Showing 99001 words to 102000 words out of 227252 words
Chapter 34 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt
take jin jikin ta duk yayi sanyi kalaman Hajiya Layla ba karamin sanya zuciyarta rauni sukayi ba.
Ware idanu Hajiya Layla tayi ganin abin da Areefa tayi kallonta tayi tana ma tsuke fuska.
"Maza wuce ki shirya ki tafi aiki kin ji ko akan me zaki ce ba zaki ba ke da ba wani abu ke damun ki ba".
kau da kai tayi tana kokarin yin magana Hajiya Layla ta daga mata hannu.
"Bana bukatar naji komai kawai ki tafi nace ki shirya ki wuce Office".
Ba ta sake yin magana ba gani ba wasa a fuskar Hajiya Layla din cikin sanyi jiki ta ja jiki ta fice daga daga dakin.
Kamar jira take yi Areefa ta fice ta zube kan gado gami da zabga uban tagumi tana mai runtse idanuwanta sosai taji kanta na sara mata zuciyarta na zafi da wani irin yanayi mai girman gaske nadama sosai take yi tana jin kunyar kanta fita ma waje kunya take ji ba ta so su hadu da muta ne gani take yi kamar kallon banza da kallon kyama suke yi mata.
*******
A hankali ta karasa shigowa cikin harabar Company din can gefe inda aka tanada Parking Space ta isa ta ajje motarta sai da ta shafe mintina kafun ta fito daga cikin motar hannun ta rike da Key sai jaka kunnanta kuwa iyafis ta mak'ala fuskar ta kawai zaka kalla ka gane akwai damuwa tattare da ita.
A hankali ta fara taku lokaci-lokaci tana lumshe idanuwanta har ta isa babbar kofar da za ta shigar da ita cikin wajan aikin nata Securty suna yi mata sannu da zuwa amma ina hankalin ta yayi dogon zango.
Ko da ta isa ciki ba wanda ta tsaya kallo har ta isa wajan gefen ta ta buɗe yar karamar kofar da kayi domin kare wajan zaman nata ta buɗe ta shiga ta zauna tana sakin numfashi kadan-kadan table din dake dauke da computer da file ta duba kafun ta janye files din da taga an anje mata gefe kanta ta daura akai tana tallabewa da hannayen ta zuciyarta take ji tana tayi mata wani irin sosai take jin rashin dadi a jikin sosai komai taki ji nata ya sauya yau daya wani irin kunci da zafin zuciya take ji sam bata so wani ya zo ya takura mata shiyasa bata so fitowa aiki ba amma ba yarda za tayi ne shiyasa...
Kwakwasa mata kofa da akayi ne ya sanya ta dago kai tana mai sakin guntun tsaki Sakatariyar Dr.Erena ce tsaye sai faman wani shan kamshi take yi tana harare harare kamar wacce ke kokarin kai duka.
"Sir ya ce sai ki zo".
Ta fadi tana wani basarwa kamar ba da Areefa take yi ba.
Sosai Areefa ta ware ido tana kallon ikon Allah wai suruka ta mari uwar miji ita abin ma dariya ya so ya bata wai batar basira rokon Allah da goge sai da ta gama kalle ta kafun ta ja wani dogon tsaki tana mai da kan ta kasa ta na kwanciya.
kwankwasawa taji an sake yi da sauri ta dago cikin bacin rai ta mike kan kafafuwan ta tana dubanta.
"Ke! ina wasa dake ne ko ni tsaran ki ce ba sako aka baki ba kin fadi ba sai ki tafi ba ko da sauran wani abu ne?".
Areefa ta fadi cikin daga muryar har sai da sauran ma'aikatar hankalin su ya yo kan Areefa da sauri ta fizgi wayar ta ta fito ta tsaya gabanta tana watsa mata wani irin kallo kafun ta ja wani tsaki ta wuce abin ta. ta bar ta shanye da baki cikin yanayi na tsoro don bata taba tunanin Areefa haka take ba tun da ta fara aiki a Company din ba tayi zaton tana da fada haka ba ashe kallon kitse take yi wa rogo kwaɓe baki tayi kafun ta ja jiki ta bar wajan tana duban Sauran ma'aikatan da suka kureta da ido kamar za su lashe duk sai taji kunya ta kamata.
Ko da Areefa ta isa Office din Dr.Erena banka kofar tayi ta shiga cike da bacin rai tsaye ta hangeshi sai faman safa da marwa yake yi jin banko kofar da akayi ne yayi sauri tsaya cak! Yana duban kofar ganin Areefa ya sanya shi ware idanu musamman ganin yarda ta shigo kamar wacce zata rufe shi da duka.
"Dr.Erena ya kamata ka san wani abu ba wai don ina karkashin ka bane ina aiki zai baiwa sakatariyarka dama wani duk da yake cikin ma'aikatar nan raina ni ba fa maula na zo yi ba aiki na zo yi kamar kowa da yake tutiyar aiki ya zo yi don haka ba wanda ya isa ya taka ni na kyale shi".
Ta karashe tana fesar da iska mai zafi shi kan sa sai da ya razana da yanayin ta da sauri ya iso gareta jikin sa har rawa yakeyi.
"Lafiya me aka yi miki wani dan iskar ne ya bata miki rai a cikin Company nan nawa?".
Yanayin da yake maganar cikin yanayi na harzuka ya sanya Areefa duban sa cike da mamaki kafun ta kau da fuska.
"kar ka sake tura mani sakatariyarka in kana nema na ai akwai waya ko ka kira ni mana".
Tun kafun ta dire maganar ta taga ya figi jikin sa yayi kofar fita kofar ya banka cikin sauri ya fara kiran sunan sakatariyarsa wacce a daidai lokacin ta iso tana kokarin zama amma jin kiran da Ogan nata yake yi mata ya sanyata sauri mikewa tana rarraba ido kamar wacce ta san bata da gaskiya.
Yana isa gareta ya nuna ta da hannu kafun ya kwasheta da mari ji kake tas! wata kara ta saki gami da kiran 'jesus'.
saura kadan ta hantsila bayan kujera nan ta shiga ja da baya idanuwanta a warwaje ganin yanayin da yake nunata da yatsa cikin matsanancin bacin rai.
"Sorry Sir...".
Wata mahaukaciyar tsawa ya daka mata kafun ya fara magana cikin masifa.
"Baki da hankali uban me tayi miki zaki nemi raina mata wayo dana aike ki cewa nayi ki yi mata rashin mutunci ba cewa nayi kawai ki duba in ta zo ki ce ina kiranta ba da yake ke dakikiya ce shine kika je kina yi mata hauka ko".
ware idanu tayi tana duban hanyar Office din sa da wani irin yanayi na dacin rai a ranta tana sa ba wanda zai mata haka sai Areefa tun da suke da Dr.Erena bai taba ko zaginta ba amma yau ta dalilin ta ya mare ta dubansa tayi cike da takaici kafun ta kau da fuskarta zuciyarta na yi mata zafi ba abin da take yi a zuciyarta sai 'Allah ya isa ba ta yafe ba'
Wani mugun kallo tabi shi dashi lokacin da ta ga ya ja tsaki ya koma office din itama dogon tsaki ta ja zuciyarta kamar ta fashe janyo kujera tayi cikin takaici ta zauna tana dukan saman table din dake gabanta.
Shikuwa Dr.Erena yana shiga Office dinsa zaune ya tadda Areefa sai faman girgiza kafa takeyi fuskar nan ta ta kamar hadari ba karamar razana yayi ba da sauri ya isa wajan yana mai bata hakuri yana kokarin zama kusa da ita tayi saurin jan jikin ta tana wurga masa wani wulakataccen kallon.
"Don Allah Areefa kiyi hakuri waccen tsinaniyar yarinyar ba hankali gareta ba shiyasa don Allah karki bata ran ki akan ta na hukunta ta".
Kallo shekeke tayi masa gami da na raina maka wayo kafun ta ja guntun tsaki tana kokarin tsahi ta fice da sauri ya sha gabanta yana kallon idanuwanta da wani irin yanayi na tsananin so da yake yi mata.
"Haba mana magana fa zamuyi shiyasa nace a kira mani ke don Allah koma ki zauna maganar ba za ta yuwuwa ba a tsaye".
"ka ga don Allah Dr.Erena ka rabu dani bana bukatar yawan magana a daidai wannan lokaci ina bukatar zaman kadaici ni kadai please".
"Areefa don Allah ko mintin biyu ki bani wallahi maganar mai muhimmanci ce".
Duban sa tayi ba tare da ta ce dashi komai ba ta koma ta zauna hakan da ya gani shima yayi saurin jan kujera ya zauna yana fuskartanta sai faman ajiya numfashi yake yi kafun ya kokarta duban idanunta sosai da sosai.
"Areefa ba zan boye miki ba a gaskiya nagaji da yanayin da kike yi mani na shariya da halin-ko-in- kula ya kamata in san matsayina domin ni dai da gaske son ki nake yi kuma ko auren ki zan iya yi...".
wata irin zabura tayi ta mike kan kafafuwan ta kafun ta lailayo wasu tawagar ashariya ta sauke ta dora da fadin.
"Kan Uban can! So Aure fa ka ce Dr.Erena wa zaka aura".
Ta fadi tana mai sakin wani murmushi mai kokarin tarwatsa mata zuciya da ruhi wani daci ne gami da raɗaɗi taji sun saukar mata a zuciya kirjinta yana wani irin bugawa kamar zai tarwatse lokaci guda taji kwanyarta tayi wani irin hautsinewa kamar zata tarwatse itama duban sa take yi da wani irin yanayi na tsana mai girman gaske idanuwanta lokaci guda suka sauya fuskarta tashiga wani kunci runtse idanuwan ta tayi kafun ta sake dubansa ta girgiza kai da sauri ta ja kafarta tayi hanyar ficewa daga cikin office din cike da tashin hankali da a zuciya kiranta ya shiga yi amma ina ko ta kan sa ba tabi ba illa banka kofar da tayi har sai da office din gabadaya ya amsa da sauti mai girman gaske.
Da gudu ta isa kasa ba ta tsaya wata wata ba ta fizgo jakarta ta fice daga cikin wajan da yawan ma'aikata kallo suka bita dashi har fa fice wajan motarta ta isa ta buɗe ta shige tana mai da numfashi kai ta hada da sitiyarin motar gabanta na wani irin dokawa tsanar Dr.Erena take ji tana kara samun filin zama a zuciyarta ko son ganin sa ba ta so ta sake yi ta lura da gaske yake yi kokari yake yi ya gama da ita tun kafun ta cika burin ta akan sa wanda ba zata so hakan ba sam!.
Ya zame mata dole ta canza taku dole na biyo masa ta hanya wacce zata yi saurin cimma kudirin ta domin a gaskiya ta gaji da zuwa wajan gani take yi kamar komai zai lalace yar da ta fuskanci al'amarin Dr.Erena so yake yi yayi mata yawo da hankali wanda ba za ta yarda haka ta kasance ba dole ta sake sabon lale tun wuri....
*_KAMALA MINNA_*😍😍😍
UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA ASHIRIN DA TARA.
Cikin wani irin yanayi ta kai wayar kunnan ta sai faman jan numfashi take yi daƙyar idanuwanta sun kada sunyi jajir kamar an watsa mata barkono zuciyarta take ji tana mikata cikin wani irin waje mai dauke da tashin hankali mai girman gaske komai take ji ya tsaya mata cak! ji take yi kamar motar ta ta tuntsiran da ita ta mace ko ta huta da wannan tashin hankalin da kunar da zuciyarta ke yi tana babbaka duk wani sashi na kirjin ta ruhinta take ji yana wani irin fizga mai haifar mata da wani matsanan cin ciwo a dukkan sassan jikinta.
Girgiza kai take yi tana jin yarda yake wani irin sarawa da duk tashin hankalin da take ciki komai take ji a wannan lokacin yana barazana da duk ragowar farincikin da yayi sauya a gareta na filin duniyarta.
Ba ta san abin da ya sa ta fito yau ba bata san mai alkalamin ƙaddararta yake kokarin rubuto mata ba sosai take jin zuciyarta na haifar da wani kunci mai radadin gaske sosai take jin duk wani sashi na jikinta yake narkewa kamar ba na ta ba kafafuwan da suke kan giyoyin motar take jin su kamar ba a jikin ta suke ba ta tabbata da a tsaye take ba za su iya daukar gangar jikinta ba.
Nisawa tayi a daidai lokacin da taji iska mai nuna alamun an daga wayarta ta buso cikin kunnuwan ta runtse idanu tayi gami da tura laɓɓanta gabadaya cikin bakinta tana cizawa kamar zata fizgesu daga mazauninsu.
A hankali ta fara gangarawa gefen titin domin ba zata iya furta ko da kalma daya a yarda take jin zuciyarta ba, ba za iya motsa wani sashi na laɓɓanta a cikin halin tuki ba ji take yi kamar in ta motsa su komai zai tarwatse a gareta.
Sai da ta shafe mintina biyu kafun ta ja wani dogon numfashi ta fesar mai matukar ciwo.
"Alhaji Abdulwahaab".
Ta fadi can kasar makoshin ta kamar wacce akayi wa dole sai ta ambaci sunan.
"Na'am Areefa".
Ya ansa da yanayi na farinciki a muryarsa.
Runtse idanu tayi kafun ta sake jan numfashi.
"Kana ina Please I need your help right now?".
Yanayin da take furta kalmar cikin sauti mai rauni ya sanya Alhaji Abdulwahaab yin sanyi sosai.
"What is wrong with you Areefa me ke faruwa dake ne naji muryar ki So Sad?".
"Kana ina right now Alhaji Abdulwahaab don Allah ina son ganin ka ko a ina kake ka fada min gani nan zuwa".
Sosai muryarta tayi rauni kamar zata fashe da kuka a hankali ta kai hannunta baki tana toshewa.
"Ok...Cool down Please yanzu haka ina Muhabbir Coffee daidai Alo-Vera Hotel ki zo nan ki same ni".
Ba ta ji ra abin da zai ce ba da sauri ta sauke wayar tana cilli da ita kan kujerar dake gefen ta wani wawan ribas tayi tare da juya akalar motar ta koma kan titin sosai ta hau hanya.
Zabga gudu take yi kamar wacce zata tashi sama ita akaran kanta ba ta san ta nayin sa ba zuciya ce kawai ke aikinta domin ba ta cikin hayyacita motoci da yawa sai dai su kauce mata domin sun lura ba ta cikin hayyacin ta cikin mintina kalilan ta hau titin da zai kai ta alo-vera Hotel kwanar da zata sha saitin W. I .WUSHISHI ESTATE. Sukayi a rangama da wata motar saura kadan su haye juna Allah ya tsagaita amma duk da hakan ta bugar wa mai motar fitilu har sun dan tsage hannu kawai ta daga masa alamun bashi hakuri ta shiga layin girgiza kai yayi mai motar don ya lura bata cikin hayyacin ta.
Tun kafun ta isa Muhabbir Coffee din tayo parking din motarta gefe guda ta fito cikin hanzari murfin motar ma da kafarta ta tura ta shiga sauri kamar zata kifa har tana turgudewa Allah ya taimaka bata je kasa ba.
Ta shiga Get din wajan ta shiga rarraba idanu can gefe guda ta hango shi yana dago mata hannu kamar wacce aka ingiza haka ta tafi tana isa ta tsaya kinkam! A tsaye tana mai da numfashi ta shiga nuna kanta da hannu kirjinta sai faman dagawa yake yi idanuwanta na juyawa kamar mai shirin zubewa a kasa da sauri Alhaji Abdulwahaab ya mike don ya lura bata cikin hayyacinta jakarta ya riko ya ajje kan Table din dake wajan kafun ya riko hannunta ya zauna da ita sosai gorar ruwan dake ajje a wajan ya murɗewa kai ya tsiyaya cikin Glass Cup ya mika mata kau da kai tayi cikin wani irin yanayi.
"Haba mana anshi ki sha ko kya samu sa'ida a zuciyarki".
"Bana tunanin ruwa zan yi mani wani amfani a halin da nake ciki a yanzu".
Ta fadi cikin wani irin yanayi tana daura hannayenta saman goshinta da take ji kamar zai dare gida biyƴ.
"Ki ansa ki sha Areefa ruwa zai miki abin da baki taba zato ba".
Ba ta bukatar surutu da yawa don haka ta anshi ruwan ta kai bakinta aiko sai gashi ta take ruwan gabadaya ta dire kofin da karfi har sai da ya tsage don wahala runtse idanuwanta tayi tana faman sauke ajiyar zuciya a hankali gumi ya karyo mata saman goshi idanuwanta a lumshe sosai taji wani sashi na zuciyarta da ruhinta sun yi sanyi kadan da ta sha ruwan.
Lokaci guda ta ware idanuwanta kan na Alhaji Abdulwahaab da yayi kuri yana dubanta nisawa tayi cikin fesar da wani zazzafan huci.
"Wai ni Dr.Erena yake so har yana ikirarin zai aure ni".
Ta fadi tana runtse idanuwanta zuciyarta take ji tana kartawa da wani irin tashin hankali mai girma wata irin tsana mai tsanani da take ji akan Dr.Erena take samun fili a zuciyarta tana kara hauhawa sosai take jin kalamansa na ansa kuwwa a kwanyarta da zuciyarta.
Da na sani take yi na zuwan Company yau da na sani take yi da har ta je Office din sa ta saurare shi dana sani take yi da har ta bari kunnuwanta su ka jiyo mata kalaman da suke kokarin tarwatsa mata zuciya.
Wasu hawaye ne masu tsananin dumi taji suna biyo fuskarta da sauri ta ware ido tana kai hannayenta tana taba su murmushi take saki mai tsananin ciwo kafun ta dubi Alhaji Abdulwahaab mamaki fal a zuciyarta da fuskarta murmushi taga yanayi har hakoransa na bayyana kafun ya mike kan kafafuwansa yana taku a hankali hannayensa goye a bayan sa.
Juyowa yayi ya dubi Areefa har lokacin murmushin bai kau ba sai ma kara fadada da ya yi dawo wa yayi ya zauna sosai yana daura kafa daya kan daya ya jawo Mug din Coffee yana kaiwa bakin sa da wani irin yanayi na nishadi sai da ya kurba sosai sannan ya dire ya daura hannunsa kan Table din yana dan kwankwasawa har zuwa lokacin idanuwansa na kan Areefa da tayi fakare tana dubansa a wani irin yanayi mai cike da mamaki da AL'AJABI mai girma gaske wanda ya kusan sanya zuciyarta tsalle sama.
"wondefull Story".
Ya fadi yana mai girgiza kai cike da farin ciki kafun ya dora da fadin.
"Sosai da sosai naji dadin wannan ranar a daidai wannan lokacin da na samu daddadar lamari irin wannan How Comes na ce miki yau ce ranar farko da nake hango cinmma nasarata akan Dr.Erena".
Mikewa ya kuma yi kan kafafuwansa hannunsa rike da Mug din Coffee.
"Areefa ya kamata ace wannan lamarin ya samu nishadi a filin duniyar rayuwarki a yanzu...".
"Alhaji Abdulwahaabbb!!".
Areefa ta fadi cikin wani irin sauti mai haifar da ɗaci a saman zuciya tana mikewa kam kafafuwanta idanuwanta a warwaje tana dubansa ciki da kunci zuciyarta na wani irin zafi.
"Ban san mai yasa kake farin ciki da haka ba, Ban san mai yasa kake so nayi farin ciki da wannan lamarin ba, shin ka mance abin da ke tsakanani da Dr.Erena, shin ka mance abin da yasa na ke