Header Ads
Showing 1 words to 3000 words out of 159513 words

Chapter 1 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1205

Ads at the middle of Article

 *Y'AR GARUWA........*
_{ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ ơʄ ąmąʑıŋɠ wąɬɛr ۷ɛŋɖơr women}._

*STORY,WRITTEN & EDITING*
*BY*
_HAWWA M.U {®ɛąl $mąʂɧɛr}._


*COPIED BY.*
_HAWWA M.U (REAL $MASHER)._

 💠💠💠💠💠







*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹












*©®2018*


*8/mąrcɧ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_


🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹








_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._










*Da ѕυnayen υвangιjιnмυ tsarkaka naĸe ғara rυвυтa wnn laвarι, wanda ѕнι ya вanι daмa,laғιya,тare da вaιwar da a ĸυllυм nake godiya gareshi....*


*Aminci,tsira su k'ara tabbata ga fiyayyen halitta,Annabi Muhammad (S.A.W) tare da ahalinsa da sahabbansa da wad'anda suka biyosu da kyautatawa har i zuwa ranar sakamako....*


*~___________________________~*






*wannan laвarι ĸ'ιĸ'ιrarѕa nayι,ѕaι daι yana d'auke da darussan rayuwa iri²,ina fata Allah ya bani ikon kammalawa lafiya....*


*ban yarda a juyamin labariba ta kowace fuska,wanda yayi haka na barshi da Allah...*


*Idan kunga kuskure aciki ina fata za kumin uzuri,Allah ya yafe mana baki d'aya, wanda yaga wani abu da yayi dai² da rayuwarsa yamin uzuri badon cin fuska nayi ba....*


*Allah yasa mu dace.... Ameen thumma ameen...*


*~___________________________~*




_YA ALLAH INA ROK'ONKA DA SUNAYENKA TSARKAKA KA BAWA MAHAIFANMU LAFIYA,INGANTACCIYA MAI 'DOREWA,KAJI K'ANSU,KAYI MUSU RAHAMA......._






_WANNAN LITTAFI NA SADAUKAR DASHI GA MAHAIFANMU,NA GIDA DANA ASUBITI......._

*_•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°_*








*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_


*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*0⃣1⃣*
















*S*allama take tayi tun daga k'ofar gidan,amma ko tari ba ayiba,ga rana dake dukan kanta...


Banda maik'o babu abunda take,jin ank'i ansawa,yasa ta d'aga allonta dake hannunta ta d'ora akanta,don kare ranar da ta addabeta...


Zuwa can ta sake maimaita yin sallamar,nanma dai shiru aka mata babu amsa....


Hakan ne yasata tsugunawa,ta cire silifanta ta zauna akai kamar mai d'aukan darasi.....






Tun daga nesa dattijon dake tahowa,yake kallonta,sauri ya K'arawa k'afarsa dan tabbatar da zatonsa....


Daf da ita ya k'araso,tare da fad'in *"NANA KHADIJATU*, Uwata me kikeyi a cikin wannan ranar da kowa yake gudunta???"


'Dagowa tayi da saurinta jin muryan mahaifinta dake tsaye,da murnarta ta kalli mahaifin nata tana fad'in "Abba na dawo ina sallama,ba a amsaba shi yasa na zauna anan ban saniba ko ba kowa a gida"....


Banda abunki kuma uwata sai kizo cikin wannan ranar ki zauna kamar an miki dole...


"Tashi maza mu shiga ciki,kar kuma ki sake zuwa ki zauna kinji ko,wannan ai sai wani ciwon ya kamaki"...
Fad'in abban *KHADIJATUL KHUBRA*.....


Hannunta ya kama suka kama hanyar shiga gidan....




Tun daga bakin k'ofar gidan yayi sallama,jin shiru ba a amsaba,yasa abban yaci gaba da kutsa kai cikin gidan had'e da sake yin wata sallamar....


Abunda ya matuk'ar bawa abba mamaki bai wuce ganin da mutum a tsakar gidanba.....


K'arasawa yayi yana k'are mata kallo,kafin ya iya furta ‘’ladiyo dama kina zaune muke sallama,amma amsawa ta gagareki‘’.....




Fuska ta yatsina (tamkar kayan miyan da yaso lalacewa).....


kafin ta bashi amsa da cewa ‘’ina ji sai me??
ko kuwa cewa akayi an ajiyeni ne dan na amsa muku sallama?''......




Ganin zata kunyata shi gaban y'arsa yasa yabar maganar ta hanyar fad'in ''Allah ya kyauta''......


Bud'ar bakin ladiyo sai cewa tayi ''ya kyauta abinda yafi haka''.....


Bai kuma tanka mataba,ya juya yana girgiza kai,ya shige d'akinsa.....






Duk wannan budurin da ake a gaban KUBRA ake,kanta na k'asa sai hawaye dake tsiyayowa daga ciki......


Ganin abbanta ya bar gurin itama ta juya da niyyar barin gurin....


Sai dai muryar ladiyo ta rigata k'arasawa bakin k'ofar d'akin,ta hanyar mako mata mula²n zagi......


Da sauri ta k'arasa shigewa,gabanta na dukan 9²....


Can ku'ryar D'akin ta nemi guri ta zauna,tana jiran gawon shanu....




Cikin d'akin da baida wadataccen haske,take zaune,tayi shiru sai kalle² take tamkar wata bak'uwa,ko wacce ta fara rayuwa inda bata saniba,haka taketa fama ita kad'ai,a haka bacci yayi awon gaba da ita.......






Wani k'ayataccen guri ta hango mai kyan gaske....

Sauri take ta k'arasa gurin,amma duk da haka ta kasa k'arasawa gurin,saima gajiya da tayi......
Haka ne yasata neman guri ta zauna,tana k'arewa gurin kallo ko zata hango inda ruwa yake.....




Rashin ganin alamar ruwa yasata,juyawa ta kalli hanyar da ta biyo.....
hanyace mik'ak'kiya wacce ko farkonta bata ganiba,bare k'arshenta,hakan yasata kifa kanta ta fara rera kukan rashin Madafa....




Tun daga nesa ta fara jiyo hayaniyar mutane had'e da wani daddad'an k'amshi da yasata saurin d'ago kai,tana bin hanyar da hancinta.....


Ayarine na mutane da suke da mayuk'ar yawa suke shirin giftawa ta kusa da ita......


Da sauri ta mik'e tabisu duk da suna kan abun hawa,hakan bai hanata shiga gabansuba,tana fad'in
"Dan Allah ku taimakamin"....


Babu wanda ya saurareta,sai zagayeta da sukayi suka ci gaba da tafiya......


Da gudu² ta sake shiga gabansu,tana rok'onsu.....
Wannan karon kam saboda haushi da ta bawa wasu daga cikinsu yasa su yi mata tsawa....


A firgice,jikinta har rawa yake saboda tsoro take kallonsu,wani k'ato da yayiwo kanta d'auke da bulala yasata fara kuka....


tana bashi hak'uri,d'aga bulalar ya d'aga da niyyar sauke mata a jikinta......


Kafin ya k'arasa ida nufinsa,wata siririyar murya daga bayansa take fad'in kada ka kuskura ka aikata abunda kake k'ok'arin yi .....


Da hanzarinsa ya juya don ganin mai magana,sai dai ganin fuskar wanda yayi maganar yasa shi kaucewa daga kusa da ita,jikinsa na kad'awa tamkar Mazari.......


Kyakykyawan matashi ne ya bayyana daga inda ya kauce,yana sanye cikin fararen tufafi,tafiyarsa cike da k'asaita,har ya k'araso Inda suke.....




Kallon k'aton yayi kafin ya bud'e baki,har ya rigashi cikin ladabi da girmamawa yake fad'in ''tuba nake ranka ya dad'e''......


Hannu ya d'aga masa,ba tare da ya sake yunk'urin yin maganaba,ya juya da nufin barin gurin............






*~_KEEP MOVING 😍😍😍……………_~*









*_REAL SMASHER 🤞🏻😘.._*
💠💠💠💠💠



*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹












*©®2018*


*9/mąrcɧ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_


🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹








_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._






*__________________________*


_Godiya gareki *FATEEY TAMBARIY* tabbas y'an *TIME WRITER'S* muna godiya marar adadi gareki,Allah ya kara baseera,hazaka da kuma daukaka..._
_Ki jima kiyi karko tawan,Allah ya bar zumunci da kauna..._






*__________________________*












*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*0⃣2⃣*












*C*ikin sauri tabi bayansa,tana k`ok`arin tsayar da shi,sai dai hak`anta bai cimma ruwaba…....


Duk da bawai sauri yakeba,haka take binsa tana fad`in *"BAWAN ALLAH* ka tsaya"......
Ganin ta kasa cimmasa,kuma baiyi kokarin tsayawaba,yasa taci gaba da binsa....
Sai dai kamar wanda yake tafiya a cikin iska,haka ta kasa riskarsa,tsayawa tayi,lokacin ne ta hangoshi har ya dad`a mata nisa sosai..…


Zama tayi cike da takaici,gashi ko sunansa bata saniba,a matsayinsa na wanda ya ceci rayuwarta..…


Murmushi ta saki lokacin data tuna cewar zasu sake had'uwa koba wannan lokacinba....…






***************




*LADIYO* dake zaune tsakar gida,wadda tun wucewar *KHUBRA*,take rafka mata kira...…
Jin shiru babu amsa yasata mikewa tayi hanyar d'akin,da niyyar dubawa taga uban me take da har zata kirata tak'i amsawa...…


Shigarta d'akin ta tarar da ida kwance kan dagargazajjiyar tabarmarta,da take kwana kai..……


Ganinta tana bacci ba k'aramin b'acin rai tajiba,Kai ta girgiza,kafin ta koma da baya,tana fad'in da ni kike zancen yarinya...…


K'aton randan k'asa ta d'auka,ta nufi d'akin dashi,bata jira komaiba,ta juyeshi akan *KHUBRA* dake tsaka da dreaming....…





****************


A razane ta mik'e tana duba jikinta da yayi sharkaf da ruwa ga shi duk d'akin ya jik'e ruwan har ya kwanta,a tsakar d'akin...…


'Dagowa tayi ta kalli *LADIYO* dake tsaye tana watsa mata wani mugun kallo...…


Sake juyawa tayi ta kalli d'akin duk wani kaya dake ciki a jik'e yake,saboda ruwan ba kad'an bane...…


Kayanta ta fara tattarawa da niyyar gyarawa...…


*LADIYO* dake tsaye,tana raba ido akanta,ta fizgota tare da wanke mata fuska da mari...…


Gigicewa *KHUBRA* tayi,ta rasa me zatayi,shin kuka za tayi ko kuwa me????

Rashin madafa yasata neman hanyar ficewa daga d'akin...…


Ashar en da *LADIYO* tayi ne ya dakatar da ita,juyowa tayi,cikin ladabi tana fadin
"Kiyi hakuri baba ladiyo,zan gyara gurin ne"…………




''Dan ubanki ni kike fad'awa zaki gyara guri,to billahillaziy baki isaba'' fad'in LADIYO kenan kafin ta d'ora da cewa......


''Maza tun kafin na sab'a miki,ki wuce ki d'ebo ruwa,kin san aiki na nan yana jiranki,kika shigo d'aki kika kwanta ke ga sarauniya koh?''......


Rab'awa tayi ta kusa da ita ta fice,ba tare da ta sake cewa komaiba,sanin irin aikin dake gabanta.....


Tulunta ta d'auka ta kama hanyan rafi,jikinta duk babu dad'i ga kayanta dake jik'e.......
Tafiya take duk kunya ya isheta,saboda surar jikinta dake bayyane ta jikin kayan,duk da bawai banyan ne yake da mutaneba,sai dan kasancewarta mace mai tsanin kunya......


Tana tafe tana tunanin abunda ya faru yanzun,kafin fitowarta daga gida.....


A wani b'arin kuma na zuciyarta tana tunanin mafarkinta,Wanda shi ne kusan zata iya sashi a matsayin silar faruwar komai.......


A haka ta kammala d'iban ruwa,ta sake duk'ufa kan aikin cikin gida,duk da kasancewarta ba mai yawan shekaruba,amma yau da gobe yasata gogewa a fannin aikin gida......


Wuni guda tana aiki,tamkar jaka har kusan almuru ta kai,kafin ta kammala aikin.......


Sai a lokacin ne ta samu kwanciyar hankali,bayan ta je ta watsa ruwa,alwala ta d'auro ta shige d'akinta,da tun fitarta bata sake samun damar komawa cikinsaba sai ynzn.......




***************




Ta jima a tsaye tana kallon yadda k'asar gurin ta tsotse ruwan.....


Haka ta lallab'a ta rab'a gefe ta kabbara sallah...
Kafin wucewar wasu sa'o'i har ta idar....
Kwanciya tayi a gurin duk ta takure guri d'aya......

Sai a lokacin tunanin mafarkinta ya sake dawowa,murmushi tayi,tare da fatan sake ganin fuskarsa ko da a mafarkin ne,duk da dama bata tsammanin ganinsa a zahiri......






*************




Haka rayuwar *KHUBRA* taci gaba da kasancewa,kullum safiyar Allah za taje makarantar allo,daga zarar ta dawo kuma zata fad'a harkar aikace² har goshin maghreb.....



Bata da wajen zuwa,kullum tana gida (kamar daddawa).......


Rayuwarta ita kad'ai,babu k'awaye,bare ta samu abokin shawara......


Babban damuwarta baya wuce rashin zuwa dangin mahaifiyarta,Wanda tun kafin ta girma,shima bawai zata iya tunawa bane.....


Siraran hawayen da suka sakko mata ta goge,tare da tausayawa rayuwarta,irin k'angin da take ciki............

















*_~KEEP MOVING..... 😍😍😍~_*
















*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠



*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹












*©®2018*


*10/mąrcɧ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_


🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹








_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._






*~__________________________~*






_Ina matuk'ar godiya da addu'anki gareni,ina kuma jinjina gareki bisa k'ok'arinki Allah ya k'ara basira Doughteeyy *AISHA ISAH (MUMMY'S FRIEND)*......._


*~_#DUK WUYA MUNA TARE DA IZININ UBANGIJI.....~_*




*~__________________________~*










*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*0⃣3⃣*












*D*a sanyin safiyar wata laraba,tana tafe a hanya,tunanin mutumin da ta gani a mafarkinta ya sake dawo mata,ji tayi duk duniya babu abunda take da muradin gani sama da shi......


Wanda rabonta da shi tsawon sati guda kenan......




Sauri ta shiga yi na ganin ta k'arasa gida,burinta bai wuce tayi aikin da ta saba ta k'are ta kwanta ko zatayi dace a yau tayi katarin ganinsaba....




Da haka ta k'arasa,sai dai me zata tarar,zuwanta gidan ta tarar da LADIYO da wata k'anwarta da tazo daga garin KANO suna zaune cikin rumfa banda shewa babu abunda suke,duk sun cika gidan da hayaniya.... .


Tayi sallama yafi a k'irga,amma cikinsu babu Wanda yayi yunk'urin amsawa..
Haka ta wuce ta ajiye allonta.....


Dawowa tayi har k'asa ta durk'usa ta gaida ASMA'U wacce akema lak'ani da MA'U........


Yatsina fuska tayi,kafin ta kalleta had'e da zabga mata wata uwar harara........
Tsakine ya biyo baya,cikin tsawa take fad'in
''ke ni dallah b'acemin anan gurin,kinibabbiya kawai''.....


Cikin sanyin jiki KHUBRA ta mik'e ta bar gurin,ranta duk a b'ace,haka ta Shiva aiki babu ji babu gani......



*°°°°°°°°°°°°°°°*




LADIYO ce ta buga wani uban tsaki,da yasa k'anwarta MA'U kallonta,tana fad'in ''YAYA ince dai lafiya''.......


''Inafa lafiya,wannan shegiyar yarinya tana gidan nan ina naga kwanciyar hankali'',cewar LADIYO..........


Nan MA'U ta samu dama,ta fara magana da cewa
''YAYA aradu nu kaina na tsani tarinyar nan,da nazoma banyi tsammanin tana nanba,amma yanzun ga wata shawara.......
Me zai hana ki bani ita mu tafi birni,a samamata aikatau,duk wata abunda aka biya sai ina aiko miki da shi,kinga kin huta zaman banzan nan,ke ba sana'aba,ko kuwa ya kikace?''
Ta k'are maganar tata da son jin amsar da za a bata.......


Tunanin maganar MA'U ta shiga yi,zuwa can kuma ta ce
''To amma banda abinki MA'U ta ina zaki tafi da ita ba tare da ubanta ya saniba,ni da bani na haifetaba,dama anamin gorin ko kwai na kasa ajiyewa,kuma na tabbatar ba yarda zaiyiba''......


''Haba YAYA ke kam kamar ba mace ba ko da yaushe aka kawo magana bakya saurin amincewa sai kin kawo suka,shi kenan kinga ai sai kiyi ta zama babu sana'a'' ta fad'a tana had'e fuska,da alama bata hi dad'in maganar da y'ar uwar tata ba........


A'a MA'U baki fahimci me nake nufiba,dolefa sai malam BUBA yasan inda zata,kodama ace an tafi da ita babu saninsa saiya tambaya,kuma yana ganin bani na haifetaba ta ina zai amince da abunda zan fad'a.......

''Shi kenan na gane,amma dai kisan yadda za kiyi ki had'a mata kayanta,a kaita aikatau kema kya samu kifi k'arfin wani abun''.......
Yanzun an daina saka y'ay'a a gaba ana kallonsu,barema ke da babu d'a bare jika........
Ki lallab'ashi akan ni zaki bawa aronta,mijina ne baya nan zata tayani zama,zuwa nan da wani d'an lokaci zata dawo.........
Kinga daga nan sai dai yaji kid'a a magwan.......
Nan suka sa shewa,har da tafawa.......




Wunin ranar haka MA'U ta zauna tanata yiwa LADIYO hud'uba,wanda k'arshe sai da ta amince,akan ko Malam en baya so sai ta aikata........





*°°°°°°°°°°°°°°°*




Kwanakin MA'U uku a k'auyen na KASHIN DILA,tayi niyyar komawa inda ta fito.......
Kayan da KHUBRA ta fito da shi ne ya tabbatarmin da sunyi nasara akan k'udurinsu......


Fuskanta cike da damuwa,haka sukayi sallama,har bakin k'ofar gida LADIYO ta rakosu,tana yiwa y'ar uwarta fatan sauka lafiya......


Nan suka kama hanyan barin garin,mashin d'in achab'a suka hau,daga nan bai saukesu ko inaba sai tashar garin na HAD'EJIA........
Misalin k'arfe d'aya na rana motarsu ta harba kan titi.......


*~#SAFE TRIP KHUBRA...~*






Tafiya

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads