Showing 138001 words to 141000 words out of 159513 words
Chapter 47 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt
hanyar fad'in
"Haba hajiya bafa wani girman da kikayi da karatu kuma da kike wannan maganar ma SHEHU JAHA ma cewa yayi acikin labarinsa *"GEMU BAYA HANA ILIMI"* sannan kinga kuma yanzun baki san wane irin y'ay'a Allah zai azurtamu da suba,shin bakya sha'awar ace kin bada naki gudunmawar ta b'angaren ginuwar iliminsu...?"
Shiru ta sake yi tana nazarin maganarsa,ita kad'ai a zuciyarta take fad'in
"Gaskiya dai kuma da haka,ko ba komai zanyi alfahari da kasancewar hakan idan har ya faru,to amma abun tambayan shin zan iya kuwa....?"
Tambayan daya tsaya mata a rai kenan,ta kasa samun wani ya bata amsa,ganin jikinta yayi sanyi da maganar kuma da yiwuwar ya canja mata ra'ayi yasa baiyi k'asa a guiwa ba ya shiga kwad'aitar da ita amfanin karatun,wanda a k'arshe ya samu nasaran amincewarta,dan BB cewa yayi bazai mata doleba idan har ta nuna bata so zai bita a sannu har saita amince,saboda a nasa tunanin cewa yayi
_"Duk abunda wani yake so wani yayi,idan har wanda ake so yayin ba shida sha'awar hakan to tabbas baza a samu nasara ba amma idan yana so nan ne zaka ga ya dage dan ganin ya aikata wannan abun kuma burinsa zaka tarar bai wuce na ganin yayi nasara ba"_
Murmushin samun nasara yayi yana shafa lallausan gashinta dake kwance yasha gyara
"Uhmmm! JODI kenan wato kenan fa wai gani kike kin girma ko...?"
"Haba mana YAYA kaimafa kasan na girma ai yanzun ai wani abun da zanyi shi da a yanzun kam ko da kud'i banyinsa,bare kuma da hankalina ai baranma soma aikatawa ba"
"Gaskiya kam amma ni banga wani girman da kika yiba har yanzun"
Mik'ewa tayi a jikinsa ta tsaya tana juya jikinta cikin salo tace
"Haba YAYANAH kallenifa kaga yanda na koma hakama ai wani cewa zaiyi na zama uwar mata.."
Dariya kalamanta suka sashi,sai dai kawai ya gintse yana kallonta yana murmushi,janyota yayi yana maidata muhallinta data tashi
"Lallai kam babynah ta girma,amma wannan girman ai daban wanda nake nufi daban"
"To wanne kake nufi kai...? ni dai nasan na girma yanzun"
"Eh haka ne nima nasan kin k'ara girma amma ni barin fad'a miki irin wanda nake nufi.."
Kallonsa taci gaba dayi tana sauraren jin me zai ce,hannunsa tajiyo k'asan cikinta yana shafa dai² mararta yake fad'in
"Da ace kin girma ina tunanin ni ne mutum na farko da zai tabbatar da haka,kuma da nan gurin ya tabbatarmin da hakan koba haka bane..?"
Sakin bakinta tayi tana kallonsa,lallaima YAYA'N nan nata ya rainata da yawa wato nufinsa har yanzun bata girmaba kenan yake nufi? Har sai ya ganta da ciki zai yarda lallai ne kuwa ta bashi mamaki kuma tabbas ta d'auki alk'awari saita nuna masa itan ta girma.
Bata sake bi takan maganarba tayi cilli da ita gefe,idanunta ta lumshe tana jin yadda yake shafa k'asan cikinta ita kam bata san wane irine YAYA'N nata ba duk wani abu da zaiyi ya jefa zuciyar mutum cikin soyayya ya iya,gani take da ada ne aka tambayeta yaya halinsa yake zata ce babu ruwansa shi en kamili ne kuma bashi da fitina,amma kam a yanzun cikin d'an tak'aitaccen lokaci ta gama fuskantarsa a nata tunanin tsaf zata zane littafi hard cover da halayensa,katse mata tunani yayi da fad'in
"JODI ki shi shiryafa cikin satin nan zaki fara zuwa makaranta"
Daga haka bai k'ara ko wasalin 'a' ba ya d'inke bakinsa ta hanyar rufe idanunsa danma kada ta dameshi da tambayoyi,hakan data ga yayi yasa ta yin murmushi cikin sanyin murya ta furta
"Allah ya kaimu,ubangiji kuma ya bamu sa'a..."
Amsawa yayi yana yadda yake tare da sakin mata kiss a porehead enta,murmushi tayi tana sake tightening hands enta dake jikinsa,kamar masu bacci haka palour'n yayi shiru baka jin maganar kowa cikinsu amma kuma a hakan hira suke da junansu,kiran daya shigo wayan KHUBRA ne yasa ta d'ago ta kalleshi,shi enma ita yake kallo mik'ewa tayi daga jikinsa inda bayan ta d'auka kiran ta shiga gaida MAMA,tambayan da MAMA tayi mata ne yasa ta kallonsa da sauri kuma ta d'auke kanta tana ci gaba da sauraron maman dake maimaita mata tambayan
"Doughter wai kam ina son tambayanki,ranan da kuka zo gida mai ya had'aki da ABBA ne kam har kika janyo ya miki fad'a...?"
Ajiyar zuciya tayi kafin cikin sanyi ta shiga bawa MAMA labari bata b'oye mata komaiba,a b'angaren MAMA kam taji dad'i sosai da yarinyar tata tayi wannan tunanin sai dai kuma dalilin da yasa ABBA ya mata fad'a shine tayi k'aranta ta fad'a masa wannan maganar kamata yayi dama a samu mutum wanda yake babba mai cikakken hankali sai ya nusar da shi cikin hikima da siyasa,kuma tabbas al'amura zasu tafi yadda ya kamata idan haka ta faru.
Nasiha tayi mata sosai akan ta kira shi ta bashi hak'uri sannan kuma kada ta sake yin maganar da kowa,haka dai har suka gama wayan ta ajiye,suka sake ci gaba da uzurin gabansu...
Kwanaki sun ci gaba da wucewa yayin da kowace rana da zata zo ta wuce take tafe da nasarori masu d'umbin yawa.A bangaren su KHUBRA da BB ma hakan ce ta kasance inda maganar makarantar ta ya kankama,makaranta mai kyau wacce kuma zata koyi karatun babu wasa ya kaita,kuma alhamdulillah! al'amura na kyau sosai,shi da kansa yake kaita school sannan idan an tashi shi yake zuwa ya d'aukota,ko da ace yana office ranar da zaran lokacin komawanta gida yayi zai tattara abunda yake yi ya tafi,sai ya maidata gida sannan zai koma office ya k'arasa aikin ranar,wata ranar kuwa idan ya dawo tofa bai komawa sai dai gobe.
Rayuwarta a makarantar wani lokacin idan ta kalli da yawan d'aliban sai taga akwai wanda ko a shekaru ya girme mata bare kuma girman jiki da wasu tsaf sai su d'auketa suyi ta gudu da ita ba tare da nuna gajiyaba,wani lokaci idan taga haka sai take tuna BB lokacin da yake mata maganar karatun,sai dai kaga tayi murmushi ita kad'ai.
Zaune take k'ark'ashin wata bishiya tana duba littafinta da suka gama lesson,tayi nisa a dubawa taji an mata sallama,d'agowa tayi dan ita a tarihin zuwanta makarantar babu da wacce suke k'awance,wata y'ar matashiyar budurwa ta gani tsaye tana mata murmushi,kyakykyawa da ita son kowa k'in wanda ya nema bai samuba,cikin dakewa ta amsa mata suka gaisa a mutunce,kallonta waccan d'ayar tayi tana fad'in
"Idan babu damuwa kuma ban takura mikiba shin zan iya zama...?"
'Dan murmushi KHUBRA tayi ganin itama da fara'a a fuskarta tayi maganar
"Babu komai bismillah! ki zauna"
"To ai kuwa na gode sosai da amsamin da kikayi.."
Matashiyar ta fad'a kafin cikin d'an yanayi na kasancewarsu sababbi a gurin ta furta
"Ni suna na AMINA UMAR FANA,nima sabuwar d'aliba ce a nan,to kuma ban san kowa ba a nan sai yau Allah yasa na ganki nayi kuma sha'awar miki magana ban sani ba ko zamu iya zama k'awaye.."
"Allah sarki ai nima da yake sabuwar zuwa ce shi yasa kika ga na zauna nan saboda babu wanda na sani,amm! ni kuma suna na KHADIJAT ABUBAKAR SA'AD amma a gida ana kirana da KHUBRA.."
Dukansu suka yi murmushi wa junansu,a hankali suka ci gaba da hira jefi-jefi kuma mafi yawanci duk akan karatunsu na ranar da suka yi ne,sosai tarayyarsu ta basu sha'awa ganin sun taimakawa juna da abunda d'aya ya gane d'aya bai ganeba,har lokacin tashinsu yayi,dai² lokacin aka zo d'aukan AMINA inda tayi ta yima KHUBRA magiyan tazo su tafi tare,hak'uri ta bata tana kuma fad'a mata itama yanzun za a zo d'aukanta,haka ta tafi wanda suna yin gaba BB yayi parking,glass en side ensa ya sauke yana kallonta,d'an murmushi tayi kafin ya fito ya bud'e mata ta shiga,sai da suka d'auki hanya ba tare da ya kalletaba yace
"Wane mota na gani ya tsaya inda kike....?"
Shiru ta masa babu amsa,shi kuma yaci gaba da fad'in
"Kina sane da cewa ke matar aure ce ko...? to ina so ki kiyaye kule-kule babu ruwanki da kowa coz bana son fitina kinji me nace...kiyi abunda ya kawoki babu ruwanki da shiga abunda ba a sakiba kinji...?"
Kanata ta d'aga alamar taji.
Kwanaki biyu tsakani take bashi labarin AMINA da suka had'u a school irin kirkinta da kuma yadda suke zaune da juna,yaji dad'in yadda ta fad'a masa abunda ya had'asu kuma shima ya tabbatar da cewa yes matarsa kam y'ar baiwa ce,yanayin yadda yake zama suna lesson kan abunda aka musu a makaranta duk bayan sallar maghreb yasan tabbas baya asara...
Tun bayan da sukayi magana da MAMA akan dalilin daya sa ya mata fad'a a wani zuwa da sukayi a can baya,MAMA bata b'oyewa ABBA'N su BB komaiba ta sanar masa cikin hikima da siyasa shi da ABBA'N KHALEEL suka sashi gaba da maganar,sosai suka kai ruwa rana da su wanda daga k'arshe kuma yaga rashin dacewar k'in amincewar da yayi tun farko,shi da kansa ya same su da maganar daga baya,cikin lokaci k'alilan aka gama magana,da taimakon MAMA da UMMI suka sata gaba itama kuma sai Allah ya taimaka basu wani sha wahala ba ta amince,an yanke d'aurin aure kad'ai za ayi sai tariya kuma babu wani taro da zasu yi bare mutane su fahimci wani abu game da sirrinsu,cikin lokaci kad'an aka d'aura auren ALHAJI ABUBAKAR SA'AD da amaryarsa HAJIYA ZUWAIRA akan sad'aki mafi inganci,anyi taro lafiya wanda y'ay'ane kad'ai suka halarta babu wata gayyata da suka yi daga iyayen sai su.
ASHNA kam lokacin bikin tana ta fama da laulayin ciki kuma sosai take shan wahala,babban dalili kenan daya sa FATAHIYYA komawa gidanta tana taimaka mata,palour suka rashe sunata hira tsakaninsu BB,KHALEEL,SADEEQ BIGGY,KHUBRA,ZUHRA dama ASHNA dake fama da kanta amma a haka ta dage itafa saita zo dan baza ayi babu itaba,FATAHIYYA kam d'akinta na gidan ta tsere dan cewa tayi bata iya zama gaban yayyen nata da ko wanne yake manne da matarsa ita a nata ganin kam wannan fitsarar da suke gwadawa bata iyawa.
Haka aka gama taro kowa ya d'auki matarsa yayi gaba,sai fatan samun zaman lafiya da sab'awar halaye.
Lokaci baya jira sai dai a jira shi kamar yadda wannan magana take haka fa abubuwa suke,bayan kimanin watanni biyar da auren ABBA'N KHUBRA,ASHNA ta haifi zankad'ed'en saurayi Yaro yaci sunan ABBA'N BIGGY wato MUHAMMAD suna kiransa da AL-MUSTAPHA,fad'in hidimar suna da suka sha a wannan family'n b'ata baki ne,yayin da a b'angaren ZUHRA da KHUBRA kuma shiru kake ji babu wacce tayi ko da b'atan wata,sam hakan bai wani dame suba dan ganin samu da rashi duka daga Allah suke lokaci kad'an yake azurta mara shi kuma hakan ma ba abun damuwa bane tunda duka yaushe akayi auren da zasu d'aga hankalinsu,a b'angaren karatunta kuwa ta dad'a maida hankali sosai k'awancen su da AMINA kuwa sai abunda yayi gaba,mutane da dama suna mamakinsu wanda bayan tsayin watannin da suka shud'e kowacce ta san y'ar uwarta nada aure,k'awance na tsakani da Allah suke duk inda kaga d'aya cikin makaranta to zaka ga d'aya,mazajensu sun san juna yanzun baya ga ziyara da sukan kaiwa junansu,sun dad'a dagewa akan harkar karatunsu abunda ya kaisu shi suke yi babu wasa,tsakaninsu da mutane gaisuwa ce suna kuma matuk'ar girmama junansu.
Yau tunda KHUBRA ta shigo skul take baza idanu taga inda aminiyar tata zata b'illo amma shiru kake ji,zaman makarantar duk ya isheta haka dai tayi manage har aka tashi,ko data koma gida bayan ta kirata a waya a kashe aka shaida mata,yinin ranar haka ta yini wani iri da ita wanda shi kansa BB sai da ya gane haka,ko da ya tambaya bata b'oye masa komaiba ta sanar masa,addu'ah ya nusar da ita tayi kan Allah yasa lafiya.
Washe gari tana shiga skul ko ta hangota har ta rigata zuwa,da saurinta ta k'arasa kusa da ita tana fad'in
"Haba CWEET SIS jiya kuma sai najiki shiru,kuma line wayanki a kashe haka naita fama da tunanin lafiya..."
"Allah sarki y'ar uwa ta gari wallahi ki bari ke dai,ai ban baki labari ba,kwana biyu ne sai a slow wollah duk dare da wani irin zazzab'i nake kwana,shi nefa ogana yace lallai sai munje asibiti to ni nake k'in zuwa sai nace masa makaranta,shi nefa jiya na tashi da shi aiko shi ne yace mu tafi asibiti dana ce makaranta baki ga yadda yamin fad'aba har yana cewa lafiya ita ke gaba da komai.."
"Kai amma naji dad'i daya miki haka banda abunki ai oga gaskiya ya fad'a..."
"Ke dai bari kawai ai kuwa munje hankalinsa ya kwanta.."
"To ya jikin hope komai normal...?"
"Uhmm! ke dai bari inafa normal.."
Da sauri KHUBRA ta kalleta tana fad'in
"Kamar yaya kenan?"
"Babu komaifa da wasa nake miki,da sauk'i sosai sai dai kun samu k'aruwa.."
Wani ihu KHUBRA tayi tana rik'eta
"Wayyoo! kice min ciwon kenan dama.....To Allah ya raba lafiya,ubangiji ya kawo mana su masu alkarka.."
Wata y'ar class ensu ce ta lek'o da yake ta iya gulma da munafurci a makarantar coz idan kana neman expert ta munafukai ka samota to ka gama,nan take fad'in
*"AUFANA* lafiya kuke ihu da wannan safiyar..?"
Wani kallon k'asan ido KHUBRA ta mata tana fad'in
"Lafiya k'alau ko kinji ance miki ba lau bane..?"
"Au too..."
Ta fad'a tana barin gurin,yadda AUFANA taga KHUBRA tayi da fuska yasa ta yin dariya tana fad'in
"Kai CWEET SIS ki d'an saki fuska mana irin wannan had'e rai haka kamar wata BOSS.."
Dariya dukansu sukayi AUFANA ta furta
"Allah sarki harna tuna da wata mak'ociyata mai suna *JIDDAH* da take bani labarin yadda mijinta yake a da kafin a musu aure,wallahi ko da take fad'amin ita da sister enta *MEINERH LITTLE* sun sha wahalarsa shi yasa suke ce masa *YAH BOSS* amma kuma kafin aurensu da bayan sunyi aure data fuskanci halinsa shi kenan wai shi raini ne baya so shi yasa ya dinga musu haka..
Kuma yanzun haka wallahi idan kika ga yadda suke zuba luv sai kinyi mamaki,ammafa suna da kirki wollah musamman suka had'u su uku da wata sister en tasu mai suna *HUBBEEY* gaskiya ranar duk da suka zo har bana son mu rabu saboda y'an chapter ne.."
"Allah sarki Allah ya bar musu zumuncinsu.."
Inji KHUBRA dake k'ok'arin bud'e littafi don tana son yin nazari kafin malamin ya shigo
"Ameen ya Allah...aiko wata rana Allah ya kawoki suna nan wallahi zaki ji dad'in kasancewa da su...yini d'aya idan kukayi da su wallahi ji za kiyi kamar kun shekara da su,Allah dai ya had'aku nasan zaki k'aru da zaman da za kiyi da su sosai.."
Murmushi kawai KHUBRA tayi lokacin da take mai da hankalinta kan littafinta,itama AUFANA nan ta d'auko nata tana fad'in
"Yawwa teacher KHUBRA yau kece malamata dan kinga jiya ban zoba saboda haka amin bayanin lesson en jiya,nasan dai kam YAYA'N ki bazai barki ba sai yayi miki karatu na musamman.."
Dariya suka sake yi duka,can kuma suka tsunduma cikin karatu...
Suna zaune suna karatunsu,wani malami ya taho zai wuce bayansa da wata d'aliba itanma dai baza ta wuce tsaransuba a shekaru kallon-kallo suka yi da ita,kafin suka ci gaba da abunda suke yi,har malamin ya gota su,sai kuma ya dawo yana tambayarsu wane class suke,fad'a masa suka yi ya juya ya kalli wannan d'alibar yana fad'in
"Yawwa to kinga ga y'an uwa nan kin samu class enku d'aya da su,ki rik'esu su zasu baki masauki tunda sun jima a nan..."
Godiya ta masa sannan ta musu sallama suka gaisa a mutunce ta nemi guri ta zauna kusa dasu tana sauraron yadda KHUBRA ke zubo bayani kamar wata lecturer.Saboda yadda take bayanin karatun ko malamin nasu yaji dole ne ya sara mata saboda wani abun ma bai bud'a musu bayaninsa kamar yadda take yiba yanzun,sai da suka gama sannan AUFANA ta kalli bak'uwar tasu tana fad'in
"Sannu dai y'ar uwa..."
A mutunce itama ta amsa mata tana murmushi,saboda itama ba dai arhar dariya ba..
AUFANA tace
"Ni suna na AMINA UMAR FANA amma zaki iya kirana da AUFANA saboda sauk'ak'awa ma'anarsa kuma AU na farkon AUFANA yana nufin AMINA UMAR,shi ne idan kika had'a shi da FANA zai baki cikakken sunan,ita kuma y'ar uwata sunanta KHADIJA ABUBAKAR SA'AD,amma ana kiranta da KHUBRA."
Murmushi ta sakeyi tana fad'in
"Na gode sosai da amsata da kukayi...ni kuma sunana *MARYAM HAROUN SULAIMAN* amma ana kirana da *JANNAT*..."
Hira suka d'an tab'a kafin suka koma class saboda ganin teacher na tahowa...
Watanni sun sake zuwa har sun shud'e inda har sukayi jarabawoyi da dama wanda yanzun gashi har sun sake samun ci gaba na changing class..
Wata rana suna zaune suna hira su uku kasancewar yanzun sun zama su uku kuma k'awancensu babu algus cikinsa,suna ta hira a wata ziyara da suka kaiwa AUFANA da cikinta ya soma tsufa...
AUFANA ce ta kalli KHUBRA da JANNAT tana fad'in
"Sisters ena niko zanso jin labarinku da dalilin daya sa bakuyi karatu da wuriba musamman yadda naga Allah ya rufa muku asiri gidajenku da family enku babu talaka cikinku.."
Kallonta sukayi duka suna murmushi saboda irin shak'uwar da sukayi da juna yasa suka san da wasu sirrika na junansu,KHUBRA ce tayi gyaran murya tana fad'in
"Ai kuwa dai kam ya kamata musan dalilin dayasa mu duka haka ta faru damu,amma kafin naku bari kuji nawa...."
Gyara zama sukayi dukansu,nan ta shiga basu labarin gwagwarmayar da tayi fama da shi a rayuwarta,sai dai kamar wancan lokacin data b'oyewa BABA ZUWAIRA farkon had'uwarsu haka suma ta b'oye musu da sa hannun MAMA a saceta,da kuma wasu abubuwa da suka faru a matsayinta na wacce bata son aga laifin iyaye da danginta..Bayan ta k'are su duka hawaye ne kwance a fuskokinsu suna jinjina labarin nata da tayiwa lak'abi da *Y'AR GARUWA..*
"Lallai kin sha wahala sister amma haka Allah ya kaddara mana rayuwarmu...Badan lokaci daya k'ure ba dana baku nawa labarin sark'ak'iyata wanda nayiwa lak'abi da *"BAMBANCIN AL'ADU"* (My upcoming novel) amma