Header Ads
Showing 9001 words to 12000 words out of 227252 words

Chapter 4 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

1368

Ads at the middle of Article

ka yarda da ƙaddara ko wacce iri ce ta fado rayuwarka".


"ƘADDARA".


malam Bello ya furta kalmar cikin jan numfashi da fada ruɗani.
Ya shiga nazarin kalmar shi dai ana sa tunani ya san abin da ake nufi da ƙaddara akwai kaddara mai kayan farin ciki akwai kuma akasinta shi dai a yanzu ya san kaddarar sa ba mai dadi ba ce.


"likita kayi min bayani yarda zan fahimta zuciya ta na cikin bala'i".


Ya fadi yana mai dauke gumin dake karyo masa kamar wanda ya fito daga surace hannunsa daya kuma jariri ne sai faman wuntsil-wuntsil yake yi yana tsotsar hannunsa alamun yunwa yake ji.


"...Uhmm nace ya kamata ka nemo wacce zata kula da ita na dan lokaci kafin komai ya zama daidai".


Likita ne ya fadi haka cikin rashin abin cewa.


Kallon sa yake yi, kallo na tuhuma mai cike da son karin bayani akan komai, kallon sa yake yi na rashin yarda da yanayin da ya gan sa a ciki, kallon sa yake yi cikin bugun zuci da ruhi. idanuwansa ya shiga juyawa akan ko wani dayan su cikin yanayi na kara tsoro da fargaba gani yake yi kamar Habeeba mutuwa zatayi in da a kwance take zai iya cewa mutuwa tayi amma suke boye masa amma zaune take cikin wani irin yanayi wanda shi kan sa bai san a matsayar da zai ajje shi ba.


Nisawa yayi gami da juyawa ya ajje jaririn kafin ya dubi likita.


"bana tsammani zuciyata zata yarda da kai da sauran ma'aikatan ka, na lura kana boye min wani abu da yake boye, likita in kayi min haka ba ka yi mani adalci ba sam, kuma ba zan yafe maka ba".


Magana yake yi wanda da ka kalle shi zaka tabbatar ba isasshen hayyaci a gareshi.


Gyaɗa kai likita yake yi tausayin sa na kara narkar masa da zuciya cikin jan jiki ya isa gareshi ya dafa kafadar sa.


"kayi hakuri kayi abin da nace".


"bani da wannan natsuwar, ka taimaka".


Idanu ya zuba masa sosai kamar wanda ya ga bakuwar fuska, bai san mai zai ce masa, ko ma ya samu abin cewa ba tabbacin zai iya kamar sa domin yasa dole abin da yake faruwa ya fado cikin abin da zai ce dashi.


"kai nake jira likita kace min ta haihu kayan farinciki kenan amma kuma naji kana kokarin dauko min kayan da za su ruɗani cikin wannan lokaci, na lura akwai abin dake kokarin faruwa, koma nace ya faru amma ka ki ka sanar dani".


zuciyarsa ce ta fada masa da ya kawai fada masa domin ta san koman daren dadewa dole abin da ke boye ya fito fili.


Kallon Habeeba yayi wacce take takure waje daya kamar wacce ake kokarin cire mata wani abu daga jiki ta hada gwuiwa da kai sai sakin numfashi take yi kadan-kadai


"Uhmm...".


Sai kuma yayi shiru yana duban Malam Bello ya ma rasa da mai zai fara wani tunani ya fado masa zuciya lokaci guda da sauri ya dubi Nurses ya ba su Umarni cikin yanayi na amfani da ido a take suka gane abin da yake nufi da sauri suka fice daga cikin dakin.


Malam Bello ya dubi Likita izuwa lokaci. Zargi da kokwanto akan sa ya fara samun mazauni sosai a zuciyarsa.


"ina ga kawai gida zaka ku tafi da ita tunda ta haihu lafiya...sai dai in ko wata matsalar ta faru sai ka dawo da ita".


Tunda ya fara magana Malam Bello ke yi masa wani irin kallo mai dauke da TUHUMA hakan ya sanya jikin sa sanyi domin ya lura sam bai abince da batun sa ba.


Juyawa yayi da sauri ya fice daga cikin dakin ya barshi tsaye shanye da baki hannunsa ruke da ɗan jaririn da izuwa lokacin ya fara kuka mai sauti sosai.


kallon Habeeba yayi har yanzu dai tana nan yarda take isa yayi gareta yana mai zama kusa da ita.


"HABEEBA".


ya kira sunanta cikin wata irin murya mai taushi.


ba ta dago ba, balle ya saka ran zata dago idanuwanta har ta sauke su akan sa, ko motsi ba ta yi ba, illa sautin ajje numfashi da take yi.


Sake kiran sunan nata yayi a karo na biyu nan ma bata dago ba balle kuma ya sa ran zatayi magana.


Tsayin lokaci suka dauka cikin haka shikuwa jaririn sai zunduma ihu yake yi sai faman jijjigashi yake yi amma ba alamun zai daina kukan mikewa yayi tsaye yana zarya cikin dakin yana duban Habeeba gabansa na kara tsinkewa da lamarin nata musamman da ya ga duk kukan da jaririn yake yi ko motsi bata yi ba.


Nurses ne suka shigo ba tare da sunyi masa magana ba suka kama hannun Habeeba suka fice da ita yana mai bin su da kallo kamar wani sauna abubuwa da yawa sun daure masa kai ya rasa a ciki wanne ya kamata ace yayi tunani akai da ya dauko zaren tufka tunanin nasa sai ya warware haka ya cigaba da zarya domin rashin abin yi kusan mintina biyar yana cikin wannan yanayi sai ga likita ya shigo yana duban sa.


"An kammala komai ka zo ku tafi don Allah ka kula da ita sosai domin ba karfin jiki gareta ba haihuwar ta bata wahala matuka kai kan ka sheda ne don haka a kula mun yi mata duk wani bincike da ya kamata, zamu hadaka da ma'aikaciyarmu daya domin akwai abin da muke bukata ta kula dashi".


tunda ya fara magana yake gyaɗa kai cikin amincewa amma ba har zuci ba kawai rashin abin yi yayi ya bige da amsa maganar da ba yarda yayi da ita ba.


Duk halin da yake ciki Likita na lura da shi haka ya ja shi suka fice daga daki har zuwa inda motar da aka saka Habeeba tana zaune a takure kallo kawai ya bita da shi yana gyaɗa kai cikin rashin taka maimai in da zai ajje tunanin da yake yi akan ta.


gaban motar ya shiga rungume da jaririn can baya kuma Habeeba ce da Nurses zaune gefen ta sai direban da zai ja su.


Sosai da sosai likita ke tausayin su a zuciyarsa sai faman gyaɗa kai yake yi har ya ga tashin su suka bar harabar asibitin...
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I


NA


KAMALA MINNA.


BABI NA HUDU
Kamar wacce aka watso haka ta fado cikin gidan, kallo daya za kayi mata kayi tunani rainon dawanau ce gabadaya yana yin jikinta ba shi da maraba da wacce aka durbuɗe cikin jar kasa ana cakudawa har sai da aka ga ta canza launi aka sake ta.


"Ahayye Yaro Ahayye Yaro,
A ƙyawu wata tafi wata a taku koni nafi".


Waƙar da take ta faman yi kenan da tayi tafiya daya biyu za ta tsaya tana girgiza kugu gami da tafa hannu a haka har ta isa kofar daya daga cikin dakunan gidan ba sallama ta bankaɗe labule ta faɗa.


Goggo Marka dake zaune tana faman ƙadin zare zumbur tayi tana shirin arcewa don ba karamar tsoro taji ba wani irin kallo ta watsa mata bayan ta ga wacece.


"ke kam an yi 'yar wofi wallahi ai wannan sai ki tsinkar min da gaba".


turo baki tayi gama tana mai galla mata harara.


"Uhmm nikam Goggo ki daina ce mani 'yar wofi".


"ke dalla jaye ki bani waje yar banzar 'ya mara hankali".


"nikam ba 'yar banza bace".


ta fadi tana mai yatsine fuska.
Juyawa tayi zata fice daga cikin dakin da sauri Goggo Marka ta dakatar da ita ta hanyar cewa,


"haba 'yar gidana ba ma haka dake, ina kuma zaki je?".


ko sauraron ta bata yi ba ta kara azama wajan ficewa daga cikin dakin da sauri ta mike ta riko hannunsa cikin karya murya.


"haba hafsatutuna yar gidan Mati da Abulle jikanyar Goggo Marka yar gaban goshin Danliti kar kiyi fushi mana".


Da alamun kirarin da akayi mata ya yi mata dadi shagwaɓe fuska tayi.


"Nikam in har kina zagina zan bar zuwan gidan ki ke kenan kullum zagin mutum".


"yi hakuri na daina, yo ai kece da turawa mutum haushi ba ki iya abin hankali ba amma dai yi hakuri zo mu zauna in ji abin da ke faruwa".


ba musu ta koma cikin dakin ta zauna ta shiga jayo kayan kaɗin Goggo Marka tana kokarin batawa da sauri ta buge mata hannu.


"nifa tsiya ta dake kenan ba kya gani ki kyale sai kin taba".


harara ta galla mata.


"kwarankwatsi zan daina zuwa gidan ki ke abu kadan sai ki daki mutum ko ki zage shi".


Hafsatu jikan Goggo Marka ce ba ta ji sosai da sosai rashin jinta ya wuce inda kake tsammani kullum cikin kawo wa uwarta korafi ake yi duka kuwa kullum cikin shan sa take amma ba abin da yake sauya zani ba wanda bai santa ba cikin kauyen nan iyaye da yawa ba sa son suka ga 'ya'yansu da ita domin rashin jin ta da kangarewrta sau da dama in tayi laifi bata zaman gida domin tasan halin uwarta jibgarta take yi kamar Allah ne ya aiko ta shiyasa da tayi laifi sai ta kwaso jiki tayo gidan Goggi Marka wacce ita ce bata ganin laifinta ko fada ta tsokano in dai ta zo wajan ta sai dai ta balbale wanda ta tona da masifa da zagi a wajan Goggo Marka ta samu daurin gindi take tsula tsiyar ta yarda take so sai dai kuma wani abu dake faruwa tsakaninsu duk son da Goggo Marka take yi mata bai hana a dinga jin kan su ba kullum in har ta zo gidan ba ta barin sa ba suyi fada ba Goggo Marka bata da hakuri sam kamar zawo ita kuma Hafsatu ba ta ji kamar 'yar Allah bani.


Mikewa Hafsatu tayi tana kokarin ficewa daga cikin dakin da sauri ta ce da ita.


"ina kuma za ki je?".


Cikin rashin baiwa maganarta muhimmanci tace.


"aƙwai zafi yasin dakin ki sosai ba zan iya zama ba, bari na zauna waje".


ba ta tsaya jin abin da zata ce da ita ba, ta bankaɗe labulan ta fice nan kofar dakin ta samu kujera yar tsugunno ta zauna ta shiga sakin yan waƙoƙin ta na shirme a zaunan ma rawa take yi.


Mariya dake kunshe cikin daki cikin wani irin yanayi na rashin tsammani komai na rayuwa domin ta gama yankewa kanta ta rabu da uwarta kenan tunanin ta sai wansafo mata abin da yake wakana da uwarta yake yi aceqar ai ta jima da matuwa gawarta kawai za a kawo gida lokaci-lokaci hawaye da suka zama abokan zamanta a wannan lokaci sai faman zubowa suke amma ko ta kan su ba ta bi don ta tabbata ko dauke su tayi ba abin da zai ragu daga tashin hankali da take ciki saboda komai na duniyarta ya kwance mata.


juyi take yi lokaci lokaci abubuqa sai faman kara yawa suke na tunanin zuci masu tayar hankali.


kamar wacce aka tsikara haka ta mike zumbur cikin taimakon jarumtar zuci jiki kuma a sake ta miki sai faman tangaɗi take yi kamar wacce ta baje aka idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kamar wacce akayi wa surace da barkonon tsohuwa sannu a hankali ta fara jan kafar ta har zuwa kofar dakin ta dage labulan ta fito ba ta lura da Hafsatu dake zaune ba can gefe guda ta shiga kokarin yin waje motsinta ne ya sanya Hafsatu dagowa daga abin da take yi ganin Mariya ya sanyata jan jaki domin ba shiri suke yi ba sam! Jininsu bai haduba.


sarai ta ji tsakin da aka ja amma ba ta tsaya daga tafiyar da take yi ba domin tashin hankalin da take ciki ya zarce ta tsaya neman ba'asi ko da bugun ta kuwa akayi a daidai soron gidan su ta tsinkayi tsayuwar Napep cikin wani irin karfi da bata san tana dashi ba ta kwasa yi waje a guje adaidai lokacin Mai Napep din ya tsaya turus! tayi ta tsaya ba tare da ta isa wajan da suke ba idanuwanta kuriii kan na mahaifiyarta abubuwa ne suka shiga yi mata shawagi akai gani take kamar ba gaske ba gani take kamar mafarki ne yake kokarin yaudararta.


ba ta san lokacin da Malam bello ya fito ba har ya biya mai Napep kudin sa Ya dubi Nurses.


"zaki kamo ta ku fito ko sai na taimaka muku".


"barshi kawai shiga da jaririn cikin gida tukunna".


Habeeba ya kalla har yanzu tana nan yarda take ba abun abin da ya canza domin tunda suka taho maganar duniya yayi mata amma ko tari bai ji tayi ba girgiza kai yayi gami da daukar hanyar cikin gidan Mariya da tajima cikin tunani ba ta san lokacin da ya iso ba ya dafa kafaɗarta firgigit tayi tana mai baza idanuwa kamar wacce zata arce kallon mahaifinta tayi da abin da ke hannunsa kanta taji yana juyawa gani takeyi kamar ba gaske gani take yi lamarin kamar ba faruwa yayi sai da taji ya ambaci sunanta tare da girgizata sannan ta tabbatar da abin da take zargi ta shiga duban jaririn ta na kallon mahaifinta murmudhi take ajjewa wanda bata san ya akayi ta samu damar yin sa ga ruwan hawaye sai kwaranyo mata suke.


Shima murmushin yayi mata wanda shi da ka kalle nashi bai kai zuci ba iyakarsa fatar baki.


"jeki ga Umman taki can".


ba ta tsaya tanka masa ba tayi hanzarin barin wajansa ta nufi Napep in da ta hangi Nurse na kokarin fito da ita shi kuma ya fada cikin gidan.


tun kafin ta isa gabanta ya yi wani irin bugu lokaci guda taji wani irin yanayi ya ziyarce ta zuciyarta na sanar da ita an samu matsala, matsala babba.
da sauri ta isa gaban Nurse tana kallon ta cikin wani irin yanayi kamar mai son karin bayani kallon Ummanta tayi wacce ta zama tamkar rakumi da akala ba wani kuzari sam! a gareta sai yarda Nurse tayi da ita.


"NA SHIGA UKU!".


Mariya ta fadi gami da riko Ummanta kallonta sosai Nurse tai jin abin da ta fadi girigaza kai tyi cikin yanayi na tausayi a haka suka rungumi Umma sukayi cikin gida da ita wacce a wannan lokacin sam bata san a ina take ba duniya ce ko lahira haka suka isa cikin gidan a lokacin Malam Bello ya fito daga cikin dakin ya na musu nuni da dakin ta ciki suka shigar da ita


Duk abin da ake yi Hafsatu tana nan zaune shanye da baki mamaki ne ya cika ta sosai ganin an shigo da Habeeba ya sanya ta saurin mikewa ta fada dakin Goggo Marka tana kiran ta.


"Goggo zo ki ga Umman Mariya ta haihu".


dubanta ta shiga yi da mamaki don ita sam ta mance da cewa Habeeba na nakuɗa har sun ta fi asibiti cikin hanzari ta mike tana duban Hafsatu cikin murya kasa-kasa.


" wa ya ce miki ta haihu?".


"yanzu naga sun shigo Malam rike da jinjiniya sai kuma wata mata ringome da Umman Mariya...".


kuri tayi mata da idanu kamar mai son gano wani abu ita ma Hafsatun kallon ta tashiga yi cikin rashin abin yi


kwankwasa kofar da akayi ne duk ya sanya su zabura Goggo Marka ta kalli kofarta jin muryar Malam Bello wani takaici ya turnuke ta ba shiri ta saki hannun Hafsatu kamar bata san abin da ke faruwa ba ta bankaɗe labulan tana kokarin tura ashar harara ta saki gami da jan guntun tsaki juyar da kan ta tayi cikin dakin cikin kunkuni.


"gaskiya na shiha hakki wallahi, sai azo ai ta dannawa mutum sallama duk a firgita shi sai mutum yayu zaton mutuwa ce ta kawo farmaki".


kasa-kasa tayi maganar amma sarai ya ji abin da take cewa ransa kuma ya sosi da maganar sai dai ya ki nuna hakan a fuska illa girgiza kai da yayi ya shiga kokarin yin magana.


"kiyi hakuri Goggo, dama zuwa nayi na sanar dake Habeeba ta haih...".


dariyar da Hafsatu ta saki ne ya sanya shi kasa karasa maganar sa domin bai yi zaton tana cikin dakin ba sam!


ita ma Goggo Murmushi ta shiga saki, sai ka rantse na farinciki ne amma ina! ba haka bane duban sa tayi tun daga sama har kasa baki a kwaɓe.


"Ikon Allah. ashe shiyasa na ga sai faman ɓarin jiki ka ke yi kamar wanda ya ga sabuwar Amarya".


Gyaɗa kai ya shiga yi jin maganganun da take fadi ya tabbata ba har zuci ba kawai magana ce a fakaice take dankara masa.


"Uhmm shi ne dama na zo na sanar dake...".


bai dire ba, tayi saurin caɓewa.


"Gaskiya kam!".


Ta sauke guntuwar maganarta ta da dubansa tana mai sakar masa yaƙe.


Shiru yayi yana ganin ikon Allah ran sa yayi matukar ɓaci musamman da ya lura dariyar da Hafsatu ke yi ta gayya ce da raini ita kuma Goggo ta hanashi sauke maganar da ya dauko nisawa yayi cikin haushi.


"ba wani babba don Allah Goggi ki zo ki yi wani abu".


"...haka fa na manta ashe watan tashin asuba na da wankar jego ya kama Hafsatu zo muje zaman mursu".


ta fadi tana mai duban Hafsatu da take ta faman dariya


Baki ciki iyaka Malam Bello ya shaka ji yake kamar ya fada cikin dakin ya shago Hafsatu ya jibga ko ya rage jin haushi amma ba damar haka don ya tabbata in har ya dake ta yau sai kowa ya ji a gari ga abin da yayi cikin rashin abin yi ya juya ya bar kofar dakin yana mai cizon laɓɓa.


Isar sa cikin dakin ya tadda Nurse ta gyara ko ita da taimakon Mariya wacce natsuwarta rabi da kwata ba ta tare da ita tana ga Ummanta wacce take girke waje guda ba Uhmm ba uhm-uhmm.


"ya kamata ace anyi wani abu izuwa wannan lokaci".


Cikin rashin fahimta ya dubi Nurse yaka faman gyaɗa kai.


"kamar me kenan?".


ya fadi cikin raunin murya da rashin abin yi domin ya tabbata kayan bukata ake nema wanda ya tabbata ba shi da karfin yin su don ko wuka za a daura masa a makoshi baya magani kudin da za ace za ayi bukatu na azo a gani.


"ya kamata ace izuwa yanzu an yiwa jiririn nan wanka itama.uwar kanta ta gyara jikin ta sannan kuma da abubuwan da za ta sanyawa cikinta".


tun da ta dora zancenta yake faman binta da kallo yana gyaɗa kai cikin rashin abin yi ita kan ta Mariya kallon Nurse take yi domin abin da taji tana fadi to ta tabbata mahaifinta bai da wannan halin a yanzu haka ita sheda ce.


kamar wacce aka tsikara ta mike tayi tsakar gida gindin murhu ita isa ta janyo guntayen itace da karare ta hada ta

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads