Header Ads
Showing 135001 words to 138000 words out of 159513 words

Chapter 46 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1249

Ads at the middle of Article

yarda ba zamu tambaya amma da *sharad'i* idan akace irin nawa ne zaki bani wani abu..."
Ya k'arasa yana mata winking.


"Hahhhh! YAYANAH sharad'i dai sharad'i dai ko wane lokaci kacemin kana da sharad'i,ni kuma na fad'a maka na daina yarda da sharad'in nan naka...Sai dai ka fad'i wani abun amma banda sharad'i..."


Cikin shagwab'a ya furta
"Ni gaskiya a'a shi kad'ai nake so,kuma idan baki yardaba zanyi miki kuka har sai kin rarrasheni da wannan abun zan hak'ura nayi shiru..."
Yanayin da yayi magnar yasa ta kwashewa da dariya tana fad'in
"Wai kam YAYANAH baka gajiya ne...?"


"Dame zan gaji JODI.....? dake wai kike nufin zan gaji ko me..?"


"Eh mana wancan satinfa sam baka barni na hutaba wannan ma haka...wai kam idan aka ce na haihu ya za kayi lokacin...?"
Hak'oransa ne suka bayyana a fili yana mata murmushi cikin d'oki da farin ciki ya furta
"Allah ameen JODI..ni yanzunma bank'i ace mun samu k'aruwa ba..yanzun ace cikin kwanakin nan nayi ajiyar baby a nan ai sai nafi kowa farin ciki.."
Yana maganar yana shafa k'asan maranta,murmushi kad'ai tayi bata yi maganaba,hakan yasa shi fad'in
"Ko bakya farin ciki ne JODI....?"


"Me ka gani YAYANAH..."


"Naji kinyi shiru ne daga maganar ciki,kuma bayan ke kika kawo zancen.."


"Laaaa! YAYANAH me yasa bazan soba bayan ya fito ta sanadin abunda nafi k'auna,shirun da nayi wani abu nake tunani ne.."
Da sauri ya dad'a rik'eta a jikinsa yana fad'in
"Haba JODI bayan gani a gabanki wane tunani kuma za kiyi..?"


"YAYANAH kenan ina tunanin ranar da za ace an kaini asibiti zan haihu ne...har na fara jin tsoro Allah.."


_Dariya sosai maganarta ta bani nida nake gefe,cikin da ba ama tabbatar akwai ko babu ba shi ne har ake tunanin ranar haifeshi...Allah ya kyauta muku da kuke maganar cikinma._


"Laaaaa! JODI mene ne abun tsoro ai tare zamu haihu,kin san baran tab'a barinki kisha wahalaba duk rintsi muna tare a mak'ale da juna.."
Mab'allan gaban rigarsa da suka kasance a bud'e wanda hakan ya bawa lallausan bak'in gashin dake kwance saman k'irjinsa damar bayyana,tasa hannu tana wasa dashi kanta kwance gefe tana ci gaba da abunda take,kamar wata k'aramar yarinya sai ta d'an ja a hankali ta saki tana sosa masa gurin wanda ya kasance kamar tafiyan tsutsa,a hankali ta kalleshi tana fad'in
"Laaaaa! YAYANAH kacefa zamuje gida kaga kuma naga kana rufe ido Allah yasa ba bacci zaka ce za kayiba....ko kacemin na bari sai an jima..."
Ido d'aya ya bud'e while the other one yana rufe
"Sai zuwa anjima idan na gama abunda nake.."


"To ammafa naga a kwance kawai kake,mai zai hana mu tafiya yanzun...?"


Idanunsa a rufe duka ya furta
"Na ce saina gama abunda nake.."


"Ammafa YAYANAH...."
Bakinta ya rufe yana fad'in
"Bana son yawan maimaita magana mu barshi iya haka JODI,idan na tashi yanzun zan sake shiryawa.."


"Shiri kuma wane iri..? canja kayan shi ne shiri kuma YAYANAH"


"A'a ba iya changing kaya bane kad'ai.."
Da mamaki a fuskarta take k'arewa fuskarsa kallo,coz maganarsa ta d'aure mata kai ta kuma kasa fahimtar abunda take nufi
"Ni dai gaskiya YAYANAH ka tashi mu tafi kagafa idan rana yayi cewa za kayi sai wani lokacin...kuma ni Allah ina son zuwa kaji..."


"Ok! muje kimin wanka to tunda kina so mu tafi yanzun..."
Ba tare daya bud'e idanunsaba yayi maganar
"Wankafa kace YAYA bayan tare mukayi wanka'n da kai...me zaisa ka sake wani sabon wankan kuma..?"


"Kece.....! kece zaki sani sakewa.."
Fuska da alamun tsoro tace
"Nifa Allah YAYANAH banyi komaiba,ta ina na zama sanadin da zaka sake wanka kuma...?"
Hannunta da take wasa da shi har lokacin a jikinsa ya rik'e yana fad'in
"Saboda wannan abun da kike yi mana,ni kuma kinga baran ce ki bari ba..."


"Hahhhh! YAYANAH haka ka koma kuma...Tabbb barin sauka a jikinka tun kafin wata ranama kace kwanciyan da nayi yasa ka....."
Bakinta ta damk'e tana dariya jin irin rik'on da ya sake yi mata
"Babu inda zaki je har sai kin k'arasa aikin kwangilar da kika amsa..."


"Hahhhh! YAYANAH kenan ni dai nasan babu wani kwangila dana karb'a sai dai ko ban saniba yanzun za a bani..."


"Uhmm! JODI kenan kwangila ai tuni kika karb'a signing ya rage kiyi..."


"Gaskiya YAYANAH ban san yaushe ka koma haka ba..."


'Dagowa yayi yana kallonta idanunsa a kanta yake fad'in
"Ke kika mai dani haka JODI tunda kinga ni lafiyayyen namiji ne,so dole sai kinyi hak'uri dani sannan kuma sai kin koyi juriya saboda mijinki..."


"Yo to YAYANAH wane juriya kuma bayan wanda nake da ita har wani zan koya..."

Dariya yayi mata "Noo! ina sone ki k'ara akan naki da kike da shi.."


"Hahhhh! to ni dai gaskiya ka tashi mu shirya mu tafi...Kaji...?"


"Ai sai kin k'arasa aikinki sannan zan yarda mu tafi,idan kuma bara kiyiba za a fasa tafiyan..."
Ya fad'a teasingly yana kashe mata ido d'aya,fuskanta ta shagwab'e kamar za tayi kuka,da sauri ya dakatar da ita yana fad'in
"Noo! kin san tun can bana son yawan kuka,so kuma abun nan it's a matter of deal,idan kin yarda shi kenan mu gama abunda ke gabanmu kafin mu tafi idan kuma ba haka ba shi kenan an fasa tafiyanma gaba d'aya.."
Kallonsa take kamar sakarai saboda jin yadda yake ta tsara zance kai ta langab'e gefe bata iya cewa komaiba,ammafa idanun nan kamar wanda aka tsoma cikin ruwa
"Yawwa! sannan idan kika yi kuka shima an fasa tafiyan yau sai wani lokacin..."
Da sauri ta shiga maida hawayenta duk dan gudun kada a fasa tafiyan yau,bayan ta gama sawa a ranta zataje taga su MAMA...
Wani killer smile ya saki yana dad'a janta jikinsa,idanunta a rufe saboda bata son tayi kuka coz tasan halin abunta tunda yace idan tayi za a fasa tsaf zai fasa en tun ba yauba tasan halinsa a d'an zaman da tayi a gidansu.Tana jinsa yana laluben bakinta ta bud'e masa dan kam a wannan lokacin gardama ba nata bane,sannan tun farko tayiwa kanta alk'awari duk abunda zai faru bazata tab'a hana shi hak'k'in saba duk runtsi,saboda a kullum abunda take tsoro kada ta hana shi Allah yayi fushi da ita,baya ga tsinuwar mala'iku da zata yita sauka akanta.
_To k'alubalenku matan aure dama y'an mata masu niyyan yin aure,wasu suna d'aukan hakan a matsayin fansa idan miji ya musu laifi sai kuji ana cewa zamu had'u da shi a gado ne ai wallahi sai ya gane kuskurensa,shin y'ar uwa idan kika yi haka bakya tunanin faruwar wani abune kam? misali ya miki laifi yanzun shi kenan baki da wata hanya davzai gane ya miki laifi har sai kin had'a da bi ta wannan hanyar? to idan baki saniba ki bud'e kunnenki ko kad'an dan kinyi haka ba shi kika cutaba kanki kika cuta,kuma ki sani yin hakan tamkar kin d'auki wuk'ane kin dab'awa kanki,dan kuwa a lokacin da yake tsananin buk'atarki idan baki bashi kankiba to tabbas abunda ba a fata zai faru,imma dai ace daga wannan lokacin ya fara bin matan banza idan har da baya yi,imma kuma idan yana yi ya k'ara a kan na da,ya rage naki ki gyara ko karki gyara,amma kam tabbas idan kika yi haka k'arshe zaizo miki da sakamakon abunda kika jefaku ciki,sannan kuma ga tsinuwar mala'iku baya ga fushi da Allah zaiyi da ke,kafin kuma ki samu k'arin tsinuwar mutane ta soma yawo akanki,kinga saiki zab'a bashi hak'k'insa ko tsinuwar....Allah ya bamu ikon gyarawa._


Harshenta yake lalube ganin yana neman wahala ta mik'a masa nan yaci gaba da aikin dake gabansa,sai da suka gama jagwalgwala junansu sannan cike da farin ciki suka koma toilet,bayan sun gama shiryawa suka fito kai da ganinsu zaka gane wannan d'anyu ne a amarci,hannunsu sak'ale dana juna,ko a motanma yana driving hannunsa d'aya na cikin nata kamar wanda za a kwacewa ita,idan ya kalleta sai suma juna murmushi mai d'auke da sak'onni daban-daban haka har suka k'arasa mai house nasu.
Ko gama daidaita parking bai yiba ta shiga k'ok'arin fita,da sauri ya dad'a rik'o hannunta,wani kallo wa watso mata idanunsa a narke yake kallonta,kanta ta sunkuyar k'asa da sauri
"Saurin mene kike yi ne kam...Kina so mu koma ba tare da mun shigaba ko..?"

Kanta ta shiga girgizawa kamar za tayi masa kuka,dariya yayi k'asa-k'asa
"To idan kina so mu shiga ki bari mu tafi tare,bana son wannan gaggawa'n da kikeyi.."
Dakatawa tayi har ya gama abunda yakeyi sannan ya fita,shi ya bud'e mata k'ofan ta fito cikin tafiyan sa ba zai ce tayi sauriba,hannunta ya rik'e a haka suka cimma parlour'n gidan.
Sallamansu tasa MAMA da BABA ZUWAIRA fitowa daga kitchen suna fad'in
"Maraba da amarya...."
Hannunta ta fizge daga nasa tayi jikinsu da d'an gudu,rungumeta sukayi suna y'ar dariya game da tsokanarta tayi kyau kamar ba itaba.
Bayan an gama gaisawa BB,ya mik'e yana fad'in
"MAMA zanje wani guri na dawo,sai zuwa dare zamu koma in Allah ya kaimu..."
Fatan alkhairi tayi masa,k'asa-k-asa yake kallon KHUBRA data wani mak'ale jikin MAMA ita kuma sai biye mata take ita ga mai y'a,har ya kai k'ofar palour yajiyo BABA ZUWAIRA nawa KHUBRA fad'an ta tashi taje suyi sallama,fuska ta kumbura kafin ta tashi ta biyo shi,har bakin mota ta rakashi yana gaba tana binsa a baya,kamar abun arziki ya bud'e motan ya shiga,ita kuma tana tsaye dafe da k'ofar ya d'ago ya kalleta ganin fuskarta a cukune yasa ya furta
"Zo nan..."
Babu musu ta zagaya ta d'ayan side en ta zauna tana kallon waje
"Wato rakiyan ne bakya so shi ne kike wannan abun ko..?

"Nifa ba haka bane..."


"To yaya ne..?"


"Babu komaifa..."
Ta sake bashi amsa kuma har lokacin bata saki fuskar ba,juyo da ita yayi fuskarsu na kallon juna ta yanda suke iya jin numfashin junansu na sauka kan fuskokinsu
"JODI nine baza ki iya rakowa ba sai an ce ki rakani...?"
Kai ta girgiza idanunta a k'asa
"Me yasa to kika b'ata fuskanki dan ance ki rakoni...? ko dan bakya so ne shi yasa..?"
Nanma girgiza masa kai ta sakeyi
"To mene ne..?"
Shiru tayi shima shirun yayi ya jingina bayansa a jikin kujeran kallonta yaci gaba dayi,ba tare da ya mata maganaba,itama taci gaba da zama kanta a k'asa ta kasa magana.
Sun jima zaune babu wanda yayiwa wani magana,shi kuma BB zuba mata ido yayi yaga iya gudun ruwanta,gajiya yayi da shirun ya fara magana fuska babu wani wadataccen fara'a
"Wato baki san kinyi laifiba ko...?"


Idanunta ne sukayi rau-rau za tayi kuka,kansa ya d'auke daga kallon da yake mata cikin muryar kuka ta furta
"Kayi hak'uri YAYANAH dan Allah.."
Dai² lokacin hawayen suka sakko kan fuskarta,kasa jurewa yayi da sauri ya furta
"It's ok...!"
Yana janta jikinsa yana patting bayanta,ajiyan zuciya ta sauke tana dad'a kwanciya jikinsa,sai daya tabbatar ya sanyata dariya sannan ya mata sallama akan sai anjiman idan ya dawo zasu tafi,cike da farin ciki ta juya suna waving wa junansu.


Har dare tana gidan kowa sai nan-nan yake da ita musamman MAMA da FATAHIYYA,a nan su ABBA suka tarar da ita lokacin da suka dawo,sosai sunyi farin cikin ganinsu hankalinsu a kwance.
A wannan lokacin ba kowa ne zai kalli ABBA'N KHUBRA ya shaida shiba,ashe dama wahala da zaman k'auye sukasa ya fara tsofewa,cikin y'an watanni har ya soma yin shar da shi,da yake Allah yayi shi mai tsafta shi yasa cikin lokaci kad'an ya dad'a gogewa musamman kuma daya had'u dasu ABBA mutanen da suka yi gogayya da turawa,yadda suke tafiyar da harkokin kasuwancinsu yanzun idan ba wanda ya san suba ba zai tab'a tunanin ba jini d'aya bane su en,dan mutane da dama suna musu kallon y'an uwan juna.
Daf da zasu tafi KHUBRA ta matsa kusa da ABBA'NTA tana masa magana,cike da sha'awar ganin yadda y'ar tasa ta koma ya kalleta yana maida hankalinsa kanta dan ya fuskanci me zata fad'a,kamar abun arziki suka dad'a gaisawa yana tsokanarta,sai dariya take shi kuma hakan shi yasa shi yake sake jin dad'i sosai
"ABBA dama fa akwai maganar da nake ta son maka.."
Kallonta ya sake yi yana fad'in
"To y'ar albarka ina sauraronki"
Sai da tayi ajiyan zuciya sannan kuma kanta a k'asa tace
"ABBA dama ba kan komai bane sai wani al'amari da nake ganin idan hakan ya kasance kowa zaiyi farin ciki..."


Dad'a d'aure masa kai tayi saboda har lokacin bata fad'i abunda zata fad'a enba,muryarta ta katse shi daga sonyin magana
"ABBA damafa shawara ne nazo da shi,nace me zai hana ka yarda da BABA ZUWAIRA a matsayin mata,kaga itama dama bata da aure mijinta ya jima da rasuwa,kuma ABBA na baku labarin yadda ta rik'eni na tabbata bata da wata matsala...Kuma kaima yanzun ABBA baka da kowa sai ni kad'ai..."
Dakatar da ita yayi fuska a had'e yake fad'in
"Maganar dama da kika zo da ita kenan saboda futsara irintaku ta y'ay'an zamani har ni kikewa maganar nayi aure...?"
Yadda taga ya b'ata rai ya kuma zage yana ta mata fad'a yasa ta shiga bashi hak'uri,amma kam bata ji dad'iba daya k'i amincewa,haka sukayi sallama da mutanen gidan da suka rakosu har bakin mota kafin suyi musu sallama suka d'auki hanya.


Cikin motan shiru babu mai magana kanta a k'asa tana matse hawayen dake sauka kan fuskarta,maganar BB ya dakatar da kukan nata
"Me kika yiwa ABBA yayi miki fad'a....kin b'ata masa rai ko...?"


Sai da ta gama kukanta ba tare data kula shiba,shi kuma sai nasiha yake mata yana nusar sa ita hanyar da zatabi su zauna lafiya da ABBA,sai da ta bari sunje gida har sunyi wanka sun kwanta sannan ta bashi labarin abunda ya had'asu,ajiyar zuciya yayi kafin ya nuna mata illar abunda tayi,sai yanzun ta fahimci laifinta dan kam tabbas ba ita ya kamata tayi masa maganar ba.Tun daga lokacin ta k'udurce a ranta duk hanyan da zata bi sai ta bi na ganin hak'anta ya cimma ruwa kuma zata dage da addu'ah akan Allah ya tabbatar da alkhairinsa................
_Wannan kenan.._








*COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃










*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*














*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠







*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com


*©®2018*
*6/ɑմցմՏԵ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*
_cwєєt ѕíѕ *HALIMATUS-SADIYA MUHAMMAD (LEEMA)* ínα tαчαkí murnα dα fαrín cíkí nα gαmα wαnnαn nσvєl mαí cíkє dα d'umвín dαruѕѕα nα *IYA KU'DINKA* αllαh чα ѕα ѕαk'σnkí чα íѕα índα kíkє вuk'αtα αllαh чαѕα mutαnє ѕuчí αmfαní dα d'umвín вαѕírαrkí dα kíkα zuвє α cíkí dα ílímí dαkє cíkín lαвαrín..uвαngíjí чα k'αrα lαfíчα dα níѕαn kwαnα mαí αmfαní._ *#1 ♥ cwєєt lєєmαtєєч.* 😍
*~___________________________~*


*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










6⃣0⃣










*K* imanin kwanaki biyu kenan da zuwansu gida,yauma yana zaune cikin parlour a lokacin KHUBRA na saman jikinsa kamar kowane lokaci da idan kaje zaka tarar dasu a hakan.Cike da so da kulawa ya kalleta yana fad'in
"JODI yanzun idan aka ce kizo a kaiki makaranta shin kina so ko kuwa...?"
Kallonsa tayi tana murmushi ba tare data ce komaiba,saima hannunta datake ci gaba da wasa da shi a jikinsa,ganin bata da niyyan magana yasa ya rik'e hannunta yana kuma kallon ta,a hankali ta d'aga kanta ta kalleshi tana murmushi
"Shi ne kina ji ina miki magana bara ki amsaba...? kin san dai bana son haka ko...?"
K'ure shi tayi da ido tana nazarin fuskarsa,ganin yanda yayi yasa ta d'an gyara kwanciyanta tana fad'in
"Ni kam YAYANAH wani karatu ne zanyi yanzun...? ina ganin bani da wannan daman dan kam lokacina ya riga da ya wuce,wanda nake da shima na addini ya isarmin,amma kam nayi girma da zuwa makaranta yanzun.."
Shiru yayi yana nazarin maganarta,lallaima yarinyar nan idan ba shirme irin nata ba,har wane girma ne za ace tayi yanzun da karatun,shi kam tabbas yana da burin ganinta tayi karatu,shirun da taji yayi babu magana yasa ta sake d'agowa tana fad'in
"YAYANAH waima me ya kawo wannan maganar ne kam yanzun...?"


Idanunsu sark'e cikin na juna yake fad'in
"Wato kefa a ganinki nan kinyi girma da zuwa makaranta ko...?"
Kai ta d'aga masa alamar eh,kuma har cikin zuciyarta take nufin hakan,d'an murmushi tayi kafin ta furta
"To waima YAYANAH kawai sai na wani tafi na zauna haka nan gemai-gemai dani nace naje koyan karatu ko me..?"
Da sauri ya katseta ta

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads