Showing 66001 words to 69000 words out of 159513 words
Chapter 23 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt
nufi ko?"
"Ehhh!HAJIYA za a kiyaye"
"Toh shi kenan sai na jiku,Allah ya kiyaye hanya"
Daga haka sukayi hanging kiran,kowa ya shiga duniyar tunani....
《《》》
Yau tun safe da ta tashi take jin jikinta na mata ciwo,wanda ta rasa dalilin faruwar hakan..
A haka ta lallab'a ta shirya,ko abinci bata ciba take shirin fita...
Kuran ta shiga kiciniya zata fita da ita BABA ZUWAIRA ta dakatar da ita
"Haba KHUBRA yanzu haka kika zab'i zama?"
Tsayawa tayi tare da juyowa tanama BABA ZUWAIRA kallon rashin fahimtar tambayanta,kafin ta bud'e baki tana shirin magana BABA ZUWAIRA ta rigata..
"Yanzu fisabilillahi ace ki tashi ba tare da kinci komaiba kuma ki hau shirin fita...
To waima idan kin tafi baki ci komaiba zaki iya aiwatar da abunda kika fita dominsa?"
Shiru tayi ta ci gaba da tsaiwa a gurin,sai dai wannan lokacin kanta na k'asa ta kasa magana...
Jikinta ne ya sake yin sanyj jin furucin BABA ZUWAIRA,inda nan take ta tafi tunanin rayuwarta ta baya..
"Lokacin da take neman abinci ido rufe ta sanya a cikinta,a lokacin da take daf da mutuwa,amma ta rasa mai taimaka mata,yau gashi a rayuwarta taci karo da inda ake mata fad'a idan zata fita ba tare da taci abinciba"...
Wasu siraran hawaye ta juya ta goge,sannan ta k'irk'iro murmushi lokackin da ta baro gurin da take
"Eyyah!BABA yau tun da na tashi ne bana jin dad'i shi yasa banyi tunanin cin komaiba"
Sai da BABA ZUWAIRA ta wurga mata harara kafin tayi magana
"Dama haka za kice,abu da ko zuba abincin kikayi ba wani cin na kirki kike ba,kina cin abinci kamar ana bawa kyanwa"
"Haba BABATA ina cifa da yawa"
Harara ta dad'a wurga mata
"Ke tafi can kya dai fad'awa wanda bai saniba,amma ba dai ni ba"
Dariya sosai KHUBRA tasa,ta jima tana dariyan wanda har tasa BABA ZUWAIRA tsayawa da abunda take tana kallon ikon Allah......
《《》》
"Dan Allah BB ka tsaya ka ji"...
ZUHRA ce mai yin wannan maganar lokacin da ta kusa taradda shi,k'in tsayawa yayi ita kuma ta ci gaba da bagging ensa kuma ba tare da ta saurara da binsaba...
Daga bayanta ta tsinkayo maganar KHALEEL
"K'yale shi kawai ZUHRA kada Allah yasa ya tsaya"
'Dan juyawa tayi kamar za tayi kuka
"Dan Allah YAH KHALEEL kace ya tsaya....please"
"K'yaleshi dan kansa zai dawo kinji"
Kanta ta d'aga alaman ta ji,sannan suka jera suna tafiya kowa da inda zuciyarsa ta karkata...
Dai² d'akin da aka kwantar da MAMA suka k'araso anan suka tarar da BB zaune ya dafe kansa da hannayensa duka biyu yayi shiru...
Tunaninsa bai wuce ta yaya zasu samo wanda zai kula da MAMA ba a zaman da za tayi a asibitin...
Yayi zurfi cikin tunani KHALEEL ya zauna kusa da shi yana kallosa,phone ya d'auko cikin contact nasa ya shiga bincike,nan ya lalubo number D.P.O,har ya gama magana da shi BB bai saniba...
Magana ya shiga yi masa amma sam bai san yana yiba har sai da ya girgiza shi,sannan ya kalle shi da rinannun idanuwansa da b'acin rai ya gama rine su
"MAN yanzufa ba lokacin tunani bane mafita ya kamata mu nema...
Waye ya kamata mu samu da zata zauna da MAMA?"
Shiru BB yayi ya kasa magana zuwa wani lokaci cike da jimami ya fara magana
"Irin abunda nayita fad'awa MAMA kenan lokacin da nake tambayarta danginmu...
Yanzun ga irinta nan,waye zai zauna da ita a wannan halin?duk dad'in k'awaye bai kai d'an uwaba,amma MAMA tayi watsi da danginta da dangin mahaifinmu"
Kallonsa kawai KHALEEL yake cike da rashin fahimta
"Kamar yayafa dude?"
Murmushi yayi mai ciwo kafin cikin jimami,takaici,haushi ya fara magana
"Tun bayan dawowarmu garin nan daga DUTSE dai² da rana d'aya MAMA bata tab'a komawa garin nanba,y'an uwanta da suke ganin tana cikin rufin asiri zata taimaka musu,k'arshe duk wanda yazo sai dai ya koma yana k'unar zuciya,saboda MAMA korarsu takeyi bayan ta ci musu mutunci"
"To amma duk da haka MAN ya kamata mu hanzarta nemo wanda zai zauna da itan"
Duk sunyi shiru sun kasa tsai da matsaya akan wanda zasu samu ya zauna da MAMA a wannan yanayin da take tsakanin *RAYUWA DA MUTUWA*.........
*~Fan's ku taimako da d'an jinya,kunga dai MAMA ta koma.... Please ba don halinta ba..~*
😤😤😤
*_~TEAM KHUBRA.~_*
*~REAL SMASHER.~*
💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*28/ʝųŋɛ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Gaskiya na yarda kamar yadda kukayi alk'awari na gani kuma na tabbatar,babu abunda zanyi na saka muku face ci gaba da posting a duk lokacin da Allah ya bani ikon yin hakan,ina godiya kuma naji dad'in comment's enku.._
_Saboda haka zamu ci gaba daga inda muka tsaya in sha Allah SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV da kuma AUFANA suna tare da ku a ko wane lokaci kuma zamu ci gaba da tafiya tare,Allah ya bar k'auna da zumunci..._
_jinjina ga d'aukacin group's en_
*SMASHER & HUBBEEY NOVEL'S GROUP 1 & 2.*
*SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVELLA*
*SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE COMMENT'S ONLY*
*MUSLIM LADIES WW*
*SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE KITCHEN*
*BARRISTER ALEEYAH & MUHIBBAT NOVEL'S*
*SAWWAMA NOVEL'S*
*LEEMA NOVEL FAN'S*
_Allah ya bar zumunci da k'aunar junah..._
*~________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*3⃣6⃣*
*K* allon da taga BABA ZUWAIRA nayi mata ne yasa ta gimtse dariyar tata,tana d'an murmushi ta k'arasa kusa da ita ta zauna tana dafa k'afarta
"Allah kuwa BABATA ina cin abinci dayawama bakiga nayi kiba ba,kuma nayi k'arfi....
Kallifa kiga yadda nake iya d'aukan wad'annan robber en"
Kallonta kad'ai tayi ba tare da ta iya maganaba saboda yadda taga ta hak'ik'ance akan maganar ne yasa tayi murmushin yak'e wanda akance "yafi kuka ciwo"...
Kafin ta samu k'arfin guiwar yin magana
"Kayya dai KHUBRA wannan ba bigiren k'arfi bane,banda abunki ina kika tab'a ganin mace tayi irin wannan sana'ar?
Baya ga hakama su kansu mazan bakiga yadda suke wahalaba,kuma duk da haka ba kowa ne yake juran wahalar da wannan sana'a take da ba..
Ni kaina dan dai tun farko ina tsoron rasa ki,abu na biyu kuma tausayinki da rashin sanin hannun da zaki fad'a yasa ban musanta miki sana'ar nan da kika ce ita kike so...
Amma har ga Allah wannan sana'a bata kwantaminba"...
'Dan murmushi tayi ba tare da ta sake cewa komai akan abunda BABA ZUWAIRA ta fad'aba ta hau fad'in
"BABA bani abinci naci sai na tafi kinga dama ban shirya da wuriba,kada rana ta yimin a hanya"
Itama BABA ZUWAIRA ganin KHUBRA ta bagarar da maganar yasa tayi shiru bata sake cewa komai ba,saima abincin da ta mik'o mata...
Duk wani motsi da abunda take yi tana cin abincin,idanun BABA ZUWAIRA na kallonta...
Ita kad'ai tana cin abincin kamar bata so tana yi tana yatsina face enta kamar wacce akawa dole haka take cin abincin...
Da kyar take iya had'iyan abincin kamar mai shan magani....
Kai BABA ZUWAIRA ta gizgiza tana kallonta da tausayawa,yau kam ta rasa dalili da yasa y'artata take wannan abun
"Jikin ne yake damunki?"
Tayi tambayar tana dad'a k'ureta da ido..
'Dago idanunta tayi ta kalleta tana kad'a mata kai
"Wollahi BABA kwana biyu ina jin jikina babu dad'i,kuma na yau sai nake ji yafi na ko wane lokaci"
"Ayyaahh!sannu,amma toh me yasa kike son fita duk da bakya jin dad'i kam?
Ina ganin dai yau kam ki hak'ura da fita,idan Allah ya kaimu gobe sai ki je ko?"
Shiru tayi bata sake magana ba,har BABA ZUWAIRA ta gama shirinta,sai da tazo fita ta kalli KHUBRA
"To ni dai zan fita,kuma abunda na fad'a miki d'azu kiyi zamanki a gida gobe idan Allah ya kaimu kya fita,kin ji ko?"
"Toh BABA Allah ya kiyaye hanya,Allah ya bada sa'a"
"Ameen".....
Ta amsa mata....
Har ta juya zata fita daga gidan ta juyo tana fad'in
"Afffff!na manta kinga anjima kad'an zan aiko yaro ya kawo miki magani....
Me ma kikace yana damunki?dan na samu a sayomin a gurin d'an lafiya jari ennan"
"Wallahi gaba d'aya jikina ke min ciwo,cikin k'ashina kamar ana saramin da adda"....
"Ashsha!sannu y'ar nan Allah ya yaye miki kinji....
Ni na tafi sai na dawo"...
"To Allah ya kiyaye hanya"
"Ameen..."
BABA ZUWAIRA ta fad'a tana mai ficewa daga gidan gaba d'aya.....
《《》》
Damuwar da yake ciki a yau ji yake kamar a kowane motsawar second k'ara masa ake yi...
Duniyar tayi masa d'umi wanda ya rasa inda ya kamata ya sa kansa dan yaji sanyi....
Hannu yasa ya dafe kansa ta kowane gefe,inda KHALEEL ke zaune kusa da shi shima yayi shiru kamar wad'anda akace musu MAMA ta wula.....
Shiru kowa da abunda ke damunsa,kome BB ya tuna yayi saurin mik'ewa
"MALAM bani key"
Wani kallo KHALEEL yayi masa na jeka na gaji da kai,kafin yayi masa magana
"Me zaka yi da key kuma? ko nace ina zaka?"
"Kaga kawai ka bani ina ruwanka da inda zani?"
"Niko nake da ruwa da inda zaka...
Kasan dai babu yadda za ayi na baka key yanzu koh?kana cikin wannan halin za kayi driven en ko me?"
Tsaki yayi daga haka kuma bai sake kula shiba yayi shiru,sai kansa da yake juyawa side zuwa side....
ZUHRA dake tsaye ta kallesu tana shirin magana sai dai tana jin tsoron abunda zata fad'a kada taja BB yayi mata fad'a irin na d'azu...
Har tayi shiru kuma ko me ta tuna ta sake kallonsu tana fad'in
"YAYA KHALEEL dan Allah ka maidani gida babu kowa sai su HANEEF kafin MAMA ta farfad'o sai na samu nayi girki,nasan yanzu haka suna can da yunwa"
Shiru babu wanda yayi magana,sai dai abunda ta fad'a yasa KHALEEL en kallon BB yaga ko zai yi magana...
Ko tari baiba bare su sanya ran zaiyi magana,hakan da yayi yasa KHALEEL mik'ewa yana yin gaba,itama ZUHRA ta mara masa baya...
Har sunyi nisa a tafiya,ya d'ago yana kallon gurin amma bai gansuba,hanya yabi da kallo can daga nesa ya hangosu,a hankali ya mik'e zuciyarsa duk babu dad'i...
So yake yaje gida dan akwai abunda yake damunsa,shi yasa yayi saurin barin gurin....
Har sun isa gurin da sukayi parking motan ya iso,babu wanda yayiwa magana cikinsu ya bude back seat ya zauna had'e da jingina kansa da jikin seat en....
Motan shiru babu wanda yake iya cewa wani komai har suka isa gida......
《《》》
Misalin k'arfe 9:00pm ASHNA ta farka,har lokacin gudu suke shek'awa kan titi basu sauraraba,kallon gefe da gefenta tayi ta kalli yadda duk suka wani kafeta da ido,uban tsaki tayi wanda yasa guy en dake gefenta ya kalleta cikin magana irinta k'auraye
"Kee!ya dai?kinawa mutane tsaki"
Bud'ar bakin ASHNA sai cewa tayi
"Dallah ina ruwanka dani ko kaji na kulaka da zaka wani yimin shishigi?kun kama kun wani sato to waima gidan wace uwar zaku kaini?? Banzaye b'arayin y'ay'an mutane kawai.."
Furucin da tayi ba k'aramin kaishi k'ololuwar b'acin rai tayiba,take ya d'aga hannu da niyyar kifa mata mari sai dai me,tun kafin hannusa ya sauka kan fuskarta ta matsa jikin BIGGY tana fasa k'ara...
Kallonta BIGGY yayi duk ta cukuikuyeshi idanunta a runtse,kamar wacce za a zarewa rai..
Dariya gaba d'aya yaran nasa suka sa dan gaba d'aya drama'n da akayi suna jinsu,banda BIGGY da ya sake d'aure fuska yana hararan yaran nasa..
"Da Allah kuyiwa mutane shiru"
Ko gama rufe bakinsa baiyiba suka shiga taitayinsu,kallon wanda ke kusa da ASHNA yayi
"Ka maida hankalinka jikinka tun kafin ranka ya b'aci...
Daga yau kada ka sake k'ok'oarin aikata abunda kayi niyya kaji dai na fad'a maka"....
"Sorry OGAA hakan bazai sake faruwa ba"
Juyawa yayi ya kalli ASHNA da take murgud'a ma yaron nasa baki ya sake juyawa yana kallon window....
Tafiya ta mik'a inda basu suka isa gidanba sai misalin 12:00am,babu wanda ya kulata duk suka fice suka nufi cikin gida...
Sai BIGGY dake bayanta,haka ya tusata a gaba har cikin gidan,a ransa yake raya "anya kuwa zai iya hak'uri da chik ennan?"...
Shi kad'ai yana biye da ita yana kallon yadda take tafiya duk motsawan da zatayi duk da ba wani jiki ne da itaba amma shi kam tafiya take da imaninsa...
Ji yake kamar tayi ta tafiya yana binta a baya a haka har zuwa tsayin wani lokaci....
《《》》
Bayan shigansu gidan suka tarar da babu kowa cikin parlor,kitchen ZUHRA ta wuce dan yin girkin da tace za tayi,nan ta bar su BB da KHALEEL...
Jin shigowansu yasa su HANEEF,KHALEEFA da kuma FATAHIYYA fitowa zuwa parlor a tunaninsu tare da MAMA suka dawo...
Sai dai fitowansu suka tarar da BB su biyu cikin parlor babu MAMA...
"YAYA ina MAMAN take?"
FATAHIYYA tayi tambayar tana yamutsa fuska alamun damuwa shimfid'e saman fuskarta...
Tsawan da ya buga mata yasa tayi baya cike da tsoron yadda taga ya mik'e yayo kanta...
Dank'ota yayi yana zare jajayen idanunsa
"Dan uwarki ba kece fitinanniyar da duk kika jawo muka shiga wannan halinba"...
Yadda ya matse mata wuya yasa KHALEEL yin sauri ya fiszeta daga hannunsa yana fad'in
"Haba MAN me kake shirin aikatawa kenan?
Please!! Dan Allah kabi komai a sannu mana kada ka k'arawa kanka wata damuwar"
"Dan Allah ka kyaleni da wannan y'ar iskar yarinyar,idan ba saita musu zama akeba basa ganewa,gara na raunata ta ko zan samu zuciyata tayi sanyi"
"Haba mana to idan ka hukuntata hakan zai dawo da MAMA yadda take ne?"
A fusace BB ya bar gurin yana watsawa FATAHIYYA mugun kallon zamu had'u...
Shigansa bed room en ya hau safa da marwa a d'akin ya rasa me yasa a y'an kwanakin nan yake fama da mugun zafin zuciya...
Kansa ya dafe tare da fad'in
"Ya Allah ka kawomin mafita"
Zama yayi ya sake yin shiru,shi kad'ai kome ya tuna kuma ya sake mik'ewa da sauri ya shige bathroom....
Cikin k'ank'anin lokaci ya gama abunda yake yi ya fito duk abunda yaje yi yana yi ne cikin gaggawa,yana shirin fitowa KHALEEL ya shigo..
Binsa da kallo yayi a lokacin ne kuma kiran sallan Azhur ya katse su...
Babu wanda yayiwa wani magana haka KHALEEL en shima ya shiga toilet en...
Yana gama abunda zai yi ya fice daga gidan....
Fitowan KHALEEL ya tarar baya nan dama yayi tunanin haka tunda yaganshi yana gaggawan fita..
Da sauri-sauri KHALEEL ya shirya,cikin closet en BB ya bud'e wasu kayan ko amfani dasu ba ayiba,nan ya d'auki wanda yake ganin zai iya sawa a lokacin ya fice cike da gaggawa kada abunda yake tunani ya faru.....
Tada sallah da yaji anyi dai² lokacin da ya fito shi yasa shi tafiya masjeed en amma zuciyarsa tana cike da damuwan Allah yasa KHALEED ba tafiyan da yayi niyya yayi ba,in dai kuwa haka ne an samu matsala babbama kuwa...
Da wannan zullumin a ransa ya isa masallacin,sai dai yana shiga ya hangoshi a sahun gabansa..
Hakan da ya gani ne yasa shi yin hamdala ya dai²ta sahunsa da na kusa da shi ya kabbara sallah...
After an idar da sallah suka fito,gida suka nufa KHALEEL ya kalli side en BB
"Kafa sa naji tsoro wallahi dana fito ban ganka ba"
"Ohh!ni wai kake magana akai?
"To idan ba kaiba dawa nake?"
"Na sani ko ba dani kake ba"
Kai ya kad'a yana jinjina k'arfin hali irin na KHALEED da yake iya rainawa mutane hankali amma a fili sai ya bar zancen haka tare da sako zancen
"Ya kamata fa muyi tunanin abunda ya kamata muyi tun kafin dare yayi... Zuwa yanzun yaci ace mun nemo wanda zai ringa kula da MAMA saboda jinya ce sai mun sami mataimaki....
ZUHRA yarinya ce baza ta iya jinyan MAMA ita kad'aiba,ko dan school ensu bai kamata musa musu ido ace baza su ba dan MAMA tana kwance....
Yawwa!! Gaskiya ina tunanina ya kamata mu nemo HAJIYA LAURA dan ita kad'ai take da masaniya kan b'atan ZUHRA da kuma sace ASHNA da akayi a safiyar yau"....
A fusace BB ya kalle shi
"Ina ruwana da wata ASHNA taita b'atama mana ni babu abunda zai d'agamin hankali..
Ai duk laifin MAMA ne ya jawo haka ta faru,kuma ina tabbatar maka da sakamako MAMA ta fara karb'a tun a duniya"....
"Nasan da haka amma