jikinta sosai da sosai ta fiddo mata da asalin kyanta da kuma fatarta mai haske wanda tayi Fresh sosai da sosai hutu da jindadi sun taimaka kwarai wajan bayyana a jikin ta kanta ba kallabi sai dai ta tufke gashinta ta sanya rinbos mai kalar pink ta saki jelar gashin na reto a bayan ta fuskar nan fayau ba alamun ko digon tabo na kuraje.
Ba ta shafa komai ba natural fatarta kawai ce ke kyalli manyan idanuwanta masu haske sun kara taimakawa waja fiddo da kyan fuskarta hancinta dan madaidaici shi dai ba za a kira shi dogo ba sannan ba za ace dashi gajera ba yana tsaka tsakiya haka bakinta mai dauke da manyan laɓɓa masu kalar ja kadan ba sosai ba suma sun taimaka wajan kara bayyanar da kyan fuskar ta na halinta da Allah yayi mata.
A yanayin da ta shigo dakin in ka kalle ta zaka gane akwai abun dake damun ta a filin duniyar rayuwarta bisa yanayin da take yatsine fuska kamar wacce aka sanya dole shan magani sai faman kaɗa idanuwa take yi tana bin dakin da kallo.
Hajiya Layla dake zaune can gefe guda tana faman goge jikinta da shawul da alamun wanka ta fito take tsane jikinta.
Fuskarta take kallo cikin wani irin yanayi tana yatsine fuska tana duban MADUBI dake tsaye a bangon dakin.
Shigowar Areefa ya sanyata tsayawa da abin da take yi ta juyo ta dube ta kafun ta mai da kanta wajan fuskartar madubin.
A hankali ta karasa takowa ta iso gareta idanu suka hada ta madubi duk fuskokin su cike da damuwa sosai.
"Maama Lafiya kuwa na ga fuskar ki wani iri daban kamar akwai abin dake damun ki ko?".
Areefa ta fadi tana mai yawatawa idanuwanta cikin na Hajiya Layla.
Numfashi ta ajje mai tauri kafun ta juyo ta dubi Areefa sosai da sosai kafun ta ajje shawul din tana mai riko hannun Areefa tana damkewa cikin nata kamar zata muntsuke sosai Areefa ta ji rikon har sai da ta rintse idanunta tana furta.
"Ouchhh!!".
Dubanta tayi tana jin zuciyarta na wani irin shiga yanayi sosai take jin rashin dadi a jikinta gabadaya a hankali ta fara motsa laɓɓanta tana son yin magana amma kafun ta kai ga furta kalma daya tari mai karfi ya turnuketa ta shiga yin sa ba k'ank'autawa da sauri Areefa ta ware idanu tana dubanta cikin yanayi na tsoro ta rikota sosai ita ma ta isa da ita daidai karamar kujerar dake gaban Madubin ta zaunar da ita har zuwa lokacin tarin bai lafa ba kwace hannunta tayi daga rikon da tayi mata ta fice daga cikin dakin cikin minti daya ta dawo hannunta rike da glass cup mai dauke da ruwa da sauri ta kai bakin Hajiya Layla wanda a lokacin tari ya tsaigaita sai dai wani lamari da Areefa ta gani ya so tayar mata da hankali domin kuwa wani bakin abu taga yana fita daga bakin Hajiya Layla.
"Yaa Rabb!".
Ta furta tana mai janyo shawul din tana goge mata baki sannan ta sake mika mata ruwan zuwa bakinta kadan ta sha ta kau da kanta.
"Maama meke damunki haka baki da lafiya ne tashi mu tafi asibiti a duba ki mana don Allah kin ji".
Yanayin da Areefa take maganar duk a rikice hakan ya sanya Hajiya Layla kakalo murmushi ta ajje a fuskarta duk da raɗaɗin da take jin zuciyarta nayi da wani abu mai girman gaske da ya tokare mata kirji sosai take jin tashin hankali komai take ji na duniyar ya sauya mata ba tun yau ba kusan shekara uku kenan take jin canji a jikinta tayi zayar zuwa asibiti wanda ita a karan kanta ba za ta ce a ga dadi ba sosai ta fara nadamar rayuwar da tayi a shekarun baya sosai take jin daci a zuciyarta dama ruhinta gabadaya nisawa tayi tana mai sake kakalo murmushi tana daurawa a fuskarta domin ta lura Areefa ta shiga tashin hankali matuka ganin yanayin da take ciki wanda ta hakikan ce ba laifin kowa bane sai nata ita ce silar komai da komai a rayuwarta.
"Uhmm Ya isa haka Areefa ba komai fa kawai dai tari ne ya tsarke ni magani na sha shine fa tun dazu nake wannan tarin amma yanzu naji komai ya yi sauki ki kwantar da hankalin ki".
Rausayar da kai tayi cikin yanayi na sanyin jiki idanuwanta na duban Hajiya Layla da alamun bata gasgata abin da tace ba amma ba zata iya yi mata korafi ba a yarda take kallon ta a matsayin uwa mai kaunar 'yar ta a filin duniyar nan ba za ta mance halaccin Hajiya Layla ba a duniyar ta ba zata taba manta taba domin tayi mata komai na rayuwa ita ce ta sauya mata komai na filin duniyarta a lokcin da ta rasa gata ta rasa wanda zai kula da rayuwarta ya taimaka mata ya ji k'anta a lokacin da ta rasa 'yancita da komai nata a lokacin da take bukatar taimako ta rasa a lokacin Hajiya Layla ta fado rayuwarta tayi mata suttura da taimakon Allah ita ta taimaka mata ta dawo cikakkiyar mace mai 'yanci wacce ba wulakanta ba duk da KETA HADDI da akayi mata aka ci zarafin ta a matsayinta na mace mai rauni a filin a rayuwarta.
Bata san hawaye na zuba a fuskarta ba sai da taji hannun Hajiya Layla na dauke mata su da sauri tayi firgigin ta dawo hayyacin ta suka kurawa juna ido kafun Hajiya Layla ta shiga girgiza kai.
"Haba mana Areefa har sai yaushe ne idanuwanki za su dai na wahalar da kan su ne har sai yaushe zaki daina zubda hawaye akan abin da ya riga ya wuce bana so ki daina kawai kin ji ko".
Gyada kai ta shiga yi kamar wata kankanuwar yarinya kafun ta sanya hannu ta na kara goge fuskarta tana k'akalo yaken dole tana ajjewa a saman fuskarta.
Kuri Areefa tayi wa Fuskar Hajiya Layla tana yawatawa da idanuwanta kafun ta nisa.
"Maama me ya samu fuskarki haka duk tayi wani iri kamar wacce ta kone da wuta sosai naga ta canza tana tattarewa?".
Murmushi tayi wanda ya sanya zuciyarta da ruhinta ciwo sosai wasu HAWAYEN ZUCIYA taji suna ta kwaranyo mata sosai ta san za a yi haka ta san komai daren dadewa sai yanayin nan ya faru da ita wanda ita a karan kan ta ta san ita ce silar faruwar komai a gareta numfashi ta fesar mai zafi kafun ta motsa laɓɓanta.
"Ban san ta ya ya zan sanar dake halin da nake ciki ba, ban san ta ya ya zan sanar dake lamarin da na daura wa kai na ba gashi yanzu yana kokarin illa tani ban san mai ya kai ni haka ba ban san mai yasa na kasa godewa Allah da baiwar da yayi mani ba na butulce masa da sani na".
Shiru tayi tana jin yarda zuciyarta ke zafi da radadi rufe idanuwanta tayi ta buɗe su akan Areefa da tayi fakare tana kallon ta sosai taji tausayin ta sosai jikinta yayi sanyi da kalaman Hajiya Layla ko da bata ji abin da ya sanya ta shiga damuwa haka ba ta tabbata abin ba mai dadin bane a filin rayuwarta da alamu kuskure tayi ba tare da ta san kuskure bne a rayuwarta.
"Areefa kin ga yarda fuskata take a haka cikin rashin kyan gani to haka duk wani sassan jiki na yake".
Tana maganar tana janye shawul din dake daure daga kugunta zuwa kasa cinyoyinta ta bude sosai Areefa ta tsorata tana mai runtse idanuwanta kafun ta buɗe su a hankali zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri kafar Hajiya Layla take kallo har zuwa cinyarta gabadaya sun sauya kala kamar wanda tayi muguwar k'una ta bada tangarɗa wajan warkewa duk tayi wani bakinkirin ga wasu dikon dikon kuraje marasa kyan gani dago idanunta tayi ta dubi Hajiy Layla dake faman sakin murmushi wanda yafi kuka ciwo.
"Maama me ya same ki haka a jiki nace baki da lafiya kin ce a,a ba haka ba ga kuma jikin ki ya nuna alamun baki da lafiya".
Areefa ta fadi tana kai hannunta saman fuskar Hajiya Layla tana tabawa cikin yanayi na tsoro a fuskarta runtse idanu tayi jin yarda fatar tayi wani irin tauri da wani giris-giris kamar an shafa mata dakanken gawayi.
"Wai meye haka a jikin ki Maama sosai fa jikin ki ya baci fa dubi kafarki ji fuskarki Maam muje asibiti a duba fatarki anya ba cutar fata ba ce ta kama ki?".
Girgiza kai kawai take yi cikin matsananciyar nadama da dana sani kafin ta ciji laɓɓanta.
"Ba cutar fata bace Areefa ni na sanya wa kai na ba laifin kowa ni na ja wa kaina".
Cikin rashin fahimta Areefa ke dubanta tana kara buɗe idanuwanta sosai cikin yanayi na firgici da abin da take ji Hajiya Layla na fadin.
"A can baya ni BAKAR MACE ce mutane da yawa suna yabawa na kalar fata ta duk da bakar ce amma ana cewa ina da kalar fata me kyau ba kowa bane ake samu da irin ta Natural skin ce mai wuyar samu domin da wuya ki ga fatar jiki na ta tattare ko ta yi kuraje ni kaina nasan ina da kyan fa sai dai abin takaici abin haushi a lokacin ni kuma ba abin da nake kauna kamar farar fata da yawan kawayena in suka ji ina cewa ina kaunar farar fata sai su ce bani da hankali ban san abu mai kyau ba har cewa suke yi da ana masayar fata dani za suyi ni kuwa a ganina hauka ce kawai suke yi me ake yi da bakar fata ga 'ya mace budurwa mai aji ai bakar fata sai namiji wanda ya gaji wuya da shiga rana ba 'ya mace ba da aka sani 'yar hutu da da zaman jindadi.
Duk kururuwar da zuzutawa da akeyi mani ina da kyan fata hakan bai hanani burin canza kalar fata ta ba a lokacin na shiga bincike har sai da na gano irin maya-mayen da ake shafawa ake canza fata zuwa fara a lokacin ba karamin dadi naji a rayuwa ta ba nayi farin ciki mara musaltuwa tun daga wannan lokacin na canza mayuka na da nake amfani da su haka sabulai na duk sai da na canza ban yi sati guda ina amfani da su ba na fara canzawa fuskata ta fara haske a lokacin mutane da yawa sun so nusar dani amma ina na yi kunnan uwar shegu da su na cigaba da harkar ta in takaice miki cikin kankanin lokaci na sauya gabadaya nayi fara tas na koma kamar in kika latsani jini ne zai fito daga jikina sosai na sauya komai nawa ya canza mutane da yawa sun nuna rashin kyautawa akan abin da nayi domin cewa ma suke yi na koma sam bani da kyan gani fatata tada ta fi dacewa dani ni kuwa ko a jikina Areefa na fi shekara goma sha biyar ina wannan abun tun ina kuruciya ta har zuwa tsufana ban daina ba domin ban gano illar haka ba sam sai da shekaruna suka ja fatar jikina ta fara gajiya domin ta rigaya ta gama rauni sosai komai nata ya gama komawa nakashasshe".
Shiru tayi tana shafar kafafuwan ta da suka koma kamar mai ciwon kuturta.
"Bani da yarda zan yi yanzu domin ni na jawa kaina duk abin da ya faru dani ni ce sila".
Ta karasha cikin raunin muryar kafun ta miki ta isa gaban madubi ta janyo robar mai basilin tashiga muttsukawa jikin ta a hankali idanuwanta na kan fatarta tana kallon yarda ta sauya gabadaya kamar wata mai cutar kuturta nisawa tayi ta dubi Areefa da tayi fakare tana bin ta da kallon ko motsi ta kasa yi.
"Yau ba zaki aiki bane hala lokaci fa na tafiya".
Sai lokacin Areefa ta kaɗa idanuwanta tana mai jan numfashi ta bude idanunta sosai ga Hajiya Layla wani irin tausayinta take ji yana samun masauki a zuciyarta da ko ina na gangar jikinta girgiza kai ta shiga yi alamun ba za ta je ba domin yanayin da

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads