Header Ads
Showing 189001 words to 192000 words out of 227252 words

Chapter 64 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

1420

Ads at the middle of Article

ba wacce ta zama sanadin komai sai Mahiafiyarta sosai abin ke taba mata zuciya tayi fadan tayi rarrashin amma ina ta nuna bacin ranta sai ma ake nuna tsanar 'yarta take yi kaicon wannan rayuwa.
Dago kai tayi ta dubi Goggo dake zaune bakin gado ta zabga tagumi kallo daya zaka yi mata ka gane kamar abin bai wani ɗaɗata da kasa ba amma akwai alamun sanyi a jikinta musamman yarda ta ga Abulle ta shiga yanayin tashin hankali.
"Abin da nake ta faman tunasar dake kenan Goggo amma kin kasa gane wa Hafsat mace ce abu kalilan ne zai bata mata rayuwa sangartar da kike nuna mata da wai sunan so ne wallahi BA SO BA NE domin ba in da zai kai ta yanzu mai gari ya waya don Allah Goggo yanzu in wannan abin yafita mai kike zaton zai faru na rantse da Allah ko ruwa gagararmu sha zai yi".
Gyaɗa kai kawai Goggo take yi tana faman turo baki gaba.
"Ai da rufe ni da duka kikayi shine zan san na bata miki rai ko kuma ni na saka Hafsat dauko mana magana a duniyar nan ai ba wanda ya kai ni bakin ciki kan wannan lamarin kuma ai ba kanta farau ba balle ta zama karau uban kowa yana da nashi kashin a gindin sa don haka ban ga wanda zai takura wa Hafsat ba akan abin da tayi ai ba da gangan tayi ba Yaudaren ɗa namiji ne ta gamu da ita da kuma makircin wadancan mutanen...".
"Goggo!".
Abulle ta fadi da muryar sauti don maganar tayi matukar tunzura mata zuciya da sauri ta mike ta dubi Goggo ji take yi kamar ta daura hannu akai ta kurma ihu ko ta samu saukin wahalar zuciya da zafin ruhi da take ji.
"Goggo ni ban ga amfanin daukar hakkin wanda ba su da laifi ba kuma na rantse da Allah in har kika ci gaba da tsanar su Mariya da uwarta wallahi sai hakkin su ya kama ki domin na lura a duniyar nan ba wacce kika tsana kamar ita duk biyayyar da take miki da cin kashin da kike mata ba ta taba daga kai ta dube ki ba tunda ta shigo gidan nan abun dai daya ne matsalar ki take fama da ita kullum ba ta da sauki anya kuwa rayuwa za ta yuwu a haka".
Tana gama fadin haka ta juya da sauri ta fice daga cikin dakin cike da tashin hankali mai girman gaske bata san ya za tayi yanzu ba bata san mai ya dace tayi ba ta san dai Allah kadai ne zai yi mata maganin matsalar ta Allah na gani bata da laifi ta san ƙaddara ce kuma ta ansa da wannan tunanin zucin ta fice daga cikin gidan zuciyarta na harbawa da yarda zata tunkari mijinta da wannan al'amarin domin kuwa ya jima yana cewa Hafsat ta dawo gida amma ba yarda ta iya ta nuna masa yayi hakuri ba wani abu tun yana hakurin har yawan maganganun da ake yi akan Hafsat ya fara tunzura shi to ina ga yanzu yaji wannan bakin labarin.
****
Hafsat kuwa tun da ta fice daga cikin gidan ta dau hanya zuciyarta sai an gizata take yi akan kawai ta tafi gidan su Huzaif domin ba za ta iya zama ba a halin da ake yanzu dole ta je ta same shi duk wacce za a yi sai dai ayi domin kuwa sosai take jin wani mahaukacin son sa na kara nakarkar mata da zuciya yana bubbuɗe mata duk wani sashi na jikin ta yana samun matsugun ni sosai take ta jin ta a tashin hankali wanda tun da take a rayuwarta ba ta taba zaton haka ba yau rana daya gabadaya komai ya kwance mata.
Kuka sosai take yi na zuciya domin hawayen sun ki zubowa tashin hankalin dake kara rikita ta shine yarda mahaifiyarta take kallon ta ta tabbata in kowa zai yi mata uzuri ban da mahaifiyar domin ita kadai ne ta san halin da ta tsinci kanta a ciki a daidai wannan lokacin.
Tafiya sosai tayi wacce akaran kanta ba ta san tayi taba ita dai ta san jefa kafafuwanta kawai take yi a in da taji sun sauka har izuwa lokacin da ta isa inda take zaton gidan su Huzaif ne sosai gaban ta ya shiga faduwa ba ta san mai zata ce ba bata san ya zata kalli mutanan gidan ba shin zuwa zata yi ta ce musu ɗan su yayi mata ciki ko ya ya.
Girgizai kai ta shiga yi zuciyarta na faman harbawa tsoro da fargaba duk suka dire mata lokaci guda numfashi ta ja kafun ta dubi tankameman Get din gidan a hankali ta kai hannu ta shiga kwankwasawa daga can ciki taji motsin ana zare sakata mai gadi ne ya leko ya dube ta sama da kasa ganin ta a hargitse alamun akwai abun da ke damun ta hakan ya sanya shi tambayarta ko lafiya?.
Hawaye ne suka balle mata da sauri ta dauke su sannan ta ce.
"Don Allah wajan mutannan gidan nan na zo wajan Mahaifiyar Huzaif".
Sake kallon ta yayi sama da kasa kafun ya ce.
"Ko lafiya kike niman ta?".
Runtse idanu tayi domin ita dai bata san abin da za ta ce da shi ba a halin da take yanzu in zai bar ta tashi kawai ya barta.
Gefe ya ja alamun bata hanya don ya lura tana wani mataki na tashin hankali a hankali ta shiga share fuskarta sannan ta saka kafar cikin gidan tana takawa zuciyarta na kara curewa waje guda tayi tafiya kadan ta ja burki ta tsaya a tsakar gidan tana mai da numfashi tunani kawai take yi ta yarda zata shiga gidan nan ba ta san a wani matsayi zata je ba ita kanta ya gama kulle.
A hankali ta shiga jan kafafuwanta tana mai da numfashi har ta isa babbar kofar da zai sadata da cikin falon Handle din ta rike ta murɗa idanuwanta a runtse gabanta na tsanarta bugu jin kofar ta buɗe ya sanyata tura kanta gaba gadi domin ta sadakar duk abin da zai faru sai dai ya faru.
Zaune suke kowannan su fuskarsa a cure da alamun bacin rai motsin shigowar da akayi ne ya sanya macen dake tafaman sababi ta tsagaita gabadayan su suka juyo suna duban Hafsat da tayi wiki-wiki kamar wacce tayi wa sarki laifi Huzaif da ke zaune can gefe yana ta faman kumbure-kumbure ganin Hafsat da yayi kamar daga sama bai san lokacijln da ya mike ba cikin yanayi na firgici da tashin hankali yana nunata da hannu bakin sa sai rawa yake yi.
"Ke! Uban me ya kawo ki gidan nan ban ce karki sake kokarin shigowa rayuwa ta b...".
Tun kafun ya idar yaji saukar lafiyayyan mari yayi taga taga kamar zai fadi kasa hannunsa saman kuncin sa runtse idanu yayi kafun ya buɗe su akan mahaifin sa da ke tsaye yana ta faman huci da hannu ya nuna shi bakin sa na rawa magana yake kokarin yi amma ya kasa tari ne ya sarke shi da sauri ya dafe kirjin sa ya koma ya zauna gami da runtse idanu a hankali tarin ya laɓa amma bai buɗe idanuwansa ba zuciyarsa yake ji tana faman zafi bai san abin da ke damun Huzaif ba gabadaya ya rasa gane kan sa sosai yake fuskarta matsala akan ɗa daya tak! da yake dashi.
"Ya akayi baiwar Allah?".
Maihaifiyar Huzaif ta fadi tana duban Hafsat da izuwa lokacin ta fara dana sanin zuwa gidan su Huzaif idanuwanta su ka kawo ruwa sosai hannu ta saka ta dauke su ta fara kokarin yin magana da sauri Huzaif yayi tsalle ya dire gabanta yana famam tunkuɗata waje ita kuwa ta ki tafiya mahaifiyarsa ce ta iso ta riko hannun Hafsat ta dube ta cikin yanayi na rashin wasa.
"Na san ɗana zai iya yin komai don ya cutar dake tunda na ganki cikin wannan halin na tabbatar akwai abin da yayi miki ki faɗa min na rantse miki zan bi miki hakkin ki kuma daga kan ki zai gane hakki ba wasa bane da yake ganin daukarsa ba komai bane".
Sosai Hafsat taji wani iri gabanta ne ya shiga faduwa tunanin take yi ta fadi kowa yaji in ta fadi tana da tabbacin zata iya samun abin da take so kuma zata iya rasa wa sannan in taki fadi ta tabbata Huzaif zai yi nasara a akanta.
Bakin ta na rawa hawaye na mata zuba sosai ta dubi Huzaif girgiza mata kai yake yi yanayin sa lokaci guda ya sauya tsoro sosai ya bayyana a fuskarsa kau da kai tayi jin yarda zuciyarta ke kokarin tausaya masa da yanayin da yake ciki sosai take jin GURBIN SO da ta bashi yana kokarin rinjayar haushin sa da take ji.
"Uhmm dama...kawai dai".
Sai kuma ta shiga taba cikin ta tana runtse idanu.
Mutuwar tsaye Mahaifiyar Huzaif tayi ta shiga ambaton innalillahi wa inna ilahiri raji'un shi kuwa mahaifinsa da ya buɗe idanu lokacin da ya ji Hafsat ta fara magana ganin abin da take nuna wa ba karamin kaɗa 'yan hancin sa sukayi ba mikewa yayi cikin tsananin bacin rai da kunar zuciya.
"Ke muje ki kai ni gidanku yanzun nan Hajiya maganar gaskiya Huzaif na lura aure yake so kuma wallahi in har ina numfashi a doron kasar nan wannan lamarin shine na karshe wanda zai dauko mani ya hanani kwanciyar hankali wallahi tallahi kin ji na rantse sai Huzaif ya auri wannan yarinyar ko da kuwa hakan na nufin numfashin sa zai yanke daga lokacin da na saka limami ya daura musu auren".
Yana gama fadin haka ya fizgi hannun Hafsat yayi waje da ita ba Mahaifiyar Huzaif kadai ba hatta shi kasan din mutuwar tsaye yayi domin bai taba zaton hakan ba duban sa tayi fuskarta da murmushi mai tafe da hawaye ta juya cikin sauri tayi sama shi kuwa kwakkwarar motsi kasawa yayi kan sa ya ji yana juya masa lokaci guda yasaka hannayensa duk biyun ya dafe shi gabansa na tsananta faduwa wani firgici yaji shi a ciki musamman akan furucin mahaifinsa wanda ya tabbatar ai iya tabbata....


*KAMALA MINNA*😘😘😘😘
[10/18, 5:01 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I


NA.


KAMALA MINNA

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*




​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.




BABI NA HAMSIN DA TAKWAS


Ba karamin tashin hankali Hafsat tashiga ba lokacin da taji mahaifin Huzaif yana ta faman sababi tun da suka dauko hanya ko hadiyar yawu ba yayi idanuwansa sun kaɗa sun yi jajir kamar jan gauta ita kan ta tayi dana sanin zuwan ta gidan.
"Ban dan dakikan ci kina 'ya mace har ki zauna namiji ya yaudareki da banzayen kalaman sa ya nemi kashe miki rayuwa a banza a wofi bayan ke kan ki in mai tunani ce ya kamata tun kafin haka ta faru in son ki yake yi tsakani da Allah sai ya fito kuyi aure duk uwar da za kuyi ba wanda zai hana ku amma da yake kan ki a tukunya yake kika saki baki kika aminci da zancen Huzaif wanda ni kaina mahaifin sa Allah na gani ina fargaba akan sa da halayen sa ban san abin da yake damun ku ba 'ya'ya mata a yanzu da yawan ku maza na amfani da ku wajan saka muku son su wanda zai hana ku ganin laifin su sam! wasun ku basa gane SON GASKIYA da SON SHA'AWA".
Kwaɓa yayi gami da dukan sitiyarin motar sai faman jan tsaki yake yi kamar zai tsinke harshen sa.
Numfashi ta ja gami da haɗiye wani abu da taji ya tsaya mata a makoshi lokaci guda zufa ta shiga karyo mata sosai ta tsorata dashi ji take yi kamar tace ya tsaya ta sauka amma ina ta kasa.
Cikin wannan yanayin da kwatancen da take masa suka iso kofar gidan parking yayi sannn ya juyo ya dube ta ganin tayi wiki-wiki da idanu ya sanya shi galla masa harara domin shi dai ba ya ganin laifin maza kamar yarda yake ganin laifin mata domin ba yarda za ayi kina 'ya mace har ki bari namiji ya yaudare ki ba tare da yardar ki ba in har kika nuna masa ba ki yarda ba ai ba dole zai yi miki ba ai so ba hauka bane.
"Maza ki je kiyi mani sallama da mahaifin ki".
Ware idanu tayi gabanta ya yanke ya fadi ita a rayuwarta har mantawa take yi tana da wani mutum wai mahaifi sosai taji wani irin yanayi a zuciyarta yau rana daya taji takaici rashin baiwa mahaifinta lokacin sa yau ga ranar sa ta zo shin da wani idanu zata je ta dube shi bata je masa da kayan alheri ba sai na akasin sa ta san dai ba zata fara ba don ta san izuwa wannan lokacin labari ya kai kunnansa.
"Dake fa nake ko ba nan ne gidan naku ba?".
Mahaifin Huzaif ya katse ta da sauri ciki firgici har tana buge koshin ta a jikin motar ta buɗe murfin ta fito sai faman rarraba idanu ta ke yi sosai ta lura da mutanan layin na ta kallonta da wani irin yanayi ita kanta sai ta ji ba dadi ba yarda ta iya haka ta ja kafafuwanta ta nubi cikin gidan kirjinta na dokawa da tashin hankali.
A tsakar gida ta tadda Mariya na wanki kallo ta bi ta shi kafun ta kau da kai ita kan ta Mariyar kallon ta take amma bata ce da ita komai ba sai yanayim tausayi da ya bayyana a gareta sosai ta lura da abin da take zargi din da gaske din dai cikin ne domin gashi nan har ya fito don ita da duk ba ta lura ba.
Hafsat na shiga cikin dakin ta tadda Goggo Marka zaune tallaɓe da haɓa abin duniya duk yabi yayi mata yawa ganin Hafsat ta shigo ya sanya ta mikewa cikin hanzari.
"Ke kuma ina kika je cikin wannan halin so kike yi jama'a su fuskanci halin da kike ciki ne?".
Kau da kai tayi tare da cizon laɓɓa ba tare da tace da ita komai ba.
"Dake nake Hafsat kika yi banza dani".
Turo baki tayi tare da cewa.
"Zuwa nayi gidan su Huzaif na sanar da iyayensa yanzu haka tare da mahaifin sa nake domin yace sai ya zo ya sami mahaifina".
Gaban Goggo Marka ne ya yanke ya fadi lokaci guda idanuwanta sukayo waje ta daura hannu akai.
"Mun shiga uku in mahaifin ki ya san wannan lamarin ai mun boni".
Dubanta Hafsat ta shiga yi ganin yanayin da ta shiga takaici ya sake kume ta.
"Yana waje fa yana jira don cewa yayi nayi masa sallama da mahaifina".
Da hanzari Goggo Marka ta figi zanin dake rataye ta yafa tayi waje zuciyarta da wani kudiri da ta dauka cikin kankanin lokaci har tuntube take yi wajan saurin tana fita hango shi tayi jikin motarsa ganin hakan ya sanyata tsayawa tana tunanin kafun ta canza fuska ta isa gareshi sam bai lura da ita ba sai ji yayi an bubbuga masa jikin mota da sauri ya juyo ya dube ta ganin ta ya sanya shi rinsinawa yana gaishe ta mai makon ta amsa sai ma wani wulakantaccen kallo da ta watsa masa.
"Ina tsinannan ɗan naka ma ci amana Allah ya wadaran ɗa irin naka".
Duban ta ya shiga yi domin jin maganganun nata yake yi kamar ba gaske ba sai da ya sake dubanta sosai yaga yarda take faman kallon sa a wulakance ya bashi tabbacin kila ita ce mahaifiyar Hafsat sosai yaji ɗacin maganar da tayi a ransa amma sai yaki nuna mata tunda a girme ta girmeshi.
"Ayi hakuri Baba kin san sha'anin 'ya'yan namu na wannan zamanin ka haife su ne baka haifi halin su ba...".
"Ni rufe mani baki kaji ko ai dole kace haka tun da ɗan ka ya gama da jikata ya cuce ta maganar gaskiya ba zan yarda ba dole kasan abin yi tun kafin wannan abin kunyar ya bazu a jama'a su sani don wallahi ba zan lamun ta ba".
Duban ta yake yi da mamaki yarda ta hakikance tana ta faman zabga masa magana kamar shine yayi wa 'yarta ta ciki ko ya ce jikarta kamar yarda ta fadi ba zai yi mamaki ba lura da yayi ita tsohuwa ce kuma zai yarda da cewa RIKON KAKA bai yi ba don ya tabbata in da a hannun iyayenta wannan yarinyar take hakan ba zai taba faruwa ba in har sun san abin da suke yi.
"Ayi hakuri Baba ina mahaifin ta yake".
Wani irin dokawa gabanta yayi jin ya ambaci mahaifin Hafsat yake nema nan da nan jikin ta ya shiga rawa da sauri ta dube shi.
"Baya nan Allah yayi masa rasuwa...kasan abin da za ayi kawai asirinmu a rufe ni da kai da 'ya'yan namu a zubda cikin nan tun kafin kowa ya sani ina ga haka shine mafita garemu...".
"Zubar wa kuma bayan laifin da aka aikawa ubangiji sannan a sake yin wani laifin anya kuwa kina tausayin jikar nan taki anya kuwa kina son ku rabauta ke da ita to a gaskiya ba za ayi haka dani ba abu daya zan iya yi muku shine na aurawa jikarki ɗana ni nayi wannan alkawarin sannan ba za ayi auren ba har sai ta haife abin da ke cikinta ina ga wannan shi kadai ne mafita a garemu".
Duban sa Goggo ta shiga yi cikin wani irin yanayi na rashin baiwa maganar tasa muhimmanci.
"In kuwa haka ne sai dai ta koma gidan ku da zama don Allah na gani ba zan zauna da ita a zo ana zunɗena da gulma ta ba".
Mamaki ne ya sake turnuke shi yau ya kara tabbatar da sakaci da rashin alfanun rikon kakan musamman ga 'ya'ya mata yanzu mai gari ya waya anya kuwa iyayen yarinyar nan sun san halin da 'yar su take ciki kuwa? Sosai yaji haushin yarda take maganganun ta don haka ya dube ta.
"In har ba zaki yarda da abin da nace ba sai dai kowa ya kama gabansa don ba damuwa ta bace jikar ki ce zata shiga cikin gagarin rayuwa ina ma laifina

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads