Header Ads
Showing 147001 words to 150000 words out of 159513 words

Chapter 50 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1252

Ads at the middle of Article

bugun k'irjinsa
"Allah ni babu wanda ya ganni.."


"Sorry haka ne babu wanda ya ganki yi shiru to kada kiyi kuka..."


Bakinta ta murgud'a masa ta cikin mirror,tana kallonsa ya d'an cije lower lip nasa,kansa ya d'an sauke k'asa dai² kunnenta ya furta
"Idan ba tsoroba idan mun kwanta ki sake min haka ki gani..."


Kallonsa tayi ta masa fari da ido had'e da sake murgud'a masa bakin
"Yanzuma na sake me zaka iya yi...?"


"Haahh! yarinya ai tsoro kike ji shi yasa kikayi a nan,amma ki bari mu gama kinji..."
Murmushin mugunta ya mata ta cikin madubin,da k'yar suka gama abunda suke sannan ya d'auko musu nighty ensu,wani guntun singlet yasa mata mai d'an fad'i tsayinta duka bai kai kan knee's entaba,sannan ya d'auketa zuwa saman bed,ko daya direta fita yayi ya kashe duk kayan wutan dake gidan had'e da kullewa,bayan nan ya dawo ya kashe light en d'akin,kusa da ita ya kwanta ita kuma tayi saurin matsowa jikinsa..
"Wa na kama...?"


Ya fad'a lokacin data gama shigewa jikinsa yana mata cakul-kuli,dariya ta shiga kyal-kyalawa tana fad'in
"N....ii...Ka....kama..!"


"Ohh! na zata zaki ce ba keba ai....oyaaa! muyi bacci to kinji..?"
Kanta ta kad'a tana goge hawayen daya ziraro mata gefen idonta.Fake ya sakar mata a porehead daga haka bacci mai cike da nutsuwa ya d'auketa..............








*Aradu kwana biyu kunamin abunda ranku ke so,to nima zan muku abunda nake so,BB ya auri KHUBRA wato comment's kuma kun daina ko.....? Masuyi kad'an ne,so zan rage posting kullum nd yawan typing enma haka,zan maidasa 1 READ MORE kamar na cweet hulbateey...*










*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*












*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠







*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com


*©®2018*
*9/ɑմցմՏԵ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*




*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










6⃣3⃣










*H* ar tayi bacci shi kam idonsa a bud'e yake ya rasa me yasa ya kasa bacci a daren,farin cikinsa sam ya kasa b'oyuwa,yanda al'amuran suka faru yake ta tunawa,bayan d'umbin farin cikin data sa shi a safiyar,ta sake bashi wani bayan d'an tak'aitaccen lokaci wanda yafi kowanne zame masa abun farin ciki,shi ne yadda a ranar ta bayyanar masa a matsayin tana d'auke da juna biyu na y'ay'ansa,shi kam a yau bai san me zai mata wanda zai biyata d'umbin farin cikin data sashi ba,a ganinsa komai yayi mata bai biyata ba kan farin cikin data haifar masa,dad'a rungumeta yayi a jikinsa yana jin kamar ya maidata jikinsa su koma abu d'aya,sai da ya bari baccinta yayi nisa sosai sannan ya mik'e cikin yanayin da ya san bazai tashe ta ba,pillow yasa mata a inda ya tashi sannan ya rufe mata jikinta,fake ya sakar mata a porehead sannan ya shige toilet yana murmushi.
Wudu'u ya d'aura sannan ya fito had'e da saka jallabiyya ya shimfid'a pray mat ya hau kai had'e da kabbara,sallah ya shiga jerowa duk sujuda sai ya jima cikinta yana musu addu'a ta neman zaman lafiya,kariya da kwanciyar hankali,tare da neman zuri'a d'ayyiba.
Kusan k'arfe 2am sannan ya idar yayi addu'o'i a sauk'ak'e saboda yadda ya fara jin bacci,a nan ya bar pray mat en ya haura kusa da ita yana dad'a mannata da jikinsa,cikin lokaci k'alilan bacci mai nauyi game da dad'i ya d'aukeshi...


Haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya a yayinda ko wace rana take zuwa musu yadda suke fata da burin takasance,cike da soyayyar junansu suke kasancewa a ko wane weekends coz sauran ranaku ba wani isashshen lokaci gare su ba,amma idan aka ce weekend ya zo to nan zaka iske su tare komai kuma nasu tare suke aiwatar da shi,yadda suke gudanar da soyayyarsu da rayuwarsu a sauk'ak'e babu wanda zai gansu yaji basu birge shiba hasalima sai kaga mutum na kwad'ayin kwaikwayonsu...

Cikinta ya dad'a girma inda yanzun yake da wata takwas da y'an kwanaki,zuwa yanzun ya zamana babu inda take zuwa tana zaune gida,shikansa BB wannan dalilin yasa shi d'aukan hutu gurin aikin nasu duk kuwa da dama company ne nasu ABBA suke aiki dukansu ciki,so wannan yasa bai wani samu matsala da hakan ba inda ya damk'a ragamar hannun KHALEEL,sai dai wani lokaci yakan lek'a ya ga yadda al'amura ke wakana.


Suna zaune cikin parlour a k'asa kan rug,daga ita sai singlet mai d'an fad'i na shan iska kasancewar yadda cikin ya maidata gaba d'aya ta k'ara bud'ewa,k'afafunta a mik'e duk sun kumbura sosai babu mai kallonta yace cikin watansa takwas saboda mugun girman da yayi,shi kuma MR KHALEED sai aikin matsa mata su yake,jingina bayanta tayi jikin cuistion hannunta dafe da plate na fruit da aka yanka tana ci da fork,wani ta soko jikin fork en tana dariya tayi saitin bakinsa da shi,sai data bari ya bud'e bakinsa saita janye hannunta ta nufi bakinta da abunta tana masa dariya,kai ya kad'a mata alamar zai rama yana maida face nasa alamun yayi fushi.
"Sorry JAAN....!"
Ta fad'a tana kallonsa,d'auke kansa yayi yana ci gaba da b'ata fuska,wani ta d'auko tana sake kawowa dai² bakinsa,kamar bazai bud'e ba kuma sai ya bud'e,sake janyewa tayi tana masa dariya.
"Kingafa kina d'aukan hak'k'ina JODI idan ba bani za kiyiba kibar abinki nima idan na tashi babu abunda zaisa na sammiki nawa.."


"Haba mana JAAN kasan fa ni taka ce,kuma dai nasan zaka sammin ko...?"
Tayi maganar cike da shagwab'a tana kashe masa ido d'aya
"Haba yarinya babu wani wayo da zakimin kijima na fad'a miki.."


"Haba mana...nicefa...."


Still fuskarsa tana yadda take,yana kuma ci gaba da matsa mata k'afafuntan,janye k'afar tayi ta matsa kusa dashi kallonta kawai ya tsaya yi ganin ta janye k'afan nata kuma ta matso kusa da shi,kan cinyansa ta hau tana zagaye wuyansa da hannunta d'aya,while d'ayan kuma still da fork a cikinsa,grapes ta chaka ta kaishi bakinta,sai data gama melting ensa sannan ta kalli cikin eyeballs ensa tana kuma nufan bakinsa da nata,tun kafin ta k'arasa ya fahimci nufinta,wani murmushi ya sake mata yana dad'a rik'eta sosai a jikinsa,nasa ya bud'e ita kuma ta shiga zuba masa ruwan narkakken grapes en,licking mouth nata ya shiga yi,daga haka wasa ya canja salo,nan suka lula cikin wata duniyar ta daban,sun manta da duniyar da suke da kuma duk wani abu dake zagaye da su,basa iya tuna kowa da komai sai junansu,burinsu a ko da yaushe su faranta ran junansu.
Bayan komai ya wuce sunyi wanka yana shiryata,wayansa tayi k'ara,saurin maida rigan yayi kan bed ya nufi inda phone en ke yashe,MAMA ya gani tana kiran da sauri ko ya d'auka yana karata a kunnensa cikin sallama,amsa masa tayi sannan ta furta
"SON kana jina ko.....?"


"Ehh! MAMA wani abu ya faru ne..?"


"A'a SON ina so ne dai duk abunda kake yanzun ka kawomin BABY gida akwai wani abu dake shirin faruwa..."
'Dan kallo inda take yayi yaga shi take kallo,d'an murmushi yayi mata yana ajiye wayan kan mirror,inda take ya nufa yana zuwa yad'auka rigan ya sa mata,sannan ya nufi cikin closet ya d'auko mata Arabian gown wanda yake da d'an sakewa bazai kuma takurata ba,da mamaki take kallonsa coz ta jima bata fita ba
"JAAN ina zamu kuma naga kana shirin samin kaya bayan kasan banson zafi...?"


"No JODI zamu gida ne,ban san mene yake shirin faruwa ba,MAMA tace muje yanzun.."
Kai kawai ta girgiza masa alamun ta gane,yana gama shiryata shima ya shirya,d'aukanta yayi ya nufi hanyan fita da ita,hannayenta zagaye da wuyansa har ya sanyata a mota,k'ofar ya bari a bud'e sannan ya koma ya kulle gidan,cikin lokaci k'ankani suka iso,shigowa yayi parlour yana d'auke da ita,nan suka tarar da gaba d'aya mutanen gidan a babban palour,sauketa yayi suna bin cikin parlour en da kallo ganin yadda suma ake binsu da kallo,hannunta ya rik'e suka k'arasa ciki suka zauna,sannan suka gaida iyayen nasu dake zaune,suka kuma gaisa da sauran y'an uwan nasu,suka kuma shiga sahun jiran jin me ke faruwa akayi irin wannan taron.
SADEEQ BIGGY aka sa ya bud'e taron da Addu'a sannan ABBA ya fara magana yana kallon KHUBRA dake zaune ta mik'e k'afafunta
"Al-hamdulillah da Allah ya nuna mana rana da kowannenmu yake cike da farin ciki da kwanciyar hankali,muna k'ara godiya ga Allah daya had'a kawunanmu muke zaune da junanmu lafiya ba tare da wata fitina ta b'illo mana ba,sai dai a yau ina son ku bani aron hankalinku domin a kwai wani al'amari daya ke faruwa wanda cikinku babu wanda ya sani sai mu da muke zaune lokacin da abun ya faru haka kuma kuma wasunku sun sani sai dai da jimawa,amma idan kun saurari bayanin da za ayi yanzun zaku ita tunawa...
Da farko dai ke KHUBRA shin zaki iya shaida wad'annan mutanen dake zaune gefe...?"
ABBA ta kalla da yake mata nuni da gefe da hannunsa,hannun tabi da kallo zuwa inda yake mata nuni nan ko idanunta sukayi arba da wasu yank'wanannun tsofi mata su biyu d'aya jikinta duk wasu irin k'uraje sun feso mata a jiki saboda uwar daud'a data lillub'esu,kallon rashin sani tayi musu sannan ta kalli ABBA da sauran mutanen cikin parlour'n ta ce
"A'a ABBA ban shaida suba."
Matan dake zune gefe sai kuka suke kamar wani nasu ya rasu suka kalleta suna sake b'arkewa da kuka mai cin zuciya kowa su yake kallo,da k'yar suka kalleta d'aya tana fad'in
"KHUBRA yanzun baki shaidamu ba? tabbas babu makawa mu mun san masu laifi ne a gareki kuma dama babu yadda za ayi ki shaida mu,idan har baki gafarta mana ba to tabbas baza mu tab'a gamuwa da rahama ba cikin rayuwar da zamuyi dama wadda mukayi a baya saboda munyi rayuwa ne cikin k'unci.."
K'uresu tayi da ido duk dan ta gane su,amma hakan ya gagara ta kasa bambance kamanninsu.


"Ni ce fa MA'U KHUBRA...Dana kawo ki aikatau,wanda tun bayan wanni biyar dana kawoki ban sake waiwayoki b..."
Ido KHUBRA ta zare tana kallonta da mamaki shimfid'e kan fuskarta na yadda ta kasa game kammaninta,ko tantama babu d'ayar kam LADIYO ce dan kamarsu d'aya su biyun fun can da.
Daga nan MA'U ta kwashe komai daya faru tun bayan data bar gidan,yadda tayi mata asiri kuma cikin hukuncin Allah kasancewar bata da hak'k'i Allah ya kareta,sannan ta d'ora da yadda asirin yayi tasiri akanta ita,maza suka dinga binta itama tana binsu kamar dai yadda igiyar ruwa ke kad'awa gefe zuwa gefe,kaf ta kwashe komai har ciwon da take d'auke da shi a halin yanzun,wanda tun bayyanar cutar a jikinta ta koma gidanta,kuma har lokacin bata bar halinta na biye-biyen maza ba,a haka ne wata rana suna tsaka da aikata masha'arsu a soron gidan nata kawai sai ga wata mak'ociyarsu nan ta shigo da niyyar tambayarta kasancewarta bak'uwa a unguwar,ganin da tayi musu mak'ale da juna yasa ta fasa k'ara dalili kenan daya sa mutanen unguwa taruwa kasancewar da yamma ne kuma ranar babu aiki,da yake an san ba aure gareta ba nan ko aka shiga jibgarsu babu ji bare gani ta k'arasa da fad'in
"Da kyar na samu na gudu,daga nan ban zame ko ina ba sai nayi tasha na tafi garin KASHIN DILA gurin YAYA,a lokacin dana je na sameta cikin mawuyacin hali wanda ko abincin da zata cima gagararta yake,babu gurin kwana babu suturar kirki har sai tayi bara take samun d'an abun da zata sawa cikinta,a k'ofar gida cikin rumfa na isketa gidan kuma a kulle,ko dana tambayeta sai take shaidamin cewa MALAM BUBA ya sake ta,kuma gidanma ya sallama shi ga mai gari tare da sauran kadarorin da iyayensa suka bar masa,yayi kuma sallama da mutanen garin da sunan bazai sake dawowaba.Sannan ta sanarmin da KHUBRA kin koma tare da wasu mutane da suka shaidawa MALAM BUBA a hannunsu kike kuma dai da alamun suna da alak'a tsakanin su da shi MALAM en Lamar yadda muka samu labari yanzun,to bayan nan kuma muka ci gaba da zama a garin wahalar da muke ciki tasa muka baro can muka dawo nan gidan dana zauna a nan kano,bayan mun dawo nan mun d'auki lokaci muna zuwa wannan unguwar muna neman gidan dana kawo ki aiki,sai dai Allah bai nufa zan gane gidanba sai yau da muka shigo muna neman taimakon abunda zamu ci saboda duk wata dukiya da nake da ita ta k'are yanzun,sai Allah yasa muka ga matar dana kawoki hannunta.Shi ne ta shaida mana kinyi aure tun shekaru biyu da aula wuce,min nemi son ganinki ne a gurinta shine race my jira zata kira mijinki ya kawo mata ke.
Kunji abunda ya faru tun daga rabuwarmu har kawo yanzun ...
Parlour'n kowa yayi shiru mamaki game da d'umbin al'ajabi na hali irin na wad'annan mutane da suke zaune duk ya d'aure musu kai,KHUBRA kam zuwa lokacin hawaye sun gama wanke mata fuska banda godiya ga Allah daya kareta ya kuma tsareta daga fad'awa tarko ba tare da an samu damar keta mata mutuncin taba take yi,mik'ewa BB yayi ya kamata suka bar gurin duk maganar da suke yi na ta yafe musu kan cutar da ita da suka yi,bai bari ta tsaya gurinba dan shima da kansa haushinsu yake ji,kuma yayi niyyar d'aukar mataki a kansu sai dai ya tuna wata magana da suka tab'ayi da yake ce mata sai ya d'auki mataki kansu,amsar data bashi a lokacin itace ta sake dawo masa,dalili kenan daya sashi janyeta a gurin coz yana son rarrashinta...
'Dakinsa na da ya shige da ita,d'akin ta kalla da hawaye har lokacin a cikin idonta,yana nan kamar yadda yake da,key ya murzawa k'ofan danma kada wani ya samu damar shigowa,janyota yayi ta shige cikin jikinsa,yana d'an jijjigata har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take,bakin bed ya zauna ya d'orata akan cinyansa yana goge mata fuska,cikin kunnenta yake hura mata iska har sai da ta koma hayyacinta,mik'ar da ita ya sake yi tsaye tayi tunanin fita za suyi,da sauri ta rik'e shi tana sake sakin sabon kuka
"JAAN please kada ka mai dani gurinsu dan Allah baran iya zama guri d'aya da suba...kaji..?"

"Ok ok..! yi shiru babu inda zamu tunda baki so kinji ko..Zo nan na cire miki rigan kisha iska.."
Matsawa tayi jikinsa,sunkuyawa yayi a gabanta ya shiga bud'e mab'allan rigan jikinta,singlet ne a jikinta ta ciki sai nicker's,rungumeta yayi ya nufi saman bed da ita,kanta ya d'ora kan cinyansa ita kuma ta kwanta a gefenta na dama fuskarta na kallon fuskarsa,sai ajiyan zuciya take saukewa,gashinta ya shiga shafawa yana mata magan-ganu masu dad'i da kwantar da hankali,saboda kasancewarta mai d'auke da juna biyu daya tasamma tsufa ba'a son kasancewarta cikin b'acin rai,kafin wani lokaci sai gata ta ware har suna wasanni cike da nishad'i..


Can ko a parlour bayan barin su gurin MA'U da LADIYO sake b'arkewa suka yi da kuka ganin KHUBRA ta bar gurin ba tare da ta yafe musuba,kan irin cutarwar da suka mata,kuka suke suna k'arawa akan a kirata su nemi gafararta,shiru mutanen dake parlour en su kayi sai sauraren su suke sai da suka yi kukan son ransu wannan suka yi shiru, suna kuma dad's tonawa Kansu aspirin abubuwan da suka yita aikatawa Wanda aka sani dama Wanda ba a saniba,cike da tausyawa halin da suka jefa KHUBRA a ciki da mahaifiyarta data jima da rasuwa saboda girman kaidi da suka dinga shiryawa mutanen cikin parlour en ke kallonsu,da kyar UMMI ta bud'e baki tayi magana wanda yasa kowa ya maida kallonsa kanta,hatta kuwa da su masu koke-koken neman gafara,kiran KHUBRA da BB tasa ayi don kawo k'arshen komai,ko da d'an aike KHALEEL yaje ya tarar da k'ofa a kulle baiyi knocking ba ya dawo dan shima akan dole yaje saboda dai kawai bazai iya cewa UMMI a'a bane yasa yaje,sanar mata yayi da k'ofar a kulle take,sashi tayi ya koma yayi knocking ai ko kamar yadda ta umarta haka yayi,bud'ewa BB yayi sukayi ido hud'u da KHALEEL a nan ya coge ya kare k'ofar ba tare daya bawa KHALEEL damar gano cikin d'akinba ya furta
"Ya akayi ne...?"


"UMMI tana kiranku yanzun..."


Badon yaso ba ya koma ciki yana b'ata rai,shi kam babu yadda za ayima ya tasheta tana bacci,saboda haka ya fice had'e da kulle k'ofar,ganinsa shi kad'ai yasa suka kalle shi UMMI tana tambayan KHUBRA
"UMMI tayi bacci ne..."
Amsa daya bata kenan fuska a murtuke,aikuwa MA'U ta hau sheshshek'ar kuka,BB wani kallo ya jefeta dashi daya sata shiga nutsuwarta tana sunkuyar da kai k'asa,babu yadda basu yiba akan a tasota ta yafe musu,shi kuma ya kafe akan wallahi babu abunda zaisa ya tasheta,kawai

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads