Header Ads
Showing 6001 words to 9000 words out of 159513 words

Chapter 3 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1208

Ads at the middle of Article

B
A A
T B I
R
A




*(YAYA HAYAT) ADMIN OF ADMINS.......*




_Wannan ranar taka ce,babban Admin mai kundin novels, *WRITER'S* naka *REDER'S* naka,kana k'ok'aree gurin nishad'antar da d'aukacin members enka dake cikin_
*COOL NOVELS GROUP'S 1,2,3,4 & 5, MAKEUP ND KITCHEN GROUP* _Allah ya k'ara 'daukaka,ya k'aro maka shekaru masu albarka,kana mai wadatuwa da imani,kwanciyar hankali........_


_Wannan page en naka ne kai d'aya kayi yadda kaso da shi....._ ✍🏻✍🏻




🍾🍾🎂 *HAPPY BUFDAY WULLNUP ADMIN...* 🎂🍾🍾


*~__________________________~*


*ADDU'AH YAYIN TASHI DAGA BACCI*


_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AHYANA BA'ADA MAA AMATANA WA-ILAIHIN-NUSHUUR..._




_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AFANIY FII JASADIY WARADDA ALAIYYA RUHIY WA-AZINALIY BIZIKHRIY....._




*_~#HISNUL MUSLIM...~_*




*~_________________________~*






*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*






_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._


*~__________________________~*






*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*0⃣6⃣*







*I*ta d'aya zaune tayi shiru,abun duniya duk ya taru ya mata yawa......


Tunanin gida da mahaifinta duk shi yafi damun zuciyanta,ko a wane yanayi yake? Allah shi ne masani......
Ganin babu sarki sai Allah,shi yasa ta bawa zuciyanta hak'uri......
'Daki ta sake komawa,bayan ta tura k'ofan gida,da yake ta san ita kad'ai ke gidan,gudun kuma kada wani abu ya faru......




***********


Tafiya take duk inda ta samu watsa k'afafuwanta take,tamkar wacce zata tashi sama.....
Son kud'i irin nata ya hanata neman abun hawa......

Sai da tsakiyan rana,ganin babu haza yasa ta hak'ura ta nemi keke napep,daga UNGUWAN KURNA zuwa RIJIYAR ZAKI,a ganinta nan ne unguwar masu kud'i,za tafi samun gidan aiki,idan bata samuba kuma,zuwa gobe sai ta nausa cikin gari......
Zafin rana da k'ishi su suka haddasa mata tsaiwa,ta nemi abun hawa,idan yaso sai ta k'arasa,in da ta nufa......
Ta tsayar da masu napep sama da guda goma,amma da sun tsaya suke k'arawa babur en nasu wuta suyi gaba.......
Da kyar ta samu abun hawa,kan neman ragi irin na MA'U......
Yinin ranar yawo ta dungayi gida² take bi a unguwan na rijiyar zaki,kan neman gidan da suke neman Y'AR AIKI.....


Sai da ta sha wahala,kafin ta samu gidan da suka nuna mata suna buk'ata......
Sun gama ciniki kan dubu biyar per month......


Duk iya yinta na su k'ara mata wani abu,hakan ya faskara....
Gudun kada tayi asara gashi wannan d'inma da kyar ta samu,bayan yini da tayi tana GARARIN DUNIYA yasa ta amince,akan zata kawota daga zaran sun gama shiryawa......
Abinci matar ta kawo mata da ruwa mai sanyi.......
Ta gama d'amke cikinta,sannan tayi mata sallama........
Godiya tayi ta tafi da alk'awarin nan da Sati d'aya zata dawo......




***********


Kwance take tana ta faman bacci wanda bata san lokacin da ya d'auketaba,tayi nisa cikin baccinta.......




**************


Tun daga nesa ta hango ingarman dokin wanda akewa lak'ani da KILI ( wato mai fari biyar),kansa mutum ne zaune,cikin farare tas en tufafi......
Matsowa yaci gaba da yi,wanda har sai da yazo daf da ita sannan ne ta iya gane mahayin murmushi d'auke kan fuskansa......
Sai da ya zo gabanta,sannan yaja linzamin dokin ya tsaya.....


Har lokacin tana tsaye fuskanta cike da mamakin ganinsa......
Mutumin daya ce bazai sake dawowaba yau shi ne a gabanta yau.......


Saukowa yayi cikin isa,ya tako har zuwa gabanta....
Cikin wani irin voice da bata tab'a jin irinsa ba tunda take a gaba d'aya tsawon rayuwanta,ta tsinkayo shi yana fad'in
_''Amincin Allah yaci gaba da tabbata agareki''........_


Kasa amsawa tayi saboda tsananin mamaki da yak'i barinta har yanzun......


Hannunta ya kama cikin wani irin salo,ya jata jikinsa.....
_''Haba wifey,ni en ne baki ganeba ko kuwa na zame miki wata sabuwar halitta?''......_


Kuka ne ya kufce mata,jikinta banda rawa babu abunda yake,tsabar tsoro ta kasa magana,sai hawaye dake ta ambaliya a fuskanta.....
Duk k'ok'arinsa da son ganin ta bud'e baki tayi magana abun ya gagara......
Janta yayi ya had'a jikinsu guri d'aya,ganin yanda jikinta yake ta faman b'ari......


Maimakon a samu sauk'i saima k'aruwa da aka samu.........
Kukantane ya sake tsananta,kan dole ya raba jikinta da nasa....
Fuskanta ya kama ya d'ago,tsura mata ido yayi


_''Shin bakiyi farin ciki da ganinaba ne wifey?''...._


Kai ta girgiza masa,alaman
A'a


_''Baby maganafa zakiyi,bana son wannan nodding en''......_
Cikin hanzari ta bud'e baki da niyyan magana
_''A'a,ina mamakin yanda ka dawo gareni ne,alokacin da bantab'a tsammaniba''........_


Fuskanta ya shiga goge mata,yana murmushin jin dad'i......






**********


k'afafuwanta tamkar wacce taje sharan gona,sunyi futu² kamar basu tab'a ganin mai ba.......


Sai murna take na samun gidan aikin da tayi,haka ta sauka a napep en da ya sauketa bakin titi.....
Ta sake ninkawa ta shiga cikin unguwan,a k'ofar gida taja burki,ganin k'ofan a rufe,ta shiga huci.....
Bugun k'ofa ta shiga yi,jin shiru ba a bud'eba,ta shiga dukanta da k'arfi tamkar zata karya.......




************


Cikin baccinta mai dad'i mai cike da mafarkin da a kullum shi ne birinta....
Ta tsinkayo bugun k'ofan da tamkar a tsakiyan kanta ake......
Bud'e idonta tayi,cikin sauri ta mik'e ta nufi k'ofa,har tana had'awa da d'an gudu,wanda saura kad'an ta fad'i,amma haka ta daure ta tunkari k'ofan..........










*_~Uhmmmm ko me KHUBRA zata tarar yau kam.......~_*








*_~KEEP MOVING...~_* 😍😍😍












*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠



*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹












*©®2018*


*23/mąrcɧ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_


🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹








_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._






*~__________________________~*




*ADDU'AR SANYA TUFAFI.*
_________________________


_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY KASANIY HAZAS-SAUBA,WARAZAK'ANIHI MIN GHAIRI HAULIN MINNIY WALA KUWATTA......._


*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*


*~__________________________~*




*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*






_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._


*~__________________________~*






*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*0⃣7⃣*







*K*okawa ta shiga yi da k'ofan,wanda da kyar ta samu ta bud'e......


K'ofan na gama bud'ewa idanuwanta sukayi arba da MA'U tsaye,idanunta sunyi jajur dasu kamar garwashi.....
Kamar ance ta kalli k'afarta,ai kuwa nan ta hangi k'afar tayi busu²,dan k'ura da daud'a......


Duk k'ok'arinta na ganin ta kaucewa yin dariya abun ya faskara....
Nan ta fara tuntsirar dariya,kamar kwancen mahaukata.......


MA'U dake tsaye tana jiran a bud'e mata k'ofa,taga ta tsaya tana mata dariya.....
Tsaiwa tayi ta dafe saman gini,tana kallonta,sai dariya take,kamar sabuwar kamu.......




Tsabar mugunta irinta KHUBRA har dafe gefen cikinta take,ita bata matsa daga kan hanya,ta bawa MA'U guri ta wuceba,ita kuma bata tsaida dariyan taba......




Kallonta MA'U taci gaba dayi,ganin abun nata ba na k'are bane,kuma ta rasa me KHUBRAN kewa wannan dariyan a tare da ita,abun ya soma bata haushi....


Ga haushin ta rufe mata k'ofa,sannan ta zo tana mata dariyar rainin wayo.......




Hankad'ata tayi cikin soron,ta shigo tare da maida k'ofa ta rufe.....
Wani gigitaccen mari MA'U ta aikawa KHUBRA da shi,wanda ta jishi,babu shiri kuwa ta had'iye dariyarta.......
Gashin kanta ta dank'a ta jata zuwa cikin gidan,sai zage² take kamar y'ar maguzawa......
Babu zato bare tsammani MA'U ta shiga jibgar KHUBRA kamar ta samu jaka ko ince kayan wanki.....

Tun tana dukanta KHUBRA na iya yin ihun neman ceto har ta koma muryanta ma bata iya fita saboda laushi da jikinta yayi.....


Sai da tayi mata dukan sa'a,sannan ta yasar da ita a gurin ta shige d'aki,ba tare da ta furta ko 'A' ba,zuciyarta kamar zata fito waje saboda haushi.....

KHUBRA dake yashe a k'asa babu,abunda ake iya ji na daga sautin muryanta,banda numfashinta dake fita da sauri²......
Ta jima kwance a gurin,wanda ta gagara koda motsin kirki......




***********


Tun tahowar MA'U da KHUBRA birni,hankalin ABBAN KHUBRA yak'i kwanciya.....
Kullum cikin tambayar LADIYO yake yaushe MA'U zata dawo da ita.....
Amsar dai guda d'aya ce kullum,dazaran lokacin da suka d'auka alk'awari yayi zata dawo da ita.....
Shi kam kullum yana jinta ne,don kuwa ya fuskanci idon MA'U bud'e yake da son nera,tsoron sa d'aya kada su cutar masa da ita.....


Abu sai dad'a gaba yake,LADIYO ta shiga tashin hankali ganin yadda malam en yake neman d'aga mata hankali,har bata so ya shigo ya tarar da ita zaune,yanzun zai dasa mata maganar y'ar tasa mai kama da aljanu.....




Yau ma zaune take cikin y'ar rumfar karan dake bakin d'akin nata,wanda daga nan kana iya hango k'ofar shigowa gidan.....


Zafi duk ya addabeta,daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta.....


Malam buba ya kawo kai zai shigo cikin gidan,da sallama a bakinsa....
Ko amsawa bata yiba ta mik'e cikin hanzari zata bar gurin.....


''Dakata LADIYO,na fuskanci kwanan nan nema kike ki mayar dani wani sha ka tafi''.....
''Ko dai yau ki fad'amin inda y'ata take ko kuma aradu ina mai kai k'ararki gurin MAI GARI''.......

Ido waje LADIYO ta juyo,nan ta shiga bashi hak'uri.....


Saboda LADIYO irin matan nan ne masu d'an karen tsoro,ammafa akwai tsokana....
Idan akwai abunda LADIYO take tsoro a duniyarta kuwa baya wuce MAI GARI ko a ambaci mai bak'in kaya wato ('DAN SANDA).....


Har k'asa ta zube tana masa magiya,akan zata kira MA'U ta dawo da KHUBRA idan ma bata sametaba zata je da kanta ta dawo da ita har gida ba sai maganar ta jega HUKUMA ba.....


Girgiza kai MALAM BUBA yayi,ya juya ya nufi d'akinsa
''Da dai yafi miki kwanciyar hankali''......
Yana fad'a ya k'arasa shigewa ciki.....




LADIYO dake durk'ushe a inda MALAM BUBA ya barta ta d'ago tana dafe k'irji....
Ganin babu MALAM en a gurin tayi wuf ta fad'a d'aki....
Nan ta shiga raba ido kamar shege a rabon gado (yo dama me zai kawo shi tunda yasan bashi da ko allura)?.....


Ita kad'ai ta shiga magana da kanta
_''Ya zama dole nayi aron waya na kira MA'U ta dawo da wannan shegiyar yarinyar mai kamar aljana,tun kafin kashina ya bushe''....._


Ko gama tunanin batayi ba ta zara mayafinta ko riga babu ajikinta,tayi waje......
Bata zame ko inaba sai gidan k'awarta mai suna TABAWA.....






******
TABAWA irin matan nan ne y'an duniya,wad'anda suke da bud'ad'd'en ido.....


Da shigarta ta tarar da TABAWA ta cokalo d'an kwalinta sai zabgawa mijinta rashin mutunci take....
Shi kuwa bawan Allah kansa a k'asa kamar wanda ke gaban uwarsa haka jikinsa sai b'ari yake.....




Bata k'arasa shigowa ba ta tsaya daga bakin k'ofa,tana kallon wannan abun aljabi.....


''Dillah can banza kawai,zaka bani ko kuwa sai na cajeka?
Katabbata idan har na laluba na tarar da kud'i a jikinka,wallahi yau kam babu kai babu cin abinci a gidan nan''.....
Ta fad'a tana hak'ik'an cewa....


Rantsuwa ya shiga yi mata,sai kace d'a da uwa,amma hakan bai sa TABAWA ta yarda ba.....


Rigarsa ta kama ta cukuikuyo shi,ta shiga lalube aljihunansa kaf,sai da ta tabbatar da abunda ya fad'a sannan ta kyaleshi tana fad'in
''Allah ya cece ka''.....


''Amma ba kyaleka nayi ba wallahi,zan ranta maka kud'in cefanen yau,kana samu kayi hanzarin biyana idan kuma ba hakaba,zaka had'u da tijarar da tafi wannan''......






Ita kam LADIYO na nan tsaye tamkar an dasa bishiya,ta lula cikin tunani,har bata san lokacin da mijin k'awar tata ya fita ba......


Dogon ajiyan zuciya tayi,kafin jiki a salub'e ta afko gidan ko sallama babu......
Binta kawai TABAWA tayi da ido
A ranta kuma tana fad'in ko lafiya?


*_~NIKO NACE OHO MUKU.........~_*














*_~KEEP MOVING....~_*😍😍😍






*_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠



*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*Viawattpad@realsmasher01.*






*©®2018*
*25/mąrcɧ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_


🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._


*~__________________________~*


*ADDU'AR SANYA SABABBIN TUFAFI.*


_ALLAHUMMA LAKAL HAMD ANTA KASAUTA NIHI AS'ALUKA KHAIRAHU WA-KHAIRA MAA SUNI'A LAHU,WA'A'UZU BIKA MIN SHARRIHI WA-SHARRI MAA SUNI'A LAHU..._


*~#HISNUL MUSLIM.~*




*~__________________________~*




*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*


_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._


*~__________________________~*






*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*0⃣8⃣*







*T*ana nan kwance in da MA'U ta yasar da ita,kamar matacciya,idan ba wai mutum ya kula da yanda chest nata dake shibring ba,za a iya cewa ta jima da mutuwa....


**********
Cikin kwanciyar hankali MA'U tayi kwance kan gadonta,ko kad'an batayi nadamar abunda ta aikataba,bare ta duba taga halin da y'ar mutane ke ciki ba....
Idonta tar kan selling tana nazari kan wannan gidan aiki da ta samu....
Ita kam a nata ganin,da zaran ta samu wani aikin da yafi wannan maik'o zatayi watsi da wannan....
Ko dama ace ba a garin kuwa zatayi aiki ba,ita meye damuwarta,tunda ba ita ta haifeta ba.....
Burinta bai wuce a kawo mata masu gidan rana......


************


Wani uban tsaki TABAWA tayi lokacin da ta kalli LADIYO,da alama tunani take....


Da k'afa ta kai mata hauri...
A firgice LADIYON ta d'ago tana k'ok'arin mai da kallabinta da yake shirin fad'owa....


Jajayen hak'oranta ta bud'e wanda babu abunda ke fitowa daga bakin nata banda wani irin azababben wari,ga su duk sun dafe saboda tsabagen daud'a.....


Kallonta TABAWA tayi tana fad'in
''LADIYO ince dai ko lapia kike irin wannan dogon nazari haka?''.....


''Ke dai bari TABAWA ina cikin tashin hankali wollahi''....


Fuskanta da tsananin mamaki take kallon LADIYON da take koro mata jawabin abunda ya had'o ta da MALAM BUBA akan yarsa......


Dariyar mugunta TABAWA ta hau yi,tana tafe hannunta....
Sai da tayi mai isarta kafin ta saurara,tana k'arema LADIYO kallo,tana tab'e baki....


''Uhmmmm!LADIYO kenan,ni ai a ganina ke kika so,da har kika tsaya MALAM BUBA yake zuba miki irin wannan rashin mutunci,da d'iban albarka haka
Ni baki ganniba,washar da ni,tunda mu ba haihuwa za muyiba,ai gara muyi abunda muke so,kafin dare d'aya suzo mana da maganar k'arin aure''.....


Baki bud'e LADIYO ke kallon TABAWA,da ta tak'ark'are tana koro

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads