Header Ads
Showing 72001 words to 75000 words out of 227252 words

Chapter 25 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

1378

Ads at the middle of Article

su sun kafa da'ira kamar ko yaushe yarda kasan ƙawaye haka suke daukar junansu sam! Goggo Marka bata rike girman ta ba ta tauna lafazi kafun ta furta a gaban Hafsi bata kunyar ta saki baki tayi ta ratata zance ko wani iri ne ya dace ko bai dace ba ita ba ruwanta.
Kasa tayi da kanta tana mai jan numfashi gabanta na cigaba da bugawa fata take yi Allah yasa har ta shige daki ba tare da sun tsinka mata ba domin ta sani in har su kayi magana to ba mai dauke da alheri bane mugun abu za su fadi akan ta ita kuwa ciwon da zuciyarta take yi a yanzu ya isheta ba sai sun dauko wani sun kara mata ba.
"Hehehehe an dai ji kunya wallahi an fita da sunan zuwa makaranta ashe halin bera akayi shiyasa ake ta ɓarin jiki a je a turmushe kudin sai gashi da yake Allah ba azzalumin bayin sa ba ne a gaban saurayi ko nace abokin sheke aya asiri ya tonu".
Sautin muryar Goggo Marka ta doki kunnuwar Mariya da mugayen kalaman da take furtawa wata irin juwa taji ana yi da ita a filin duniyar rayuwarta ji tayi komai na kwance mata komai take ji ya na fadowa kanta da kayan tashin hankali wani bugu taji zuciyarta tayi kamar zata faso kirji ta fito wani makaƙi mai ɗaci gami da ɓauri taji suna yawatawa cikin makoshinta zuwa saman harshenta.
Cak! ta tsaya waje guda tana faman jan numfashi don ji take numfashin na kokarin ficewa gabadaya daga gangar jikinta yake yi a hankali ta fara taka kafafuwanta da take ji suna lauyewa kamar roba suna kokarin watsar da ita.
"wai mu za a nuna wa son addini da tsoron Allah bayan ko an fita ba can wajan neman ilmin ake yi ba sa dai yawon ta zubar".
muryar Goggo Marka ta sake fadin haka kafun Hafsi ita ma ta caɓe.
"rungume da juna fa na tadda su cikin mota yana faman laguda ta ita kuwa sai faman yashe mssa baki take yi".
'A'uzubillahi minal shaiɗanir rajim'
Zuciyar Mariya ta shiga ambata tashin hankalin da take ciki ta ji yana daɗuwa komai taji yana juya mata kanta da gangar jikin ta sai majajjawa suke yi da ita cikin wannan yanayi ta ja jiki kanta rike a hannayenta wanda take jin sa kamar zai tarwatse saboda tsabar daukar zafi da taji yayi.
Shigar ta dakin ke da wuya ta zube tsakar dakin wani kuka ne mai ɗaci a zuciya taji ya kufce mata sai dai ba hawaye kukan zuciya ne kawai wanda ke kokarin yayyaga mata ko wani fili da zuciyarta da kirjinta HAWAYEN ZUCIYA da take jin suna zuba kamar za su kashe mata zuciya da ruhi.
Girgiza kai kawai take faman yi jin lamarin take kamar ba gaske ba jin komai take kamar a duniyar mafarkinta jin komai take yi kamar duk kuncin duniya akanta a sauke mata a duk sassan jikinta wani fili taji a zuciyarta yana kamawa da wuta ya na babbakewa lokaci guda.
Lokaci mai girma ta shafe cikin wannan yanayin kafun zuciyarta ta sarara mata dalilin ambaton sunan Allah da take faman yi cikin wani irin yanayi mai girma da tashin hankali a cikin sa sosai idanuwanta suka sauya kala kamar wacce akayi wa hayaki da barkono mai tsananin zafi.
A hankali ta dago kanta tana yawatawa da idanuwanta cikin dakin gabanta na tsananta faduwa sake ware idanu tayi ganin ba Umma a cikin dakin da sauri ta zabura ta mike tana kara buɗe idanuwanta sosai kafun ta furta
'Yaa Rabbi'.
Laɓɓanta na rawa cikin yanayi na firgata ganin Umma bata cikin dakin hakan ba karamin fadar mata da gaba yayi ba da sauri ta yo waje tana yawatawa da idanuwanta tsakar gidan ba ta ga kowa ba da sauri tayi hanyar bandakin su mai dauke da langa-langa ta shiga kwalawa Umma kira amma ina babu ita babu dalilinta hakan ya sanyata sauri karawasa cikin bandakin ba kowa a ciki da sauri ta yo waje tana duban su Hafsi so take yi ta tambaye su amma tana tsoro ta san dole sun fadi kalma mara dadi ko da kuwa za su bata amsar in da Ummanta tayi ita dai ta san Ummanta ba ma'abociya fita ba ce domin za ta iya tunawa tun da suƙa dawo daga asibiti tsayin wannan lokaci Umma ko kofar gida ba ta leka ba dole hankalin ta ya tashi tana tsoron Abin da zai je ya dawo.
Zuciyarta taji tana sanar da ita kawai ta tambayesu kar ta tsorata da abin da za su ce da ita wanda zai bata mata rai domin ko mai su kayi mata baya yake da ace bata ga Umma ba da wannan shawarar tayi amfani ta dago rinannun idanuwanta ta na saukewa akan su kafun ta shiga motsa laɓɓanta gabanta na wani iri bugu mai girma gareta.
"Uhmm...Goggo don Allah Umma ta ina ta je...?".
Muryarta da rawa a ciki duk kalmar da za ta fadi a dandatse take ajje ta.
Duban shekeke sukayi mata su duka kafun Hafsi ta saki shewa suna tafawa tare da Goggo Marka.
"mu kika ba ajjiyar ta da za ki zo kina tambayar mu ki fita mana ai gari da yawa maye baya cin kan sa itama ta fice yawon ta kamar yarda ke ma ki fic...".
"Hafsi!!!".
Mariya ta buɗe muryarta sosai ta ambaci sunan da wani irin bacin rai mai girma dubanta take cikin yanayi na gargaɗi da karki sake tafka irin wannan kuskuren sosai bacin rai ya wadatu a cikin muryarta hannu ta daga tana nuna Hafsi wacce muryar Mariya ita ce ta sanya ta tsaida da maganar take yi domin sosai taji faduwar gaba ganin yanayin da Mariya ta nuna.
"Hafsi ya kamata ki san irin maganganun da za ki dinga fadi a kan Umma ta komai za kiyi ko wani irin cin kashi zaki yi ya kamata ki sauke a kaina ba wai sai kin sako Umma ta ba".
Ta karashe da gargaɗi mai girma muryarta.
Tana gama fadin haka tayi hanyar waje cikin yanayi da zafin zuciya da raɗaɗi a kasan ruhi.
Duk kan su sakin baki sukayi suna duban juna kafun Goggo tayi kwaɓa tana girgiza kai gami da cizon yatsa.
"ji tsinanniya mai kalar muciya da zani aiko zata ci dangin uwarta bari ta dawo ita da uwar ta ta mai shegen kalan dangin tsiya da shisshigi gami da kwala kai a faranti in ban da haka uban meye hadinta da gidan kultum daga 'yarta ta haihuwa shine ta kwashi jiki zuwa barka za su zo su tadda ni sai sun ga ne shayi ruwa ne ba komai ba ".
*******
"Alkawari nayi maka Alhaji Abdulwahaab don haka ka saka zuciyarka cikin ruwan sanyi kamar kayi amarya ta mutu A DAREN FARKO".
Areefa ta karashe tana mai kai glass cup da ke zaune a tsakar hannunta mai dauke da tataccen lemon kankana da ya sha kayan hadi sai tashin kamshi yake yi da rangwamin sanyi idanuwanta take juyawa akan Alhaji Abdulwahaab dake zaune yana dubanta da wani irin yanayi mai girma kafun ya saki wani shu'umin murmushi yana gyaɗa kai bayan ya kurbi lemon da ke hannunsa.
"Ba ki da dama Areefa. Na sani za ki iya yin koma me nene don ganin cin ma burin ki dama nawa amma kuma ya kamata ki sani Dr.Erena ba saukin kamuwa yake a hannu ba ya kama ta ki san wannan karki yi saurin sakin jiki dashi domin ba karamin NAMIJIN DUNIYA bane da kike ganin sa nan ba ko wacce mace ba ne take samun abin da take so game dashi ya san hannunsa sosai da sosai don haka sai kin yi shiri sosai kafun ki aikata komai karki ga lokaci guda yana rawar jiki akan ki kiyi zaton tarkon ki ya kama miki giwa to wallahi a,a ni nasan halin sa ni zan fada miki waye Dr.Erena ni zan fada miki irin shu'umancin sa".
Murmushi a fuskarta take kallon sa dashi sosai take raina maganar ta sa a ranta har yanzu ta lura bai san wacece Areefa ba bai san salon hannnun na taba zata ba shi mamaki za ta nuna masa sabon jini da tsohon jini akwai bambanci a tsakanin su ba kadan ba za ta nuna masa zamanin Dr.Erena gaf! yake da shuɗewa ko ma tace ya shuɗe yanzu kuwa zamanin ta ne ita ce dashi dole kuma tayi amfani da damar ta sannan kuma ta nuna wa Dr.Erena har da shi Alhaji Abdulwahaab din wacece mace za ta nuna masa zamanin da Dr.Erena yayi rayuwarsa bai samu mata irinta ba a duniyar rayuwar tasa dole duk su biyun ta ba su mamaki za su san wacece Areefa.
"Ban san da me zan sanar da kai wacece ni ba amma dai zan barka da lokaci shine zai mana Alkalanci a tsakanin ni da kai kawai kai dai ka zuba ido kayi kallon wannan GAME din da za a buga".
Ta karashe tana kara sakin wani shu'umin murmushi wanda daka kalle shi zaka san akwai tarko mai girma da aka ɗana cikin sa kafun a sake shi.
Gyaɗa kai yake yi yana yawatawa idanuwansa a nata ba tare da fargaban komai ba sosai da sosai ya hango tsantsar rashin tsoro ko SHAKKA cikin idanuwanta sosai da sosai ya hango gaskiyar kalaman da suke fitowa daga bakinta amma duk da hakan bai gasgata ba domin shi ya san Dr.Erena kuma ya san wanene shi a cikin wannan harkar dole Areefa tayi taka tsantsan domin wannan wasan da take ganin shan ruwa ya fishi wahala to tabbas zai iya juyewa a ko wacce dakika ba tare da ta fargaba ya zame mata katon aiki mafi girma da wahala a filin rayuwarta.
"Ba wai ina raina yanayin ki ba ne a,a ko daya ina dai so na sanar dake wanene Dr.Erena...".
"Ya isa haka!".
Areefa tayi saurin tare shi cikin kakkausar muryar kafun ta mike kan kafafunta ta fara taku a hankali tana mai gyaɗa kan ta juyowa tayi a hankali ta dube shi bayan ta tsaya cak! da takun da take yi.
"Me yasa zakayi mani haka mai yasa ba zaka barni na karanci wanene Dr.Erena AKARAN KAINA ba mai yasa kake son ka cusawa zuciyata shakka ko wani fargaba akan sa bana zaton wannan zuzutawa da kambawa da kake yi masa zai samu muhalli a zuciya ta ba na tunanin yarda zuciyarka ke shakka a kan sa nima ta wa za tayi haka zuciya ta da taka suna da bambanci sosai da sosai don haka ka kula".
Ajje Cup din da ke hannun ta tayi kan table din dake gaban su ta sanya hannu ta dauki jakar ta da mukullin motarta bayan ta watsa masa wani kallo na gargaɗi ta fara taka kafafuwanta domin fita daga cikin Office din ranta a jagule domin kuwa sosai taji raini a maganar Alhaji Abdulwahaab sosai ta hango ya raina ta ya raina yanayin ta amma ba komi zata ba shi mamaki wanda zai jima yana taba masa zuciya da ruhi.
"Areefa!".
Ya fadi yana mikewa kan kafafuwansa a hankali ya fara takawa domin isa wajanta tsaye take rike da Handle din kofar tana faman jujjuyashi.
"Ban san mai yasa kika fiye daukar zafi akan abin da bai taka kara ya karya ba, Ban san wacce irin zuciya gareshi ki wacce take saurin daukar abu da girma ko da kuwa bai kai a dauke shi din ba".
A hankali ta juyo tana sauke idanuwanta cikin nashi kafun taja numfashi tana gyara zaman glass din da ta daura a fuskarta a wannan lokaci mai taken 'No respect' wanda yayi matukar karawa fuskar ta ta kwarjini da kyau sosai.
"A rayuwa na tsani a raina kwazo na ko ya ya ne shiyasa nake so mutum ya rike duk wasu kalaman sa akai na har ya ga in da zan tsaya da kwazon nawa sai ya bashi Mark daidai dashi".
Yanayin da take ajje kalamanta da dakewa a ciki ya sanya shi kara gasgata ta akan kwazon nata da take kambawa amma kuma ba wai fadi a baki ba a,a gani a aika ce shine sahihin aiki inji kare yace 'mu gani a kasa' ana biki a gidan su.
Shirun da taji yayi ne ba tare da ya ce komai ba ya sanya ta nisawa domin har yanzu ta lura akwai kokwanto a zuciyarsa murmushi tayi kafun ta juya tana murɗa Handle din tana fadin.
"Uhmmm...kar fa ka saka zuciyarka cikin tunanin lamari na kawai ajje shi gefe ka yi kallo kawai kamar yarda na fadi maka a baya".
Tana gama fadin haka ta sake sakar masa murmushi tana ficewa daga Office din da hanzari.
Sosai yake murmushi shima yana kallon yanayin Areefa da yanayin da take kokarin ya yarda da maganarta zai iya yarda sai sai wani sashi na zuciyarsa yana tuno masa da Dr.Erena yana hango wanene shi a duniyar filin rayuwarsa da irin gamzuwa da yake yi da mutane yana zubda su sosai yake samun nasara kafun a samu kan sa wanda ya tabbatar wannan a jinin sa yake.
Juyawa yayi ya koma tsakar Office din yana safah da marwa hannayensa harɗe a bayan sa.
*****
April 2000.
Sosai garin ya haɗe da wani irin haɗari mai matukar razanar wa wanda a ko wani lokaci zai iya zubda ruwa mai karfi gaske gami da iska.
Dr.Erena tsaye bakin kofar dakin wani hotel dake tsakanin Abuja da Suleja kallo daya zaka yi masa ka tabbatar da akwai abin da ke damun sa a ransa sosai da sosai bi sa yanayin da fuskarsa ta nuna na tsananin bacin rai.
"Mr. Ekele na lura har yanzu ba ka san wanene ni ba a fadin duniyar nan har kake tunanin yaudarata ka hada baki da wasu wajan cuta ta".
Wani murmushi ya ajje a fuskarsa yana kai hannunsa zuwa haɓarsa dake cike da suma kamar wanda yayi shekara ashirin bai bi ta kan ta ba.
Mr.Ekele da ke tsaye sai faman rarraba idanuwansa yake yi a tsakanin na Dr.Erena ya shiga sharce gumin da ke tsatsafo masa a ko ina na kofar gashin dake jikin sa na fuskarsa yake saukewa duk da iskar ake yi a wannan lokacin bakin sa na rawa cikin gurbatacciyar hausar sa ya shiga magana.
"aleji ke yi hakuri don Allah hakan ba zai sake faruwa ba na rantse miki".
Wani wawan kallo Dr.Erena ya watsa masa kafun ya dungule hannu kamar zai sakar masa naushi a fuska hakan da Mr.Ekele ya gani ya sanya shi ja da baya yana kiran.
'Jesus'.
Bakin sa na ɓari jikin sa sai karkarwa yake yi kamar wanda aka jonawa wayar wuta.
"Get out now!".
Muryar Dr.Erena ta karaɗe wajan da amo mai zurfi da bacin rai a cikinsa.
wata irin zabura yayi har yana kokarin haduwa da bango da sauri ya juya duk da hakan bai hanashi haɗe hannayensa waje daya yana bashi hakuri ba cikin tsananin tashin hankali.
Fitar Mr. Ekele ke da wuya Dr.Erena ya juya cikin dakin sa da sauri fuskarsa kunshe da bakin ciki da bacin rai mai tsanani ga kuma wani murmushi da ya dauko yake ajje a fuskar tashi gefen gadon ya zauna yana mai janyo na'urar sadarwa ta waccan zamanin talfon a hankali ya ja abin sanya wa a kunne ya na mai kai dayan hannun nasa zuwa madannan jikin talfon din dakikun kadan a ka daga cikin yanayi na umarni da nuna isa akan wanda ake waya dashi ya fara magana.
"Yanzu nan nake so ku isa titin da zai shigar da ku Abuja Mr.Ekele nan akan hanya ina so cikin mintina goma ya bar filin duniyar nan bana so ko gawarsa a gani balle a shaida shi da cewa ya bar duniyar nan".
Yana gama fadin haka kamar da minti daya ya sauke wayar yana faman sakin wani murmushi mai razanar da wanda ya gani kafun ya saki wata mahaukaciyar dariya yana mai bajewa gabadaya kan gadon.
Gudu yake yi cikin motarsa zuciyarsa sai faman tsalle-tsalle take da tashin hankali mai girma a wannan lokacin kuma a ka saki wani ruwa mai karfi da iska ga tsawa da ake ta kwaɗawa gabadaya Mr.Ekele ya gama tafiya cikin duniyar tashin hankali jikin sa faman karkawa yake yi ga wani gumi dake karyo masa duk da feshin ruwan da dake shigowa ta cikin glass din motar da bai rufe duka ba.
Zuciyarta ba abin da take zaryar dauko masa sai a rangamar su da Dr.Erena ya sani sosai zai shiga cikin matsala tun da har ya san da hannunsa cikin wannan yaudarar da aka shirya yi masa duk da dai shi akaran kan sa ba a son ran sa wannan lamarin ya afku ba takura masa akayi ba yarda ya iya ga shi yanzu ya shiga hali wanda Allah kadai ne zai iya fiddo shi daga hannun wannan mutumin mara imani da tausayin a zuciyarsa ya sani sai wani ikon Allah zai bar shi ya cigaba da rayuwa a duniyar nan ya sani koma ya cigaba da rayuwa to lokaci kalilan ne zai yi ko da kuwa be bar duniyar ba to tabbas zai shiga halin ƙaƙani kayi...
Wani iri bugu yaji an yiwa bayan motarsa wanda sanadiyyar haka sai da ta tuntsiya ta shiga katantanwa a tsakiyar titi ga ruwa da ake ta mamakawa dakiku masu yawa ta dauka tana katantanwa kafun ta tsaya waje guda bayan ta dawo daidai gabadaya glass din jikin motar su yi kwatsa-kwatsa ita kanta motar duk ta gama molewa Mr.Ekele da ya gama rikicewa gabadaya kansa da fuskarsa jini ne sosai gabansa sai bugawa yake yi da sauri sauri a hankali ya fara kokarin tayar da motar don ya gama tabbatar wa kansa ba wanda zai yi masa wannan aikin sai Dr.Erena tuni ya tabbatar wa kan sa ba zai bar shi da numfashi a doron duniyar nan ba key ya shiga juya a mazauninsa cikin iko na Allah motar ta dau wuta ganin ta tashi yayi mata birki gami da fizgarta kamar daga sama yana yin gaba yaji ya doku da katon abu wanda ya sanya motar sake wuntsulawa baya can bayar ma karo ya sake yi da wani abu mai girman gaske kafun motar tayi sama ta dawo kasa lokaci guda.
Izuwa wannan lokaci ya gama fita daga hayyacin sa ba abin da yake ambata sai 'jesus' ya ce ce shi daga wannan halin da yake ciki na tashin hankali.
A hankali yaji a na

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads