Header Ads
Showing 198001 words to 201000 words out of 227252 words

Chapter 67 - Uku Bala'i Complete Romantic Book By kamala Minna.txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

1431

Ads at the middle of Article

saka a nata.
"ki daina kiran amincin dake tsakani na dake kina danganta shi da wannan lamarin ni nace miki ki bari nayi tunani ba yarda za ayi na ansa wannan batun lokaci daya Mariya ba sauki fa lamarin nan gareshi ba duba zakiyi da shi Dr.Aqeel ba shi yace yana so na ba ke yake so kina tunanin in ya ji batun nan zai yarda har ya dube ni da kima da mutunci ya anshe ni amatsayin da kike kokarin daura ni?".
Murmushi ita ma tayi zuciyarta na kara matsewa.
"Alkawari nayi miki zai so ki so da bai taba yi wa wata 'ya mace...".
"Ya isa haka Mariya maganar ta isa haka ki daina danganta KALMAR SO a wannan bahagon tunanin naki mara tushe kece mace ta farko kuma ta karshe da Dr.Aqeel yayi wa son da ba zai sake yi ma wata mace ba a duniyar...".
"Na karya taki Baseera a wannan matakin ni nace miki in har kika aminci da Dr.Aqeel sai yayi miki so fiye da wanda yayi mani a filin duniyar nan ki rubuta wannan ki ajje ni dai BURINA ki amince".
Kanta ta dafe da take jin yana sara mata maganganun Mariya suna kokarin saka mata ciwon kai bata san yarda za tayi da ita ba amma Allah na gani zuciyarta na fargaba kan lamarin nan.
"ki je ki samu yardarsa in har ya amince nima na amince".
Tana gama fadin haka da sauri ta kwace kanta ta fice daga cikin dakin zuciyarta da kwanyarta sai hayaki suke yi kamar za su kama da wuta duniyar take ji tana juya mata kafafuwanta take ji suna kokarin zubda ita ga wani zafi da take ji tun daga kasan ruhinta har zuciyarta komai kallon sa take yi kamar a mafarki ba gaske ba laɓɓanta take turawa cikin baki tana cizawa gami da runtse idanuwa.
Dafe kanta Mariya tayi gami da jan kafafuwanta da take jin su ita ma suna kokarin zubda ita kasa ga wani hayaniya da take ji a kwanyarta zuciyarta take ji tana harbawa da sauri-sauri idanuwanta a runtse ta isa bakin gadon ta zauna tana faman fadin.
"Yaa Hayyu Yaa Kayyum".
Numfashi take fiddawa a hankali zuciyarta na kara mikata wani mataki abin da tayi ne a yanzu take jin wani banbarakwai ji take yi kamar ba gaske ba ji take yi kamar cikin barcinta ne komai ke faruwa girgiza kai ta shiga yi kafun ta buɗe idanuwanta wanda suka gajiya da kaɗawa sosai zuwa ja murmushi ta saki gami da rufe fuskarta da tafukan hannayenta ta fada kan gadon ta baya.
Tunanin ta yarda zata fuskanci Dr.Aqeel take yi ba ta san ta yarda zai dauki maganar ba in ta je masa da ita bata san duban da zai yi mata ba akan wannan maganar anya ba zai ce ta yaudare shi ba anya ba zai ce ta ci amanarsa ba anya ba zai ce tayi masa BUTULCI ba?
Tunanin da take ta faman yi kenan zuciyarta kuma ta kasu kashi biyu bangare daya na bata kwarin gwuiwar tunkararsa dayan barin kuma yana tsoratar da ita yanayin da za su kwashe da Dr.Aqeel sosai ta ji ko ina na jikinta yana sanya kwanyarta na kara rikicewa da rigimar da zuciyarta ke hango mata za su kwasa da Dr.Aqeel a maganar nan ya kamata tayi wani tunani dole ne ta nemo hanyar da da zata samawar kanta mafita sannan ta samu cikar fatanta da burinta.
*******
Kai kawo kawai take yi tsakiyar dakin gabadaya ta hargitse yarda ka san wacce ta kwato kanta daga gidan mahaukata hannayenta saman kai sai yamutsa sumar kan ta take yi lokaci-lokaci take tsayawa tana jan numfashi tun da ta dawo gida ta rasa gane kanta maganganun Mariya ne kawai ke yi mata safa da marwa gabadaya take jin kwanyarta na kamawa da wuta ga zuciyarta na ta faman kokarin fallewa da gudu daga kirjinta tashin hankalinta na daɗuwa ji take yi gabadaya duniyar na sauya mata ji take yi kamar ba ita ba.
Saitin katon Mirrow da ke dakin ta isa ta tsaya tana kallon kanta ta cikinsa l fuskarta take shafawa tana runtse idanu gani take yi kamar ba ita ba gani take yi kamar wata Baseerar aka ajje aka dauke ta ainihin.
'Ta ya ya za ta so Dr.Aqeel bayan sun taba soyayya da ƙawarta aminiyarta ta kut-da-kut anya kuwa zata iya zuciyarta take ji kamar ba zata amince ba ji take yi kamar zaman kishi za su yi da Mariya ji take yi kamar in ta amince Mariya zata dauke a maciyar amana a gareta'.
Zuciyarta ce take ta faman dauko mata wannan maganganun suna kara rikita mata lissafi kofar dakin da taji an taba ne ya sanyata saurin juyawa Yah Tareeq ne ya shigo ganin yanayin da take ya sanya shi saurin isowa gareta yana yi mata kallon tuhuma.
"Me ke damun ki Sister?".
Ya fadi yana kokarin riko hannunta da sauri ta ja da baya dafe da kai ta zauna bakin gado tana mai da numfashi harɗe hannaye yayi a kirjinsa yana dubanta cikin wani irin yanayi kafun ya isa kusa da ita ya zauna kan loka din kusa da gadon.
"Tambayarki nake me ke damun ki kin yi mani shiru".
"Yah Tareeq bana jin dadi ne don Allah ka yi shiru bana son surutu".
Da mamaki ya dube ta ganin yanayin da take ciki ya tabbatar masa da gaskiyar abin da tace mikewa yayi yana kokarin fita har ya kai bakin kofa sai kuma ya tsaya gami da juyowa ya dube ta ita ma shi take duba dawowa yayi da baya hakan ya sanyata runtse idanu so take yi ya fita so take yi ta zauna ita kadai zaman kadaici take so kwanyarta take so ta sauke daga hayakin da take yi tana bukatar zaman ita kadai domin samun mafita akan wannan Bahagon lamarin da yake kokarin rikita mata lissafin rayuwa.
Kusa da ita ya zo ya zauna bata ce dashi komai ba har zuwa lokacin idanuwanta a rufe suke tana faman jan numfashi da sauri-sauri.
"Sister wai shin ya maganar nan ta mu ne har yanzu ba ki ce dani komai ba lokaci tafiya yake yi?".
Duban sa tayi ta gefe idanuwanta a zazzare ji take yi kamar ta kwala ihu don haushin abin da yake cewa da ita so yake yi ya sake rikita mata lissafi bayan tashin hankalin da take ciki laɓɓanta ta tura cikin baki ta ciza da karfi har sai da ta dan saki kara ta dube shi sosai sai fama gyaɗa kai take yi.
"Yah Tareeq ka san me nake so da kai?".
Girgiza yayi cikin mutuwa jiki ganin yarda tayi masa maganar.
"Ka taimawa kan ka ka taimaka min ka bar maganar nan don ba zata taba yuwu ba ne Yah Tareeq kayi hakuri ka je ka nemi wata matar amma ba Mariya ba don a halin da ake yanzu bana tunanin za ta iya dubanka har ta anshi tayin ka in har ba so kake yi abubuwa su lalace ba".
Zaro idanu yayi waje sosai gami da mikewa cikin hanzari ya shiga kokarin magana amma Baseera ta dakatar dashi bayan ta mike idanuwanta sun kara kaɗawa sun yi jajir.
"Don Allah na roke ka Yah Tareeq wallahi tallahi abi nan ba zai taba yuwuwa ba kawai bata lokacin mu za muyi sannan kuma kayi dakon son da ba zai yi maka amfani ba sai ma matsala da zai ja maka kawai kayi hakuri ka nemi wata ZABIN ALLAH shine kawai mafita".
Tana gama fadin haka ta koma ragwaf! ta zauna dafe kansa yayi da yaji yana juya masa kamar zai zubda shi ya shiga ambaton Allah a hankali ya fara jin saukin zafin zuciyarsa kallon Baseera yayi yanayin da yake ganinta a ciki ya tabbatar masa da abin da take gaya masa da sauri yaja jiki yana hada hanya ya fice daga cikin dakin dagowa tayi ta dube shi bayan taji alamun ficewarsa ta girgiza kai ta koma ta kwanta....




*KAMALA MINNA*😘😘😘😘
[10/22, 5:24 PM] DEENY MINNA🙋‍♂:   UKU BALA'I


NA.


KAMALA MINNA.

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*




​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.




BABI NA SITTIN DA BIYU
Gabanta take ji yana faduwa sosai da sosai ga wani irin yanayi da take jin gangar jikinta na shiga runtse idanu tayi a daidai lokacin da Umma ta shigo cikin dakin dauke da bokitin Cake da ta gama yi can gefe ta ajje shi sannan ta juyo ta dubi Mariya da tayi shiru kamar wacce ake yiwa wasiyya girgiza kai tayi kafun ta motsa laɓɓanta.
"Kin ga Cake din nan na yau ya bani mamaki kamar ba yarda ake yi ba wallahi yayi albarka sosai".
Ta fadi tana mai zaunawa gefe gudu har zuwa lokacin idanuwan Mariya na buɗe sai faman ajiyar numfashi take yi hannu ta kai saman kirjinta ta dafa gami da buɗe idanuwan nata tana duban Umma.
Murmushin yak'e ta sakar mata kafun ta mike ta iso gareta jikinta a sanyaye.
"Umma jikina nake ji wani iri wallahi ga kirjina sai bugawa yake yi kamar wani abu zai faru dani tun safe nake jin haka".
Dubanta Umma tayi idanuwanta na yawatawa akanta so take yi ta hango wani abu da zai bata ko tabbacin abin da yake damun Mariyar.
"Addu'a kawai zaki tayi Mariya irin haka in yana samun bawa musamman faduwa gaba Innalillahi wa inna ilaihir raji'un ake so ya ta maimaitawa".
Gyaɗa kai tayi tana juyar da ganinta zuwa ga bokitin Cake din sannan ta juyo ta dubi Umma.
"Yayi auki fa a hakan ma na gani...ko da yake Birin gidanmu ba ya nan shiyasa Cake din bai shiga uku ba".
Mariya ta fadi tana murmushi ita ma Umma murmushi tayi don ta gano da Mu'azzam take....
Da gudu ya fado cikin dakin yana hak'i ya fada jikin Umma dukkan su suka dube shi da mamaki dago fuskarsa yayi ya dubi Umma sannan ya dubi Mariya.
"Ga wasu mutane nan a kofar gida su hudu har da masu kayan fulani".
Gaban Mariya ne ya yanke ya fadi kamar yarda yake yi mata tun dazu da sauri ta dubi Umma dafe da kirji yanayin ta ya sauya lokaci guda.
Ita kanta Umma ta ji faduwar gaban sosai don sai da taji cikinta yayi kara zuciyarta na tsalle kamar zata fito waje.
"Wai cewa yayi na zo na sanar daku nan gidan su ka zo daya daga cikin mutanan yace mani haka kuma yana kama da Yah Mariy....".
Wata irin zabura Mariya tayi ta mike kan kafafuwanta idanuwanta a warwaje bugun zuciyarta take ji yana sauyawa sosai haka kawai take ji a jikinta akwai abin da ke faruwa.
Umma kuwa rintse idanu tayi tana ambaton sunayen Allah da dukkan wata addu'a da ta zo mata baki haka kawai ta ji a jikinta akwai kamshin wani abu muhimmi a batun Mu'azzam.
"Yace fa ku zo yanzu Umma".
Ya fadi ya na mai jan hannun Mariya bayan ya tashi daga jikin Umma a hankali Mariya ta shiga bin sa kamar rakumi da ak'ala tana kallon Umma ita kanta Umma rasa abin yi tayi domin gabadaya take jin wata gajiya da kasala ta dirar mata a jiki lokaci guda ga wani bugu da zuciyarta take ta faman yi ba ƙanƙautawa laɓɓanta tashiga motsawa ta na son yi wa Mariya magana amma kamar an dora mata katon dutse a harshe hannunta tayi mata nuni dashi ta dauki mayafi .
Duban jikinta tayi ita sam ta manta ma da kayan dake jikinta a hankali ta kwace kanta daga hannun Mu'azzam ta ja kafafuwanta da take jin su kamar za su zubda ita kasa ta janyo hijabin Umma ta zira ajikinta fita tayi cikin kokarin saita kanta Mu'azzam na gaba tana biye dashi har suka isa soron gidan nan ta ci burki ta tsaya jin yarda zuciyarta take dokawa da sauri-sauri jingina tayi da bango tana mai da numfashi Mu'azzam shi kam idanu ya zuba mata har ta gama shan sharafinta ta taka a hankali suka cigaba da tafiya har suka isa kofar gida sai dai me.
Abin da Mariya ta gani ne ya kusan kashe ta da ranta runtse idanuwanta tayi sosai tana mai daura hannu aka ta kurma ihu gabadaya ta sulale zuwa kasa da sauri suka yo kanta ba wanda ya tabata ganin Babbar mace ce duban Mu'azzam sukayi gabadayan su kafun Baffa yace
"Me ya same ta?".
"Mu'azzam da yayi firi-firi da idanu cikin yanayi na tsorata.
"Yah Mariya".
Ya fadi ai Bello na jin haka ya sake dubanta sosai zuciyarsa da kwamyarsa suka mika shi wani mataki mai tsayin gaske da ya gama shuɗewa sosai yaji wani irin abu ya dokar masa zuciya mai girman gaske.
'Mariya'.
Ya furta hakan a ransa yana sake muntsuka idanunsa yana saukewa akanta juyawa yayi da sauri ya fizgo gorar ruwan dake rataye a jikin Ja'e ya balle kanta ya shiga kwarara mata kamar yarda hawaye lokaci guda suka shiga zubo masa a fuska wani dogon numfashi ta ja gami da buɗe idanunta ganin mutanan dake kanta ya sanyata saurin runtse ido tana furta.
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un".
Da karfi komai ganin sa take yi kamar ba gaske ba sosai zuciyarta ta tsorata ta sosai take jin jikinta wani iri gani take yi kamar a mafarki ba gaske ba laɓɓanta ta tura cikin bakinta tana cizawa zafin da yake ratsa ta ne ya tabbatar mata da GASKIYAR LAMARI da sauri ta sake ware idanunta.
Fuskar dake saitin ta take kallo fuskar da take hango hawaye suna zuba a samanta fuskar da ta jima tana cigiya fuskar da ta bace mata a rayuwa tsayin shekaru wai ita ce yau take gani kunnuwanta ta rufe da tafukan hanayenta gami da sake runtse idanu zuciyarta na harbawa da wani irin yanayi wanda ba za ta ce ga matsayin da zata ajje shi ba.
"Mariya".
Muryar da ta shuɗe sama da shekaru bakwai ita ce yau take jinta a saitin ta tana ambatar sunanta muryar da tayi kewarta muryar da kullum take yabonta da shi mata albarka yau ita ce ta dawo gareta bayan shuɗewar lokaci.
Wani irin kuka ne taji ya zo mata da saurin ta rufe bakinta amma ina sai da sautin sa ya fita da sauri ta shiga kokarin mikewa amma ina ta kasa gaɓɓanta take ji kamar an doke mata su kamar daga sama taji hannaye da tajima da saninsu sun riko mata kafaɗu cikin wani irin yanayi suna mikar da ita kan kafafuwanta wani numfashi take ja mai tafe da kuka buɗe idanuwanta tayi sa'ilin da taji ana dauke mata hawayen fuska sosai take kallon sa da wani irin yanayi na mamaki da tu'ajibi gani take yi kamar bashi ba gani take yi kamar gizo yake yi mata hannayenta ta shiga dagawa tana kokarin kai fuskarsa amma ta kasa da sauri ta shiga ja da baya tana duban sauran fuskokin wanda bata shaida su ba amma a jikinta take jin wani irin yanayi game da su.
Da gudu tayi cikin gida kamar wacce za a sace a soro suka ci karo da Umma da Mu'azzam a hargitse domin tun lokacin da ya ga ta fadi din nan ya kwasa yayi cikin gida yana kiran Umma.
Kallon ta Umma take yi da wani irin yanayi gabanta take ji yana yankewa yana faduwa hawayen da ta gani a fuskar Mariya ya kara rikita mata lissafi da sauri ta riko hannunta jikinta sai faman ɓari yake yi bakinta na karkarwa.
"Su waye Mariya...tambayarki nake yi su waye?".
Yanayin da take maganar kawai ya isa ya tabbatar maka da cewa sosai take cikin firgici Mariya da ta ga yanayin da Umma ke ciki ya sanyata sake rushewa da kuka kafun ta tsagaita da cewa.
"Umma Allah yasa ba mafarki nake yi ba gaskiya ne Abbana ne...".
Da sauri ta sake ta tana ja da baya gabanta na kara tsananta bugawa kafafuwanta take ji suna lauyewa idanuwanta suna lullubewa lokaci guda taji duniyar na juya mata kwanyarta na ansa kuwwa sosai jingina tayi da bango tana maida numfashi kafun ta zabura kamar wacce aka tsikara tayi hanyan waje da sauri a daidai lokacin shikuma ya sanyo kai cikin gida cikin rashin tsammani suka bangaji juna taga-taga Umma tayi zata fadi dama ba wani karfin jiki take dashi ba da sauri ya rikota gabadaya jikinsu ya dauki wani irin yanayi runtse idanu Umma tayi sosai tana jin yarda jikinta ke ansawa da wasu bakin lamari masu girman gaske gareta.
A hankali ta shiga kokarin buɗe idanuwanta tana saukewa gareshi bakinta dauke da addu'a don gani take yi kamar a mafarki ba gaske ba jikinta na rawa ta dago hannunta tana shafe fuskarsa lokaci guda wasu hawaye suka shiga kwaranyo mata a fuska zuciyarta na kara matsewa kwanyarta take ji kamar za ta kama da wuta a hankali ta zare jikinta daga na shi tana ja da baya kallonsa take yi a yanzu cikin tuhuma shi kansa ya hango hakan da sauri ya dube ta amma ita juyawa tayi tana kokarin komawa cikin gida.
"Tare da su Baffa nake".
Da saurin Maganganun nasa suka bugar mata zuciya da kwanya lokaci guda jinin jikinta da numfashinta sukayi tsayawar wucin gadi ji tayi kamar ba a duniya take ba kunnuwanta sai faman maimaita maganar da Bello yayi suke wani GWAURON NUMFASHI taja da take jin kamar zai fasa mata kirji tsoro ne sosai ya bayyana a gareta maganar take ji kamar ba gaske ba so take yi ta gasgata zuciyarta take jin tana ansawa tana amanna da batun juyawa tayi cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa ta dube shi wani kuka mai girma taji yana zuwa mata zuciyarta na buɗe wani wawaken ciwo da ta jima tana jinyarsa.
A hankali ya isa gareta yana riko hannayenta gami da girgiza kai idanuwanta sai faman bin shi da kallo suke komai take ji kamar almara gani take yi ko a cikin barcinta hakan ba zai faru ba amma zuciyarta sai kara karfafa mata guiwa take yi a kan ta yarda.
Mariya da Mu'azzam suka iso garesu kallon kallo suka shiga yi a

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads