Showing 42001 words to 45000 words out of 159513 words
Chapter 15 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt
rud'e ta k'arasa kusa da shi fuskanta duk ya gama yin kacha² da hawaye,chakumoshi tayi tana kuka take fad'in
''Sun tafi da ita dan Allah YAYA karka bari su tafi da ita''
Gaba d'aya kalamanta sun gama rud'ashi,ya rasa ganema inda ta dosa,a hankali ya shiga girgizata dan kam ya gama fuskantar a kwai matsala
''Su waye ne kam,kuma waye suka tafi da ita?''
''YAYA KHUBRA sun tafi da ita,YAYA za su cutar da ita,please karka bari su gudu da ita''
Sunan KHUBRA da ta ambata shi ya masifar d'aga masa hankali,take ko ya sake ta yayi hanyan fita daga gidan,da gudu ta biyo bayanshi,sai dai ko da ya fita babu ko da k'urar motan bare yasa ran ganin ita kanta motan,tsayawa yayi ya dafe kansa baya ga *''INNALILLAHI WA-INNA ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNIY FIY MUSIBATIY WA-AKLIFNIY KHAIRAN MINHA''* babu abunda yake fitowa daga bakinsa sai wannan,wani sabon yanayi ya tsinci kansa a ciki,sam ya kasa magana fuskarsa lokaci guda har ta sauya kammani....
ZUHRA dake tsaye kusa da shi ko har yanzun banda gunjin kuka babu abunda take,kallonta kad'ai ya iya yi,kusa da ita ya matso yana son tambayanta sai dai kalmomin sun mak'ale a iya mak'oshinsa.....
Matsawa yaga ZUHRA na yi har dai² gurin da motan su BIGGY ta bari,takalman KHUBRA ta d'ebo wanda garin kokawar sata a motan suka watse a kasa,rik'esu tayi k'am ta rungume tana ta faman kuka,gwanin tausayi haka take kukan babu mai rarrashi....
Kusa da ita ya dawo hannayensa yasa akan sholders enta
''Pleasee!ya isa haka sisnah waye ya sa ku fito a daren nan?''
''MAMA ce ta aikomu''
Katseta yayi dan ko sunan kad'ai da ta ambata sai da gabansa yayi mugun fad'uwa,a zuciyarsa ya furta
''Ko me ya sameki tabbas da sa hannun MAMA a ciki,amma me yasa za ta aikata mata haka?",rashin amsa ya sashi dakatar sa tunanin,dan ko ba lokacin tunani bane,gefe suka sake komawa cikin low voice yake mata magana,ammafa hankalinsa baya tare da shi
''SIS abunda nake so dake ki dena kukan nan haka,kuma koda mun koma gida kada ki nuna damuwa kan abunda ya faru,har sai mun gano gaskiyar wanda ya aikata hakan''
''YAYA ai babu wanda ya aikata komai face MAMA''
Duk da ya sani da sauri ya dakatar da ita
''A'a SIS ba a saurin yanke hukunci,mu jira mu gama bincike tukun kin ji ko?''
Kai ta kad'a masa,hannunta ya ja suka kama hanyar komawa cikin gidan suna tafe yana bata baki kan kada ta kuskura ta nuna damuwa ko da anzo ana maganar a ganta....
A hanyan suka rabu shi ya nufi corridor da zai sada shi da bedroom ensa,suna tafe kowa zuciya babu dad'i kamar majinyata haka kowa ya shiga bed room ensa.....
Daren ranar kam a b'angaren ZUHRA da BB babu wanda ya iya cikakken bacci,gani suke kamar an had'e musu darare arba'in dan ko har fatan wayewar gari suke.....
《《》》
Tun bayan barinsu line en basu tsaya ko inaba sai k'auyen ZAKIRAI dake cikin garin kanon dabo,da yake dare ya soma yi sosai kuma suna son komawa dan ko hanya suke shirin d'auka zuwa garin kaduna,dai² kasuwarsu dake gefen hanya suka perker,sai da suka duba suka tabbatar babu kowa da yake ganinsu kafin suka kinkimota daga cikin motan,k'asan wata rumfa suka shimfid'eta tare da sanya mata ledan da ta fito da ita a tsakanin hannayenta,juyawa suka yi da mugun gudu suka bar gurin,yayinda KHUBRA ke baccinta peacefully,ko sanin inda kanta yake bata yi ba.....
Sai da gari ya gama haske mutane nata hada-hadar kasuwanci sannan ta farka,nan ta shiga k'arewa ko ina kallo,can ta kalli kanta sai a lokacin ta iya tuna abunda ya faru da ita a jiya da dare,take ko wasu zafafan hawaye masu k'una suka shiga sakko mata,ta jima tana kuka uwa baza ta dena ba,da k'yar ta mik'e ta nausa cikin kasuwar k'afarta ko takalmi babu,ita dai har yanzun tana rungume da wannan ledar.....
Yunwa ce ta fara damunta take ko ta sake sakin wani sabon kukan,tuna yadda rayuwarta ke garawa bisa doron K'ADDARA,zuciyarta fal addu'ah ta neman agaji daga mahaliccin sammai da k'assai,a hankali ta ware ledan dan duba abunda ke ciki dan kam ita tunanin yasarwa take,kud'i tayi arba da shi y'an one thousand sababbi,take ko tayiwa Allah godiya....
Guda ta zaro ta shiga bulayin neman abunda za ta karya,mai k'osai kad'ai ta samu aiko take ta tsaya sai dai gurin akwai yalwar mutane dake faman bin layi....
Kallo ne ya koma sama (wai akace shaho ya d'auko giwa) duk inda ta gifta sai dai kaga idanun mutane a kanta,bama kamar gurin mai k'osan da take tsaye uwa wacce aka dasa,har lokacin k'afafunta babu takalmi,tana nan tsaye har layi ya zo kanta mik'a kud'in tayi tana jiran a bata ba tare da ta fad'i adadin na yanda za a bata ba,kanta a k'asa ta kasa kallon kowa zuciyarta ko tarin k'unci ne a cikinta bama kamar yadda take fama da tunanin ZUHRA sahibarta,k'awarta,take ko wasu sabbin hawayen suka sake sakko mata....
Mai k'osai tana tambayarta amma sam bata sanma me take yiba,ganin haka yasa kawai ta auna mata,kafin tasa aka tab'ata,a d'an tsorace ta d'ago hannu tasa ta amsa tare da juyawa za ta bar gurin,chanjin da ta juyo da niyyar bata taga har ta yi gaba da sauri tasa wani yaro ya bi bayanta,d'an murmushi ta masa duk da tarin k'uncin dake cunkushe a zuciyarta ta amsa wash hawayen na dad'a sakko mata taci gaba da tafiya....
K'asan wata bishiya ta zauna jama'a nata kallonta amma sam hakan bai wani d'aga mata hankali ba,sai da ta tabbatar ta k'oshi kafin tunanin neman mafita ya fad'o mata....
''Ina ya kamata na dosa ni da ba ko ina na sani ba?''
Babu inda ta sani bare ta ce ga hanyar gidansu,ko da canma ba fita take ba bare daga baya da ta dawo wani gari na daban,tana zaune ta had'a kai da gwuiwa tana tunani,wani mai kuran ruwa ya d'an tsaya a kanta
''Yarinya sannu ko''
Kallonsa kad'ai ta iya ba tare da ta iya magana ba,kamar mai nazarin wani abu take kallon gurin da take zuwa wani lokaci kuma ta sake kallon mutumin ji tayi ta aminta da shi take kuwa ta bud'e baki da niyyar yin magana.......
《《》》
Haka gari ya waye musu babu wanda yayi isashshen bacci idanunsu a soye,kasa fitowa suka yi su duka biyu....
Lokacin break yayi y'ay'an HAJIYA suka fito da niyyan break,sai dai suna zuwa suka tarar da gurin wayam babu komai,kowa sai tura baki yake gaba uwa shantu,suka nufi d'akin MAMA da niyyar yi mata k'orafi....
''MAMA kinga fa ba a had'a break ba har yanzun''
Abunda ya fito daga bakin FATAHIYYA kenan da take kan gaba gurin shiga d'akin
K'wak'walwar MAMA ta tafi yajin aikin ina kuma KHUBRAN ta shiga (ni da nake gefe nace kajimin y'ar cin).........
Ta jima d'age da kai tana tunani,kafin ta soma tunanin me ya faru da ta aiketa jiya?
''Kuyi hak'uri kunji,maza kuje ku sha ko tea ne kafin na fito''
Fita suka yi suna tura mata baki,sai k'unk'uni suke,suka nufi dinning area,flask en suka kinkimo a tunaninsu a kwai wani abu cikinsa nan ko suka tarar da shi wayam shima,kuka kad'ai su HANEEF suka sa,wanda sanadin haka yasa BB fitowa fuskarsa uwa wanda bai tab'a dariya ba,wani kallo ya watso musu wanda yasa suka shiga hankalinsu ba tare da ya furta komai ba...
Cikin parlor ya kwanta idanunsa a rufe jijiyoyin kansa sun gama bayyana a fili,shi kad'ai yasan abunda yake ji a zuciyarsa,yanzun kam ko magana baya jin zai iya yi
''To amma ai bai kamata na ci gaba da zama ba yanzun,,,,,,,,me ya kamata nayi?''
Yayiwa kansa tambayar,saurin mik'ewa yayi ya koma bed room ensa,cikin abunda bai fi mintuna biyar ba ya fice daga gidan gaba d'aya.....
ZUHRA kam kasa fitowa ma tayi tana d'akinta,kuka take sosai tamkar wacce uwarta ta mutu,idanunta duk sun kumbure sun canja launi kan kukan da tayi,sai da ta ji cikinta tamkar babu komai ta fito da k'yar tana tafe tana bin bango har ta shiga kitchen...
Kallonta suka yi ganin yadda take bin bango,da ka suka tambayi juna sai dai babu amsa...
Kitchen ta shiga kallon gurin da KHUBRA ta saba tsaiwa tana aiki ta shiga yi,take wasu hawayen suka k'ara b'alle mata ganin babu KHUBRA cikin gurin da suka saba zama tare,sai da tayi kukan mai isarta da k'yar kuma ta iya dafa indomie a plate ta juye ta d'auka tayi bed room enta.....
Kallonta suka sake yi,coz tun tana cikin kitchen en suke jiyo k'amshi na tashi,gaba d'aya sun rashe suna jiran ta gama ta basu,aiko tana barin gurin suka shiga da sauri suna dubawa...
Wayam babu komai ciki haka suka janyo tsummokaran k'afafunsu suka fito,guiwoyinsu a sake....
《《》》
Fitarsu daga d'akin ta sauke wani gwauron numfashi,wayarta ta janyo ta shiga kiran HAJIYA LAURA...
Bata wani jima tana ringing ba ta d'auka cike da izza da k'asaita kamar d'iyar sarauta....
''Aiki yayi kyau mutuniyata,yanzun kam yaranmu sai yanda mukayi da su''...
''Ban fuskanci me kike nufi ba''
HAJIYA MURJA ta tambaya cike da zak'uwa da son jin labarin...
Take ko ta zayyane mata sawa tayi aka d'auke KHUBRAN daga garin,ta k'arashe zancen da fad'in
''Nasan yanzu kam tayi nisa da mu''
Wata dariya ta saki ta makiran mutane....
Sai lokacin hankalin HAJIYA MURJA ya kwanta tana fad'in
''Mun rabu da alak'ak'ai,jarababbiya aje can a k'arata''....
Tana sakin dariya itama,sun jima suna shirya makircinsu kafin suka yi sallama....
*_~TEAM KHUBRA~_*
*_REAL SMASHER._*🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*14/ʍɑվ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~________________________~*
_Ga masu buk'atar son kasancewa da group na *Y'AR GARUWA* za ku iya yin joining ta hanyar amfani da wannan link en,saboda gujewa had'uwa da maza,mata zallah dan Allah👏..._
👇
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/EvdAvnFbBaX2BBMAwCCH4E
*~________________________~*
🍟🍟🍟🍟🍟
🎂 *HAPPY BORN DAY*🎂
_OUR SURIKI *HASSAN ATK*_
🎊
🎉🎉🎉
_A birthday is just the first day of another 365-day journey around the sun. Enjoy the trip. *HAPPY BIRTHDAY*_
🍻🍻🍻
🎂🎂🎂
*ONCE AGAIN..HAPPY BIRTHDAY*
H A
A
S T
S
A K
N
💃💃💃💃💃
*~________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*2⃣7⃣*
*G*idansu KHALEEL ya yanke shawarar zuwa danko baya tunanin a yanzun yasan abunda ya kamata ya aikata...
Driving kawai yake ba dan yana da nutsuwar da zai iya kai kansaba,ikon Allah ne kad'ai ya kaishi,idanunsa sun koma jaa yayin da ta tsakiya har wani layi² yayi na coffee....
Shigansa harabar gidan bayan yayi parking ya nufi hanyan parlor,ta balcony ya hangosa zai shiga parlor,da yake KHALEEL ba mutum ne mai rik'o ba,shi kamar UMMIN sa yake,suna da sanyin hali...
''MAN!''.......
Ya fad'a da d'an k'arfi ta yadda BB en yajiyo shi,d'an waiwayawa yayi ya kalli gurin da yaji maganar,inda yake ya nufa fuskarsa babu annuri a tare da ita...
Chairs en da ke gurin ya zauna yana mik'a masa hannu,duk wani motsinsa idanun KHALEEL na kansa,ganin yadda ya chanja ya koma wani silent duk da dama bai da yawan magana...
''MAN lafiya kake kuwa?"
Kallonsa kawai yayi da rinannun idanunsa...
Sam KHALEEL bai kula da yadda idanunsa suke ba,sai yanzun da ya d'ago...
Cikin tashin hankali KHALEEL ke tambayar BB
''MAN dan Allah ka fad'amin abunda ke faruwa,kaga kuwa yadda ka koma wani abun tsoro.......Dan Allah ka sanarmin abunda yake faruwa,ni kaina hankalina ya gaza kwanciya''
Hawayen da suka fara sauka kan fuskar BB masu matuk'ar k'una su suka dad'a sawa hankalin KHALEEL ya kai mak'ura wajen tashi,zuba masa ido kawai KHALEEL yayi,sai dai sam shi kansa hankalinsa baya tare da shi,ga shi BB en ya kasa masa magana bare ya gano dalilin damuwar tasa.....
《《》》
''Dan Allah d'an uwa nan a ina nake?''
Kallonta yayi yadda take magana baiyi tunanin irin yaren da zai fito daga bakinta ba kenan,daurewa yayi ya bata amsa,yayin da yake k'are mata kallo from head to toe,hawaye ne suka sake b'alle mata,nan ko yaci gaba da kallon ikon Allah,shi dai bai san dalilin kukan ba bare ya bata baki tayi shiru,haka ya ci gaba da kallon ikon Allah har sai da tayi mai isarta sannan tayi shiru....
Tsab'an kukan da tayi muryanta har ya shige cike baka jin sautin muryanta idan tana magana har sai ka kalli yadda lips enta ke motsi....
Tunanin inda ya kamata ta nufa yanzun take,nan zuciyoyinta suka shiga fafatawa gurin ganin sun bata shawara...
''Shin gidanmu ya kamata na nufa ko kuwa?''
Take wata zuciyar ta sake bata shawaran
''A'a kawai ki koma gidan BABA MA'U''
Ta yi zurfi cikin tunaninta,har lokacin kuma ta kasa samun matsaya guda d'aya,duka kuma ta kasa yin na'am da shawarwarin da zuciyoyintan ke bata...
Tana zaune tana ta kallon jama'a dake ta faman hada-hadar kasuwancinsu,yayin da yara suka sata gaba da ihun ga balarabiya,wasu suce y'ar india ce,da k'yar wanan mutumin ya kore su suka bar gurin....
''Dan Allah MALAM a ina zan samu motan da zai kaini''......
Sai kuma ta d'an karkatar da kai gefe alamar tunani....
《《》》
''A kwai matsala MAN,ban san ya zan billowa al'amarin ba''
Shiru ya d'an yi ya kasa ci gaba da magana sai iska da yake furzarwa,wacce take fitowa cike da hucin zafi..
''Wace irin matsala ne wannan?ni kam duk ka d'agamin hankali,kai kana cikin damuwa,nima ina cikin damuwa.....Buh...Ka k'i sanarmin abunda yake faruwa''....
''Sun sa...ce......ta''
Abunda ya iya furtawa kenan,ko shima sai da yayi kokawa da kalmomin kafin suka bayyana,ta yadda za a gane....
Ido KHALEEL ya fiddo waje
''Wa aka sace? ZUHRA?ko wa???''
Kai ya shiga kad'awa cike da takaici baya ga k'uncin da yake ziyartarsa,zuciyarsa ta gama yin duhu,a iya wannan lokaci baya gane komai.....
''Uhmm!ita suka sace''
Ya sake maimaitawa,shikam KHALEEL ya kasa fuskantar wa ake nufi
''Dan Allah kamin bayanin da zan gane sosai.....Wace ce aka sace?.......Na tambayeka ZUHRA ka ce a'a,wace to daga cikin y'an gidan''
A tak'aice ya furta
''Wannan YARINYAR''
Fad'in hakan da yayi shi yasa ya fuskanci inda zancen ya dosa,take ko ya mik'e tsaye yana maimaita
''HASBUNALLAHU WA-NI'IMAL WAKEEL!!''
Da k'yar ya iya samun guri ya zauna,sun d'auki tsawon lokaci babu wanda ya iya magana cikinsu......
Ransa a b'ace yake fad'in
''Tabbas duk wanda yayi wannan d'anyan aikin,wallahi imaninsa ragagge ne,sam basu da tausayi bare imani....Laifin me ta aikata musu da zasu aikata mata wannan d'anyen hukuncin.....Baiwar Allah babu ruwanta......Wanda duk yake da hannu kan wannan aikin ya cancanci hukunci mai tsaurii''
BB kam ya kasa magana,har KHALEEL ya gama surutansa baibi ta kansa ba,tunani yake sonyi amma sam k'wak'walwarsa ta k'i karb'an ko wane irin hayaniya...
Kafad'ansa ya kalla jin an dafa shi,hannun KHALEEL yabi da kallo,lokaci guda shi kansa KHALEEL en har ya sauya kamanni...
''MAN tashi muje''
''Ina kuma zamu?''
Da k'yar BB ke tambaya
''MALAM kawai ka tashi muje,wannan lokacin bana tunani bane bare b'atawa''
Ganin BB en yak'i motsi yasa KHALEEL bugun shoulder ensa yana fad'in
''Ka tashi mu wuce''
K'in tashi yayi,wanda hakan da yayi ya k'ara fusata KHALEEL en
''Kada Allah ya sa ka taso en,wannan damuwar da kake nunawa duk na banza ne''...
Bai samu daman k'arasawa ba saboda wani banzan kallo da BB ya wurga masa cikin matsanancin fushi ya mik'e
''Me ka sani game da al'amarina