Showing 135001 words to 138000 words out of 227252 words
Chapter 46 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt
bata zuwa masa domin kuwa ba komai bane bawa ke nema ya samu Dr.Aqeel...".
Runtse idanu tayi jin yarda zuciyarta ke zafi da raɗaɗi a duniyar nan in akwai abin da ta tsana shine ayi mata gori tana jin zafin hakan sosai a ranta shiyasa ta kullacin hakan a ranta cewa duk yarda zatayi rufawa kanta asiri zata yi domin ta lura a duniyar nan ba abin da yafi bakinciki da takaici shine ka nema wajan wani ya dizga ka ko kuma yayi maka bayan idonka ya zo yana zaginka ko yana goranta maka a duniyar nan ba abin da yafi kwanciyar hankali da gujewa wulakanci kamar DOGARO DA KAI.
"Mariya don Allah kiyi hakuri wallahi tallahi ba haka nake nufi".
"Don Allah Dr.Aqeel ka rabu dani in har ba so kake yi zuciya ta buga ba ka barni haka ka sani ban ga laifin ka ba don ka fadi haka maganar so kuma Dr.Aqeel ka sani ina son ka amma halayenka ne na tsana ba zan boye maka ba a yau na kara gasgata abin da zuciyata ta ɗade tana sanar dani bana tsammanin inuwa daya da kake kwadayin mi zauna a tare zai yuwu".
Ta karashe tana mai kaucewa tana wucewa da sauri ya shiga kokarin shan gabanta wani kallo tayi masa hakan ya sanyashi tsayawa cak! Yana dubanta har ta karasa cikin sauri-sauri gudu-gudu.
Zubewa ne kawai Dr.Aqeel bai yi ba a kasa domin zuciyarsa yake ji tana wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zata faso kirji ta fito duniyar yaji tana juya masa bai san abin da ya kai shi yin wannan maganar ba bai san mai ya kai shi ba gashi yanzu bakin sa ya yanka masa wuya yankan da bai san ko zai warke ko ba zai warke ba yanayin da ya ga Mariya a ciki ba karamar kiɗima yayi ba a hankali ya fara taka kafafuwansa hannunsa rungume da kansa har isa wajan motarsa ya shiga kafun ya dago ya dubi Motar da tun dazu take tsaye ba tare da mai ita ya fito ba sosai yaji zuciyarsa tana azalzalarsa da ya tsaya ya ga kowa waye amma a halin da yake jin kansa a yanzu ba zai iya ba yana bukatar ya gansa a gida yana bukatar ya kebe kan sa waje daya domin yin tunani da samo mafita da za ta haifa masa da ɗa mai ido.
A hankali yayi wa motar key kafun yayi ribas ya fizge ta da gudu ya bar unguwar zuciyarsa a jagule.
Dr.Karami da zuciya ta kwasoshi tun dazu yana dannewa duk abin da ya wakana yana kallo ya dade yana zargin Dr.Aqeel akwai wani abu a tsakaninsa da Mariya bai gasgata ba sai yau da idanuwansa suka gane masa zuciyarsa yaji tana zafi da wani irin turiri sitiyarin motar ya buga tare da buɗe murfin motar ya fito sai faman huci yake yi kamar wani kumurci fuskarsa har ta canza launi saboda tsananin bacin rai ya shiga kai wa iska naushi kafin ya ja kakafuwansa zuwa cikin gidan da Sallama ya shiga ba kowa tsakar gida sai muryar Mu'azzam dake tashi cikin kuka sake sallamar yayi a lokacin Umma ta ansashi kafin ta bashi izini ya iso daga kofar dakin ya tsaya suka gaisa da Umma abin da bai saba yi ba yau yayi shi kansa sai da yaji wani bambara kwai wai namiji da suna Hajara ita kanta Umma sai da tayi mamaki amma ba ta nuna masa ba.
"Mariya na ciki Umma ce ina son ganinta".
Ya fadi murya a sake amma a zuciyarsa shi kadai ya san abin da yake ji
Mariya dake dunkule waje guda tun dazu dama take jiran tsammani da sauri ta mike ta zauna tana rarraba idanu alamun rashin gaskiya sosai Umma ta shiga dubanta tana karantar yanayinta kafin ta wurga mata harara lokaci guda.
"Tashi ki fice mani daga daki sakayya".
Rau-rau tayi da idanu kamar zatayi kuka don yarda Umma tayi maganar ya tabbatar zargin da take yi yiwa Dr.Karami laifi tayi shi shi haifar da komai.
"Tashi nace tun kafin na kwaɗe ki wallahi".
Zabura tayi tana mike tana tura baki gaba har sai da ta ga Umma ta mike sannan tayi saurin ficewa daga cikin dakin bata same shi a tsakar gida ba hakan ya tabbatar mata yana waje a hankali ta fara takawa gabanta na faduwa a har ta isa cikin soron gida tana kokarin ficewa daga cikin sa sam bata lura da mutumin da ta wuce ba sai ji tayi ya kira sunanta a firgice ta waigo tana kokarin kwasa da gudu ya sha gabanta saura kadan ta fada jikinsa runtse idanu tayi jikinta ya shiga rawa sosai ta firgita da yanayin sa a hankali taji yayi gyarar murya.
"Buɗe idanunki".
Ya fadi ba yabo ba fallasa jin abin da yace ya sanyata buɗe idonta daya tana kallonsa harararta yayi da sauri ta mai da ta rufe kafin ta bude su gabadaya a firgice.
"Ke kina tunanin wannan halin da kikeyi shine mafita a gareki ko a yarda kike a matsayinki na 'ya mace kina tunanin abin da kike yi mutuncin kine na lura Mariya gabadaya kin canza halayenki ba yarda na san ki a da ba wai har kece kullum baki wajan wannan saurayi ba ki wajan waccan kuna rigima a matsayinki na 'ya mace anya kuwa bana tunanin wacce ta san mutuncin kanta da darajar ta zata kasance a haka".
Wata katangar tashin hankali taji ta rikito mata lokaci guda kanta ya shiga sarawa lokaci guda idanuwanta suka kawo kwalla ta shiga dubansa shikuwa nuna wa yayi ko a jikinsa amma can kasar zuciyarsa ji yake yi kamar ana hura masa wuta.
"Duk mace mai daraja ba za ta taba kasancewa a haka ba Mariya kin bani mamaki kin canza mani ban yi tsammanin haka kika koma ba...ba ma wannan ba tun yaushe nake garin nan amma daidai da rana daya kin ki bani lokacin ki amma kin iya baiwa wanda zaku tsaya layi kuna rigima da su saboda ni bani da wata daraja a idanunki ban cancani ki tsaya dani ba shikenan na gode amma ki sani in har kikace haka za ki cigaba da rayuwa da samari kina da katon aiki a gabanki".
Yana gama fadin haka ya fice daga cikin soron zuciyarsa na suya sosai yaji ba dadi a ransa da maganar da ya gaya mata amma haka kawai yake ji a zuciyar tasa ita kadai hanyarsa ta samu sauki duk da dai bai san ya zata dauki lamarin ba.
Idanuwanta da suke zubda hawaye ta kure kofar da su tana jin wani tashin hankali mai girma yana wanzuwa gareta a hankali taji kafafuwanta na kokarin kasa daukarta zubewa tayi kan gwuiwowinta lokaci guda ta na sakin wani kuka mai ciwo da taba zuciya...
*_KAMALA MINNA_**😘😘😘
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA TALATIN DA TAKWAS.
Ihu sukeyi gabadaya sun karaɗe wajan sai cukuikuye junansu sukeyi a waje daya cikin matsanancin tashin hankali kallo daya zakayi musu ka tabbatar suna cikin tsaka mai wuya gabadaya sun jeme sun yi baki kayan jikin su gabadaya sun gama fita hayyacin su wasun suma ko kallabi babu akan su.
Janta yake yi yana faman dukanta da bakin bindiga itakuwa sai turjewa take yi tana janyon yan'uwanta suma sunan janta kallo daya zakayi mata ka gane tana cikin galabaitaccen yanayi idanuwanta gabadaya sun gama rufewa kawai fizgar ta yake yi har zuwa lokacin da ya fidda ita daga cikin wajan sai numfarfashi take yi can ciki tsakiyar rana yaja ta ya watsar da ita ga ranar ta kwala sosai kamar zata darkar da mutum.
A hankali ta shiga kokarin buɗe idanuwanta jin zafin ranar na dukanta ta ko ina gashi ba wata wadatacciyar suttura bace a jikinta wando ne dogo sai riga ita ma doguwa iyakar gwuiwa da guntun hannu amma yanayin da kayan su ka koma sai ka ka rantsee yagaggune daga bola aka tsinto su kanta kuwa ba kallabi wasu hawaye suka zuba daga cikin rufaffun idanuwanta kafin ta tashi zaune tana faman cizon laɓɓanta.
Wani irin murɗawa taji mararta tayi lokaci guda kamar yan hanjinta da mararta za su zazzage wata kara ta saki mai razanarwa kafin ta kai hannayentala duk biyun cikin galabaitaccen yanayi tana dafe wajan zubewa tayi gabadaya a kasa tashiga murkususu da shure-shure kamar kazar daka yanka take kokarin mutuwa cikin lokacin kankani ta fice daga hayyacinta ko motsi bata yi kafin can kuma jini ya balle ya shiga kwararowa ta kasanta mai dauke da gudaje-gudaje numfashi take ja jin komai na duniyar take kamar ba nata ba duniyar take ji tana canza mata da tashin hankali mai tsananin gaske zafin da take ji tun daga cikinta har zuwa mararta ya tabbatar mata da lokacin mutuwarta yayi sosai taji dumin da ke bin kafafuwanta hakan ya kara tsinkar mata da zuciya.
Tsaye yake kanta yana kallon duk abin da ke faruwa amma ko motsi bai yi ba sai faman murmushi yake yi kafin ya juya ya dubi gabadayan alkaryar tasu sannan ya juya ya dubi sauran yan'uwan nata da ke kargame ko wacce da sakar a hannayenta da wuyanta sai faman zubda kwalla suke yi suna gunjin kuka hannu suke miko mata amma ina bata san ma a ina take ba lokacin da suka lura da abin da ke faruwa da ita ba su san lokacin da suka kara sautin kukansu ba cikin matsanancin yanayi.
Bindigar da take hannunsa ya daga ya saita in da suke ji kake daram! ya sake nan take albushiri yayi fitar burgu ya sauka cikin wajan a saitin goshin daya daga cikin yan matan wani razanan nan ihu ta saki lokacin da kanta ya tarwatse kwanya ta watse duk ta bata yan uwanta kafin gangar jikinta ya zube kasa warwas.
Ganin abin da yake faruwa ya ka sanya su cikin matsanancin rikici lokaci guda duk su rikice suka shiga kai kawo cikin wajan ko wacce hannunta akanta suna faman kankame junansu.
Ihun da yake tashi ne a wajan yana ansa kuwwa ko ta isa ya sanya shi dago tambol din sa ya fito fuskarsa a murtuke kam! ya tsaya a tsaye yana faman bin filin wajan da kallo kafun ya sauke wajan yan matan da yake hangowa sun faman rusar ihu wata razananniya tsawa ya doka lokaci guda sautin tsawar ya karaɗe wajan ƙafin ya shiga takawa cikin matsanancin zafin rai idanuwansa da wani irin yanayi na tsananin rashin imani da tausayi idanuwansa na kan su sam bai lura da abin da yake gabansa ba sai da yaji yaci karo da mutum sannan ya tsaya yana duban wajan shame ya ganta ko alamun rai babu a jikinta da sauri ya daga kansa yana duban sa.
"Ita kuma wannan fa?".
Ya tambaya cikin yanayi na halin ko in kula kafun ya sake dubanta iya zuwa lokacin tana fidda numfashi a hankali hankali.
"Shiga nayi na bukace ta shine ta saka min hakora a jiki".
Ya fadi yana mai nannaɗe hannun rigarsa wani wawan cizo ne ya bayyana har fatar wajan ta dauke sosai.
Ji kake kau ya dauke shi da mari kafi ya tsartar masa da yawu cikin tsananin dacin rai.
"Mai ya hanaka rabata da filin duniyar nan tun da har zata yi maka taurin kai har haka".
Yana gama fadin haka ya zaro wata karamar bindiga fisto ya saita ta lokaci guda ya sakar mata albushiri a kai shurawa daya tayi daga shi bata sake yin wani ba.
"Wa ya fada maka ana jayayya da su ai duk wacce ta tsaya tsaiko a tsakanin ku kawai dauki ranta don ba su da wani amfani a gare mu".
Ya fadi yana mai tsartawa gawan dake yashe tana zubda jini daga kanta yawu kafun ya juya cikin takun isa yana mai juya bindigar dake hannunsa har ya isa garesu tun da suka ga ya tunkara garesu suka shiga haɗewa waje daya suna cakume junansu numfashin su na fita da sauri-sauri cikin matsanancin faduwar gaba da tsoro mai tsanani jikin kofar ragar da aka rufe su da ita ya tsaya yana mai yawatawa da idanuwansa akan su kafin ya saki wata mahaukaciyar dariya mai matukar razana su ya shiga sakin albushirin bindiga wajan na ansa sautin fitar albushirun hakan ya kara firgitar da su kafin lokaci daya ya daka musu tsawa da ta sanya su yin shiru wasun su har da sakin fitsari.
A hankali ya shiga kaucewa daga wajan yana faman cilla bindigar sama yana caɓewa har ya isa ga tambol din sa can nesa ya hangota tana ta faman kyalaye amai kamar zata amayar da kayan cikinta gabadaya ta gama galabaita numfashi kawai take saki cikin tsananin zafi da raɗaɗi gabadaya jikinta take ji ya canza komai nata jin sa take yi kamar ba nata ba a hankali ta shiga kokarin tashi amma jirin da taji yana dibarta ya sanyata komawa tayi zaman daɓaro idanuwanta sai faman shatatar da hawaye sukeyi gabadaya ta gama figewa ta rame kamar ba ita ba idanuwa duk sun zurma ga wani mahaukacin duhu da tayi kamar wacce ta shekara ba ta ga ruwa ba.
A hankali ya tako ya iso gareta yana bin ta da kallo kafin ya dan ranƙwafa sosai ya tallabo haɓarta a dan razane ta dago kai ganin waye ya sanya ta buge hannunsa tana mai jan jikinta can nesa dashi zuciyarta na kara cushewa waje daya ta wani tarin bakinciki da takaici mai yawan gaske kallonsa take yi kallo na tsana da kiyayya fuskarta a murtuke sai faman huci take yi ji take kamar ta cafko shi ta shake shi ya mutu ko ta huta da wannan bakar izaya da ukuba da take ciki a filin duniyar nan bata san yarda zata kira wannan lamarin ba bai ta san mai zata ce da wannan al'amarin ba bata san ya zata kwatanta rayuwar kaskanci da take cika ba ta rashin yancin da mutunta kallon kanta take yi a wata banza wacce bata da saura galihu tun da ta fado filin duniyar azzalumin mara imani wanda ba abin da ya saka gaba sai daukar rai da bai ji bai gani ba.
Murɗawar da cikinta yayi ne ya sanyata dafewa tana runtse idanu hadi da tura laɓɓanta duka cikin baki tana cizawa wata irin azaba ce taji tana kartar mata ciki da bayanta ji take yi kamar zata mutu don azaba da take ji hawaye suka shiga zuba wanda bata san ma suna zuba din ba kawai dumi take ji a sama kuncinta har zuwa kirjinta buɗe idanunta tayi ganin mutum tsaye akanta ya sanyata saurin matsawa tana watsa masa wani matsiyanci kallo mai cike da tsana da kiyayya mai girman gaske kafun ta shiga motsawa laɓɓanta suka shiga motsi hawaye sai faman ambali suke yi.
"Ka sani wannan dariyar da kake yi akwai ranar da za ta zame maka kukan jini, karka yi tunanin wannan rashin imanin da kake nunawa ba ranar da zai zo karshe, karka yi tunanin cin zarafi da keta haddi da kake yi ba zai zo karshe ba, ka sani duniyar ma gabadaya sai ka barta kamar yarda kake zama SILAR AJALI ga wasu to ka tabbata yarda ko wani dan aike yake zuwa ya dawo to ka tabbata kai ma dan aiken ka yana nan dawowa kuma duk abin da kake aiken sa yayo kai ma sai ya zo ya yi akan ka".
Numfashi taja tana jin yarda zuciyarta ke zafi da raɗaɗi da tashin hankali mai girman gaske.
"Ka kashe mani iyaye na ka rabani da gari na ka keta min haddi ka zaja min UKU BALA'I bala'in da bai taba rabuwa dani ba ka ja zamanin bala'in da ba zai taba canzawa ya koma alheri da yake kamar da ba amma ka sani shi sharri dan aike ne wallahi".
Mikewa ta shiga kokarin amma har lokacin jiri take ji wani fizga taji yayi mata ya watsar da ita kasa ya taka mata ruwan ciki da kafarsa mai dauke da wani kafcecen takalmi wani irin nishi ta saki hawaye suka zubo mata idanuwanta a runtse.
"Ina so ace na mutu amma abu daya zan roki Allah ya banni nayi rayuwa har zuwa lokacin da zan ga karshen ka zan fi kowa farin ciki da murna a filin duniyar nan mutane da yawa na san za suyi farinciki duk da dai baya in ta tafi bata taba dawowa amma ina so ace mutane da ka saka wa ciwon rai ka saka su a BALA'I zan so ace sun ga karshenka Malik".
Buɗe idanu tayi tana jin yarda zuciyarta take kara kekeshewa da rashin tsoronsa yinkurawa tayi zata tashi tana mai ture kafarsa daga ruwan cikin ta.
Duban gawarwakin da ake kokarin dauka guda biyu na yan'uwanta tayi kafun ta dube shi fuskarta da murmushi mai ciwo.
" 'Ya'ya Mata kayi wa haka ka sani komin daren dadewa wallahi sai hakkin su ya hanaka sukuni ba ganin ka na shiga rigar mutanan adalci kana nuna kai na Allah ne kana yaudarar mutane ta wannan hayar Uhmm...".
Taja numfashi kafin ta girgiza kai.
"Lokaci ne ba wanda yake hanyar sabawa Allah ya samu nasara komin lokacin kuwa da ya dauka yana cin nasara to akwai RANA DAYA tak! da zata zo ta rushe duk wannan nasarorin da yake zaton ya samu".
Sosai ya har zuƙa jikinsa har rawa yake yi wani wawan cafka ya kai wa wuyanta nan ta shiga kakari idanuwanta sukayo waje sun kaɗa sunyi jajir wani huci ya shiga fetar wa kamar zai ci babu kafin yayi cilli da ita can gefe guda ta hadu da wani katon dutse ta gaban goshinta lokaci guda gun ya tsage ya shiga zubda jini sosai ta ji zafin wajan amma ba ta nuna hakan ba tashi tayi ta sanya hannunta ta na dauke jinin a hankali a ko ina na sashin jikin ta azaba take ji amma jarumar zuciyarta ta kiyin rauni.
"Kisan kai da kakeyi ka dauka kuma aikin yi a filin duniyarka na rantse da Allah wata rana kai ma zaka mutu mutuwa kuwa ta wulakanci sai ka raina kan ka BAR GANIN ALLURA wallahi karfe ce bar ganin abin da kake yi kamar abun burgewa ne wallahi kai ma sai wannan hanyar ta zama silar barinka duniyar nan".
Kallonta yake yi da wani irin yanayi na mamaki tun da yake bai