Header Ads
Showing 57001 words to 60000 words out of 159513 words

Chapter 20 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1245

Ads at the middle of Article




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹










*©®2018*
*23/ʝųŋɛ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*


_AS'ALULLAHAL AZIIYM RABBAL ARSHIL AZIIYM AN-YASHFIYAKI *7_


_GWS duarling sis @CWEET HUBBEEY._


*~________________________~*


_*AUNTY G & AUNTY U* suna matuk'ar godiya da sadaukarwarki garesu gurin taya su murnan zagayowar ranar haihuwansu,fatan Allah ya k'ara zumunci da k'aunar juna.....Ameen..._
_@CWEET HULBATEEY._
*~________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*3⃣2⃣*








🇹un bayan zuwansa police station lokacin da ya kai photon da aka buk'ata,yake jiran jin sakamakon binciken daga wajen D.P.O amma shiru,har ta kai ga yau tsahon kwanaki bak'wai amma shiru kake ji....
_WAI MALAM YA CI SHIRWA...._



B'angaren Police kuwa da aka had'a BB dasu tuni suka fara aikinsu ba tare da sanin HAJIYA MURJA ko HAJIYA LAURA ba,dan ko kowacce akwai masu kula da al'amuranta duk zirga² da suke a idon hukuma suke aiwatar da hakan...


Shirun da BB yaji kwana biyu babu labari ne yasa shi kiran D.P.O yana neman k'arin bayani game da case en b'atan KHUBRA....
Cikin yanayin sarewa ya shiga kiran line en D.P.O,wanda cikin nasara ya d'auka ba tare da b'ata lokaci ba...
"Hello!yallab'ai barka da rana,ya aiki?"


Daga gefen D.P.O aka amsa masa
"Lafiya,Alhamdulillah!"


"Yallab'ai dama kira nayi na maka tuni naji kwana biyu shiru babu wani k'arin haske kan b'atan yarinyar nan"


Daga gefen D.P.O aka amsa da
"Ehhh!toh gaskiya nima dai abunda ya jima yana bani mamaki game da wannan case en shi ne,tun bayan da ka kawo photo da muka buk'ata aka watsa shi a kafafen sadarwa amma shiru har yanzun babu wani bayani da muka samu daga gurin al'umma,munyi nema munyi cigiya amma shiru har yanzun babu wani ci gaba,ina ganin dai kam sai mun k'ara hak'uri,mun kuma k'arawa abun lokaci muga yadda Allah zai yi ikonsa..
Amma har yanzun muna kan bincike da izinin Allah zamu sameta".....


Dogon ajiyar zuciya BB ya sauke kafin cikin kasala ya furta
"Allah ya bayyana ta"


D.P.O ya amsa da "Ameen"
Sannan ya d'ora da fad'in
"Ina fatan dai yaran da muka turo suna kan aiki,babu wata matsala da ake fuskanta"


"Ehhh!Yallab'ai babu wata matsala,aikinsu yana tafiya yadda ya kamata babu wata matsala"


"Ok! Babu matsala Allah ya bayyanata,amma a k'ara hak'uri"


"In sha Allah yallab'ai,na gode sosai"


Sukayi sallama,bayan BB ya ajiye phone en ya jima yana nazari kan wannan case en,shi kad'ai kuma ya mik'e ya zari car keys ensa ya fice...




《《》》


Tsaye take cikin super market en *JIFATU STORE* dai² b'arin y'an rugs tana dubawa...
Wayanta ne yayi k'ara a hankali ta bud'e jakarta ta fito da ita..
Rashin gaskiya ne yasa ta juyawa tana kallon yanayin gurin,babu kowa a arean da take shi yasa ta d'auki kiran ganin sunan dake lilo kan wayan...


"Hello HAJIYA MURJA kiyi hak'uri bana gida ne,shi yasa ban d'auki kirankiba,amma ki bari na k'arasa gida,yanzun ina *JIFATU* naje siyayya"


Daga gefen da aka kira cikin fad'a² ake magana wanda har wayan me magana ta farko tana amsawa k'asa²,ta yadda idan akwai wani a kusa zai iya jiyo abunda ake fad'a...
"Haba HAJIYA LAURA tun yaushe nake kiranki kink'i amsawa,idan abun nan ba mai yiwuwa bane yaci ace kin sanar dani,amma kin barni kara zube...
Waima dan Allah wasu sha³n kika sa suka yi aikin nan?"


"Haba HAJIYA MURJA nafa fad'a miki bana gida,kiyi hak'uri zan kiraki idan naje gida"


"Kinga HAJIYA LAURA dakata bana son jin wannan maganar daga bakinki kawai idan zaki tsaya muyi magana to idan kuma ba hakaba,wallahi zan zare hannuna a ciki duk lokacin da wannan lamarin ya kwab'e kada kiyi kuka da ni,kiyi kuka da kanki...
Kina da damar aikata duk abunda kika so,zab'i ya rage ga mai shiga rijiya....
Ko ki bani had'in kai muyi magana yanzun ko kuma ki kashe,duk lokacin da kikaga dama kya neme ni"....
Tana kaiwa nan tayi shiru tana sauraren jin me HAJIYA LAURA zata ce...


A gefen HAJIYA LAURA kuwa jin furucin na k'awar tata ya so ya bata tsoro amma ta dake tare da cizon leb'enta na k'asa,sai da tayi gefe da wayan sannan ta saki k'wafa....


"Babu damuwa muyi maganar yanzun"




Murmushin mugunta HAJIYA MURJA tayi sannan ta fara magana
"Ai ke nake sauraro naji baki cemin komai game da tambayan da nayi miki ba "


"Wane tambaya kenan?"


"Ce miki nayi wane sha³i ne suka yi wannan aikin?ina nufin wane gidadawa kika sa suka zo gidana ranan da aka sace yarinyar nan?"


Maganar HAJIYA MURJA ba k'aramin b'atawa HAJIYA LAURA rai tayi ba,haka ta danne tana bata amsa..


"Wasu yara ne da sukemin aiki,wani abu ya faru ne?"


"A'a kawai dai ina son sanar dake ne duk inda suke idan har suna cikin garin KANO to suyi gaggawar barinsa domin kuwa yaron nan ya tsananta bincike...
Sannan abu na gaba idan har sukayi abunda ya janyo aka kamasu to ki tabbatar musu da kada su sake suna na ya fito a cikin bakunansu...
Kuskuren dake cikin ambaton suna na dai² yake da rasa rai,na fad'a miki saboda haka ya rage naki,ko ki jaa musu kunne ko ki k'yalesu su aikata hakan"


Cikin sanyin jiki HAJIYA LAURA ta amsa,amma cikin zuciyarta cike take da tarin k'unci...


"Sannan abu na gaba ina so ki kula da duk wani al'amura naki,idanuna suna kanki,kuskure d'aya kikayi zaki ki hannun hukuma"....
Ita dai HAJIYA LAURA bata iya cewa komaiba,baya ga zuciyanta dake tafasa,wanda idan ka kalleta zaka iya gane tsananin b'acin rai da take ciki a kan fuskanya.....


Bayan sunyi sallama ne HAJIYA LAURA ta fara magana cikin b'acin rai ta furta
"Lallai HAJIYA MURJA wato ni take son mai dawa bagidajiya,to wallahi sai na koya miki hankali,zaki san dani kike zanc en"....
Cikin b'acin rai ta fice daga gurin ba tare da ta siya abunda ya kawota ba,ta kama hanyan komawa gida....
Zuciyarta tayi k'unci da maganganun da AMINIYAR tata ta gama yab'a mata,ita kad'ai take k'wafa idan ta tuna abun duniya duk ya isheta......


《《》》


"Hello!sir"
Aka ambata daga b'angaren mai kiran,wanda yake magana k'asa²,da alama kuma akwai wani babban al'amari a tare da shi da yake son sanarwa...

Bayan an amsa masa ya shiga koro jawabi...
"Yallab'ai akwai wata mata daga cikin assignment da aka bamu, yau nabi bayan matar zuwa *JIFATU STORE* dake kan hanyar *OBASANJO ROAD*...
Tabbas yallab'ai akwai wani al'amari a tare da matar,kuma daga dukkan alamu matar bata da gaskiya duba da yanayin yadda take magana a waya,da kuma yanayin data fito daga *STORE* en..."


"Cikin wane irin yanayi kaga ta fito?"


"Yallab'ai yanayin da ta fito yana nuna tana cikin tashin hankali"


"Shin akwai wani abu da ya faru? ina nufin wani abu ya faru da ita bayan shigarta gurin siyayyar?"


"Ehhh!yallab'ai bayan shigarta da kamar minti uku (3) naga ta d'auko waya a cikin jakarta ta hannu,to yallab'ai bayan ta amsa kiran wayan ne naga hankalinta ya tashi ta fito"...


"Lokacin da take wayan kana ina kai en?"


"Yallab'ai ina cikin gurin da ta shiga"


"Ok!ina fatan babu wanda ya kula da binta da kake"


Cike da ladabi Sergeant en ya furta
"A'a yallab'ai babu wanda ya gani"


"Da kyau aikinka yana kyau,abunda nake so da kai kaci gaba da bibiyarta,har mu tabbatar da gaskiyan abunda muke hasashe.
Allah ya taimaka"...


Daga haka sukayi hanging wayan...


Tunani BB ya tsaya bayan ya gama answering call en daga sergeant en,akan hanyarsa ta zuwa gidansu KHALEEL...
Da kyar ya katse abunda yake yama motan key zuwa gida,dan ji yayi bazai iya zuwa ba,hakan ne yasa shi canja shawara ya koma inda ya fito....


《《》》


Kwanaki sun ci gaba da giftawa kamar ana ingizasu....


Ta b'angaren binciken neman da akewa KHUBRA abu ya faskara dan ko zuwa wannan lokaci har an gama fidda rai,anyi cigiyan anyi neman amma shiru kake ji uwa an shuka dusa,wannan dalilin yasa BB yanke shawaran sawa a tsananta yin rok'on Allah game da matsalar duk da kuwa dama anayi amma yana da burin na wannan lokacin yafi na baya...
Haka kuwa akayi ko da ya tuntub'i KHALEEL bai yi k'asa a guiwaba ya amsa masa da fad'in
"Tabbas wannan ma shawara ce ya kamata muyi hakan,Allah dai ya bayyanata idan muna da rabon sake ganinta"


Suka amsa da amin cike da jimami....


《《》》


Zaune take cikin parlor ta hard'e k'afafunta d'aya akan d'aya,ta cije leb'e ta gama cika tamkar zata fashe...
Iska ta furzar mai d'umi tare da fizgo wayarta tana latsawa cikin fusata take magana..


"Haba BIGGY sau nawa zan sanar maka da ina nemanka,ko kuwa so kake sai raina ya gama yin duhu kafin ka zo?"
'Dan dakatawa tayi tana sauraren me zai fad'a


"To amma me yasa baka sanarmin da bakwa garin nanba ka b'oye??"


"Tuba nake ranki ya dad'e amin aikin gafara"


"Shi kenan amma magana nake son yi da kai mai matuk'ar muhimmanci,wanda bana son kowa ya sani,bayan ni da kai sai kuma yaranka,ka dai fuskanci me nake nufi ko?"


"Ehhh!HAJIYA amma idan babu damuwa kiyi maganarki yanzun kawai saboda bana son zuwa gidanki saboda tsaro...
Idan kuma wani aiki nema kiyi min bayanin yadda kike so ya kasance,za ayi miki duk abunda kike buk'ata"...


Jin furucin BIGGY ne yasa ta sakin murmushin mugunta kafin ta fara magana
"Toh! shi kenan,amma da san samu ne da ka zo gida ka same ni idan ya so sai muyi maganar,amma tunda ka sanarmin uzurinka na karb'a hakanma babu damuwa"....

Sai da tayi shiru na wasu y'an lokuta sannan ta soma magana
"Ka san me nake so da kai BIGGY?"


Daga gefensa ya amsa mata da fad'in
"A'a HAJJAJU"


"Ina son duk inda kuke ku je gidan dana saku aiki kwanakin baya,akwai wata yarinya da nake son ku satomin,amma idan kun sace ta kuyi nesa da ita bana son kuma a samu matsala kan wannan aiki,ina son kafin ku satota kuyi bincike sannan kuma ku tabbatar da babu wanda ya ganku...
Zan turo maka da photon yarinyar da zaku sato sannan ku tabbatar idan kun saceta kun sanar da ni a lokacin bayan kun d'aukota...
Ina fatan ka fuskance ni ko?ni kuma zanyi maka bayanin abunda zakuyi bayan nan,da fatan baka manta kwatancen gidanba"...


Dariya BIGGY yayi mai isarsa kafin yayi magana
"Amma HAJIYA ba dai yarinyar da muka sace ce ta dawo ba ko?"


"A'a wannan daban da waccan,wannan da nake son ku sato ina son 'DAUKAR FANSA ne akan mahaifiyarta,saboda ta nunamin ban iyaba shi yasa nake son ajiye mata DARASIN RAYUWA"....


"An gama ranki ya dad'e kamar anyi an gama wannan aikin,za muyi duk yadda kikace"
Sai da suka gama kitsa duk wata mugunta sannan sukayi sallama...


Zuciyar HAJIYA LAURA fal da farin cikin wannan al'amari tana zaune tana kad'a k'afa sai sakin murmushin mugunta take.......
_AYI DAI MU GANI...._


《《》》




*3 MONTH LEAP.*




KHUBRA ce rik'e da kuran ruwanta na sana'ar *GARUWA* k'afarta sanye cikin takalmin *FILLO SHOES* daga saman kanta ko ta kifa *HAT* na gargajiya,takalmin duk ya sha d'inki saboda gajiya da yayi..


Wani yaro ne ya gifo a guje daga wani k'aramin gida yana fad'in
*"Y'AR GARUWA* ki kawo ruwa gidanmu za a siya"


A hanhali taja hulan dake kanta baya kad'an tana kallonsa,fuskanta da d'an fara'a duk da yadda tayi duhu fatarta duk tayi wani iri abun tausayi...
"To amma zo nan"
Ta umarci yaron da yake shirin komawa a guje,jin ta kira shi ne ya matso..
Kunnensa ta d'an kama a hankali tana fad'in
"Suna nane baka saniba ka kirani da *"Y'AR GARUWA"* ko kuwa iskanci ne yasa kayi hakan?"


"A'a na sani"
Ya fad'a yana dafe gefen fuskarsa ta side en da ta rik'e kunnensa....


"Daga yau naji ka sake fad'in wannan sunan sai na mareka,kaji ni ko?"


Da sauri yaron ya gyad'a kansa alamar yaji kuma ya bi...


"Yawwa k'anina,maza to ungo wannan"
Ta sa hannunta cikin jakar dake d'aure jikin west enta ta fiddo da sweet....
Da murnansa ko ya karb'a yana tsalle,yana fad'in
"Daga yau idan ban sake fad'a ba zaki dinga bani alawa?"


"K'warai kuwa zan dunga baka"


"YEEEE!ya" fad'a yana tsalle "Idan zaki dinga bani har YAYA zan dunga ce miki kinji ADDA KHUBRA"


Murmushi KHUBRA tayi tana shafa kansa cikin so da kulawa..
"Maza to jeka gida gani nan zan kawo muku ruwan kaji?"
A guje ya juya ya shige gidan cike da murna...


Tana kallon shigewarsa ta d'an tsaya tana murmushi ita kad'ai tasan halin da ta shiga lokacin da taji yaron ya kirata da ADDANSA,wani siraran hawaye ne yayi layi akan fuskanta,da kyar ta tsaida hawayen nata tana mai goge su.......


~Ni da nake gefe cike da tausayin halin da take ciki "nace KHUBRA har yanzun kina nan da halinki na son kuka"...~
~My HULBATEEY kuwa hawaye naga tana sharewa kan tsananin tausayin yadda taga KHUBRA ta koma....~






*_~KEEP FOLLOWING FAN'S....~_*






*~TEAM KHUBRA.~*








*_REAL SMASHER._*
💠







*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹










*©®2018*
*24/ʝųŋɛ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Wannan page tukuici ne gareku masoyana tabbas ina jin dad'in kasancewa tare daku kuma ina jin dad'in addu'o'inku gareni Allah ya bar k'auna,jinjina gareku *Fatima Ibrahim,Fatima Zois,Fateema 🌹, Fatima M.D* dama duk wani/wata masoyin/masoyiyar *SMASHER* wollah ina matuk'ar k'aunarku har cikin jini da b'argona nake jinku,Allah ya bar k'auna,ina godiya sosai da sosai,ina yinku irin *#TOTALLY* en nan...*SMASHER* tace ana *_~#ANA MUGU MUGUN TARE..*_~_

*~________________________~*


_*AYSHA B 《AESHAB》* wollah muma muna yinki kuma muna sonki,ki jima kiyi k'arko cweety Allah ya bar k'auna *SHDG* na godiya sosai bisa karamconki garesu.._
*~________________________~*
_Masoya muna buk'atar ku tayamu addu'ah DURLING SIS babu lafiya,fatan zaku dubi buk'atarmu...Allah ya tashi kafad'unki cweet HUBBEEY._
*~________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*3⃣3⃣*








*D* a kyar ta iya saita nutsuwarta ta kama hanyan shiga gidan da yaron ya fito d'azun,hannunta d'auke da robber 25 litters...
Da sallama ta shiga gidan,bayan sun gaisa da matar gidan ta shiga juye ruwan da ta kawo cikin mazubin da aka nuna mata,bata kai da gama abunda ya kaita ba,ta jiyo yaron nan yana fad'in
"Inna kinga alawana da ADDA KHUBRA ta bani d'azu"


Y'ar yank'wananniyar matar da aka kira da inna ta kalli yaron tana d'an murmushi
"Aaaaaa!aikuwa angode,Allah ya saka da alkhairi.....
Ina fatan dai kace ka gode ko?"


"Laaaa!inna na manta ban fad'aba"
Yaron ya fad'a yana rufe bakinsa da hannu..


Ran inna ne ya b'aci jin furucin yaron dake gabanta,cikin fushi² ta janyo rigarsa
"Sau naw nake fad'a muku duk wanda zai muku kyauta ku dinga cewa an gode,ko ban fad'a muku ba?"


"Dan Allah inna kiyi hak'uri wallahi mantawa nayi"
Kamar zaiyi kuka yake maganar


"Aii ba dainawa za kuyi ba,ina jin saina fara k'wacewa zaku shiga hankalinku,tunda bakwajin magana"

"Wollahi inna bazan k'araba"


"Maza wuce kace mata ka gode,kafin na sab'a maka"




Da gudu yaron ya matso kusa da KHUBRA dake shirin fita yana fad'in
"An gode ADDA KHUBRA"


Batayi magana ba sai murmushi da tayi kad'ai ta d'aga masa hannu,daga haka tayi waje tana sha'awar halayyan matar na ganin yadda tayi tarbiyyan yaranta.....


《《》》


Tun daga wannan lokacin da BIGGY suka yi magana da HAJIYA LAURA suke observation a unguwan na RIJIYAR ZAKI dai² area'n gidan na HAJIYA MURJA...
Sai dai da yake suna da wasu ayyukan na daban a kuma gurare da dama yasa har aka d'auki lokaci mai tsayi ba tare da sun gudanar da aikin da aka sasu ba....


Kamar wani mahaukacin gaske haka yake acting ta yadda kowa ya ganshi ba zai iya ganewa ba cewa mahaukaci ne na gaske ko kuwa na bogi ne?....


Haka yake

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads