Showing 123001 words to 126000 words out of 159513 words
Chapter 42 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt
kuma sai maganar kana son wata kake,to idan za kayi maganarka sai ka bari kayita kai kad'ai amma ka denamin ni dan ban son ji ni..."
Ta k'arasa tana ture shi,kallonta yayi yanda tayi magana yasa shi sakin murmushi wato dai maganar da yayi a zuciyarsa a fili yayita kenan.
Baya ga haka kuma mene ne dalilin daya sa ta fad'in haka,fuskarta kad'ai zaka kalla kasan ranta a b'ace yake,dan ya kauda zancen yasa ya saketa da sauri ko ta mik'e tana gyara riganta daya d'anyi squeezed ta gaba,cikin sauri ta bar gurin,shi dai kawai ya bita da kallon mamakin kalmominta.
Har ta b'ace masa sannan ya sauke idanunsa yana murmushi lallai zai sha fama,dan kam ya tabbatar za tayi bak'in kishi da ganinta.
Tunawa yayi da dalilin da yasa ta fito,gashi yanzun kuma ya koreta.Lallai ya zama dole ya kirata,sai yanzunma ya tuna da jiyafa ba wani lafiya gare taba a haka kuma suka kwana,amma yau ji yanda tayi masa kamar ba itaba,bedroom en nata ya nufa,nan ya hangota kwance ta juya baya,FATAHIYYA nata fama da waya a hannu,ganin shigowansa yasa ta tab'ota da sauri ta juyo tana kallonta,ganinsa cikin d'akin tayi saurin kauda kanta daga gurin
"Kin taso kinyi break ko kuwa sai na maimaita miki warning da na miki..."
Banza tayi da shi ita ko FATAHIYYA da sauri ta fice a d'akin,ganin tak'i kula shi yasa ya k'araso inda take cike da isa ya d'agota,sai da ya tsaidata a kan k'afafunta sannan ya furta
"Oyaaah! muje muyi break sai na baki labarin abunda kike son sani..."
"Na k'oshi ni..."
"Da kika ci mene zaki fad'i haka...Maza wuce muje kafin na sab'a miki.."
Bakinta ta kyab'e za tayi masa tab'ara,bai tsaya sauraronta ba ya kama hannunta suka fice..
Har suka kammala break fast bata sake kula shiba,shi ko duk spoon d'aya da zai kai bakinsa sai ya kalleta yayi murmushi,a haka har suka kammala,ita ta fara ture plate nata tana yamutsa face,yana kallonta bai ce komai ba har ya kammala,tattara kayan tayi sannan tayi kitchen shi kuma ya koma cikin parlor,da sauri FATAHIYYA ta tadda ita a kichen amsan kayan tayi taba fad'in
"Haba AUNTYNAH ina nan kuma wane aiki za kiyi,kije ki huta bari na wanke kayan..."
Murmushi kawai tayi tana mamakin halayen FATAHIYYA a yanzun kamar ba ita ce mai d'an banzan jin kannanba a da,da sauri kuma ta juya zuwa parlor.
Tsaye ta same shi yana dad'a gyara cap nasa,tab'e baki ta sake yi da sauri kuma ta rufe bakin saboda tuna abunda yace d'azun tana kuma kallonsa,juyowa yayi yana kallonta dai² tana shirin zama cikin cuition.
"Ammm! zan fita ga FATAHIYYA nan ku zauna tare zanje gida na dawo ba jimawa zanyi ba kinji...?"
Kallonsa tayi tana mik'ewa tsaye
"YAYA nima zani kaji....kaga jiya dama banga ZUHRA ba yanzun sai ka kaini gurinta..."
Dariyar rainin wayo yayi kafin ya rik'o hannunta ya zaunar
"Haba BABY waye ya fad'a miki amarya tana zuwa gida a irin wannan ranar..? kiyi zamanki nima ba dad'ewa zanyiba kinji...?"
Baki ta kyab'e za tayi kuka,shi dariyama take bashi duk wani abu na yara ta iya
"Noo! kada kiyi kuka kinji yanzun zan dawo,barima nayi sauri naje ina son mu had'u da KHALEEL ne kinji...?"
Kai ta kad'a masa tana cuno baki,sakinta yayi da sauri kuma ya fice dan ya tabbatar idan ya biye mata to ko babu inda za shi,yana fita harabar gidan ya daidaita tafiyansa daga saurin da yake yi,KHALEEL ya kira yana fad'in
"MALAM ai sai kazo ka d'auke ni ko,tunda kunmin auren dole kuma name ne na wani yimin wulak'anci bayan kuma na karb'i matar da kuka had'a baki kuka auramin...?"
KHALEEL dake driven jin abunda BB ya fad'a yasa shi sakin baki da mamaki shimfid'e saman fuskarsa ya kashe wayan,sai da ya zo bakin get sannan ya kirashi,yana d'auka ya furta
"Idan kaga dama ka iya fitowa mu wuce ko...?"
Daga haka ko bai bashi damar yin magana ba ya kashe,bakin get en ya fito yana ganin motan babu magana ya bud'e ya shiga ba tare da ya kula shiba ya rufe k'ofan yana gintse fuska shi a dole ga wanda akama auren da baya so.Kallonsa KHALEEL yayi ya d'auke kai kamar ana fisgar maganar daga bakinsa ya furta
"MR pretender ka gama yanzun....?"
Kallon sa yayi cike da son tambayansa,gane hakan da KHALEEL yayi yasa ya furta
"Ciwon SO mana...ba shi ya kwantar da kaiba ne...? ko an fad'a maka bamu san halin da kake ciki bane..?"
"Allah ya sawak'e ciwon so kuma kamar wani mara abun yi zan kwanta ciwo kuma a hakama wai na so.."
Dariya sosai KHALEEL yayi
"Ehh! lallaifa ka samu lafiya tunda ka samu ABINDA RANKA KE SO ai dole kayi wannan maganar..Amma tunda hakane yanzun muje gurinsu ABBA kaga tunda baka son auren sai a warware tun tafiya bata yi nisa ba ko....?"
Yamutsa fuska BB yayi sannan ya furta
"Ka makara kuma ai dan ni a tsarina babu saki...Kuma ko bayan hakama ni yanzun ai na riga da na karb'a tunda babu yadda zanyi,ko ba haka nace maka ba...So no need kuma ace za a warware zanyi taimako..?"
"Kutt!!! wai K'anwar tawa kake cewa zaka taimakawa...?"
"Yeahhh! Itanfa.."
"Haba MAN kaima da kanka kasan ta wuce haka wollahi kai dai kawai ta taimaka maka dan karka mace akan so,kama rufawa kanka asiri kayi shiru haka nan,dan kana ci gaba da magana zan nad'e komai na sanar mata,sannan kuma zan bata shawaran ta baka wahala ne ko me kazo da shi kada ta yarda..."
Dariya sosai sukayi daga haka kuma BB ya canja musu firan..Haka har suka iso gidan iyayen nasu.
Gidan a cike da jama'a y'an biki da basu k'arasa tafiya ba,bayan sun gama gaisawa da su,suka wuce babban parlor inda su ABBA suke tattaunawa da su OLD KHALEED da kuma KAKA da k'afarsa tayi kyau kamar ba shi yayi muguwar jinya ba..
Kowa yaga BB sai yayi dariya a cikinsu,shi dai kam bai iya cewa komaiba har sukayi shirin ficewa bayan sun gama gaishe-gaishen suka kama hanyan komawa gida,a hanya ne BB ya kalli KHALEEL yana fad'in
"MAN nifa har yanzun ka sani a duhu wallahi kuma kak'i warwaremin yadda wannan al'amarin ya faru.."
'Dan murmushi yayi kafin yayi parking gefen hanya ya furta
"Zaka iya tuna wata rana da muka je gurin UMMI akan maganar auren KHUBRA da nake sonyi a wancan lokacin...?"
Kallonsa kawai BB yayi ya girgiza masa kai
"Baka tuna ba ko..?"
Nanma kai ya sake d'aga masa
"Toh! idan baka mantaba kamar yadda na fara fad'a maka yanzun tun a wannan ranar dana jema da UMMI maganar wacce mukayi a gaban idonka,yanayin yadda kabar gidan shi ya bamu tsoro,a take UMMI tasa nabi bayanka amma ina fitowa na tarar har ka shiga mota wanda a k'ok'arinka na yin reverse har ka daki round about amma ko kulawa baka yi ba,in tak'ai ce maka zance har biyoka nayi a baya,sai da na tabbatar da ka isa gida lafiya sannan na koma,a nan na shaidawa UMMI duk abunda ya faru...Kasan abun da ya bani mamaki a lokacin?
Bud'ar bakin UMMI bata furta komaiba sai cewa tayi KISHI ke damunka kuma ba kan komaiba ne sai kan wannan maganar da nayi mata,tun daga lokacin UMMI tayi ta bani baki akan nayi hak'uri da maganar KHUBRA,da tarin shawarwarin da take bani yasa na mata alk'awarin na janye neman auren,sai dai kuma abunda yasa bamu nuna a fili ba shi ne ganin yadda a fili kake nuna halin ko in kula da lamarin yarinyar bayan kuma a gefe kana fama da dakon soyayyarta,wannan dalilin yasa muka shirya maka wannan drama daka gani.
A ranar d'aurin aurema nasan zaka ce to kuma me yasa aka fara sanar da d'aurin aure da sunana ko? to gaskiya wannan kuma ba daga mu bane daga mai sanarwar ne dan dama a yadda muka shirya mun barshi a kan sai a gurin d'aurin aure za kaji komai...
Mistake en da aka samu yasa ka bar gurin ba tare da ka tsaya kaji d'aurin auren ba,wanda yanayin da na tarar da kai bayan gama d'aurin auren yasa nayi niyyan sanar maka da duk wani shirin da muka yi maka,sai dai kak'i saurarona,dalili kenan daya sa al'amura suka zo a haka...ina fatan yanzun ka fahimta..."
Kallonsa kawai BB keyi fuskarsa d'auke da wasu irin expressions yama rasa me ya kamata ya sakawa da aminin nasa da shi,a hankali ya rik'o hannunsa sosai
"Ban san da wane irin kalmomi ya kamata nayi maka godiyaba,kamin abunda ba zai tab'a gogewa daga zuciyata da rayuwataba,bani da bakin da zan iya gode maka,na gode na gode sosai d'an uwana...Allah ya baka mace ta gari wacce zata kula da kai.."
Da sauri KHALEEL yana murmushi ya furta
"Tabbas ya bani sai dai fatan Allah ya bamu zuri'a ta gari..."
Sai da suka gama hiran yadda al'amura suka wakana sannan suka yi gaba,sai da ya sauke BB a gida kafin ya wuce nasa gidan.
A parlor ya tadda su suna fama da kallon wani adventure film a MBC 2,nan ya zauna shima tun shigowansa da suka amsa sallama KHUBRA ko kallonsa bata sake yiba,har after asr prayer FATAHIYYA na gidan sai wajejen 5 sannan tayi niyyan tafiya gida.
Driver'n daya kawo musu lunch shi ya dawo da dinner sannan suka tafi da FATAHIYYA,gidan yayi mata shiru babu abokiyar hira,sai BB dake kwance yana faman chat,ita dai bata da aikin daya wuce idan ta kalleshi ta tab'e baki ta kuma juya taci gaba da kallonta..Har bayan Maghreb suna a haka wajejen 10 kuwa suka sake sa wani film mai suna *DRAG ME TO HELL* film en abun tsoro musamman yadda a farkon film en inda ake marin iyayen yaron da malamar dake masa addu'a saboda yadda yake yi kamar mai iskokai,yadda aka cilloshi daga saman stairs bayan nan kuma k'asa ta bud'e wuta na ci ta ciki take kuma yaron ya nutse...
KHUBRA dake wani cuition en daban,bata san lokacin data koma kusa da BB ba,yana chat lokacin yaji mutum a kusa da shi,kallonta kad'ai yayi yaci gaba da abunda yake yi,kallonta take ci gaba da yi idan taga abun tsoro saita sake shigewa jikinsa,shi kuma yak'i kulata dan bai sanma me ake a channel enba,maganar da suke da KHALEEL ya d'auke masa hankali kan maganar makaranta da yake ganin ya kamata ace an sa KHUBRA'N.
Dai² gurin da yarinyar ta farka lokacin da wani k'waro ya shige mata hanci ta farka a bacci,har ta koma ta kwanta taji abu kusa da ita juyawan da za tayi tayi arba da wani irin halitta...Take ko suka kwala ihu tare da KHUBRA data gama cukuikuye BB,wanda ihunta yasa shi kallonta da kuma cikin parlor'n,TV en ya kalla take ya gano dalilin daya sata yin hakan,murmushi yayi yayi switching TV en,sannan ya mik'e da ita a jikinsa saboda yadda ta rik'e shi ya tabbata ba zata yadda ya kyaleta ita d'aya cikin parlor ba....
*~TEAM KHUBRA-KHALEED.~*
*_.®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
*©®2018*
*31/ʝųlყ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
5⃣6⃣
*H* anyan bedroom enta ya nufa ita dai tayi luf a jikinsa,k'wak'warran motsi ta gagara yinsa bare yasa ran zasu rabu,sai da ya tabbatar da ya zaunar da ita a saman bed sannan ya mik'e da niyyan fita,hakan KHUBRA data gani shi yasata buga wani tsalle daga inda take,aiko nan ta rik'e shi cike da son tayi kuka ta fara magana
"YAYA ina kuma zaka tafi...?"
"Bedroom nawa zan wuce mana,wani abu ne ya faru kuma..?"
Ya tambaya kamar bai san komai ba,kame-kame KHUBRA ta soma fuskarta cike da damuwa,duk wani abu da take idanunsa na kanta,shi kad'ai yake sakin murmushin mugunta,jira kad'ai yake tace ba zata iya zama nanba,ai ko take ya jiyota tana fad'in
"Dan Allah YAYA ka tsaya a nan,baran iya zama ni kad'aiba kaji...?"
Idanunta duk sunyi rau-rau wanda k'iris take jira ta fashe masa da kuka,a hankali ya fara magana
"A'a BABY ni kuma nawa d'akin waye ne zai kwana ciki...Ki kwanta kinji babu abunda zai faru,kinga jiyama na tsaya inda kike saboda na tarar dake baki jin dad'i...kinga yau kuma tunda kinji sauk'i saina tafi nawa room en ko...?"
Hakan daya fad'a shiya jawo hawaye suka fara tsere a saman fuskarta,cikin sheshshek'ar kuka take magana
"Dan Allah YAYANAH kaji kagafa ina jin tsoron wannan abun na can..."
"Haba mana BABY idan kikayi addu'ah babu abunda zai sameki kinji ko,maza je kiyi wanka ina jiranki kafin nan sai na wuce..."
"A'a wollahi ni bazan iya shigaba ni kad'ai sai dai ka rakani....Dan Allah YAYA kaji zaka kwana a nan...?"
Shiru yayi yana kallonta har lokacin kuma hawayen basu daina zubowa daga idanuntaba
"Lallai ashe haka take da d'an banzan tsoro...? in dai kuwa haka ne to tabbas babu wata wahala da zai sha gurin shawo kanta.."
Hannunsa ta dad'a k'ank'amewa jin yayi shiru bai ce komaiba while her eyes continuously shading tears,a hankali ya d'an kalli yadda ta cukuikuyeshi sannan ya d'aga mata kai yana fad'in
"Ehmmm! muje dai kiyi wanka tukuna sai muyi maganar latter.."
'Dan murmushi ta saki,da kansa ya goge mata face nata sannan yaja hannunta zuwa toilet,ko da suka shiga bayan ya rakata yana k'ok'arin fitowa nan fa KHUBRA ta kafe akan itafa lallai sai dai ya jirata nan cikin toilet,rarrashi babu irin wanda bai mata ba akan ta hak'ura ya jirata cikin room en amma ina sam tak'i amincewa
"Ni kam BABY ban san me kuma kike so nayi mikiba..Nace zan jira ki fito.."
"Ni dai gaskiya a'a idan baraka tsaya ni nanba Allah zan fasa wanka'n ma gaba d'aya.."
Cikin zuciyarsa yake fad'in "lallai na had'u da rigima,banda abunta ta ina zan iya jiranta a nan...?"
"YAYA nifa tsoro nike kada su biyoni nan..."
"To banda abunki ai canma zaki na ganina ba sai na tsaya nanba..kiyi wankanki babu abunda zai sameki ko ina nan ko bana nan.."
Yana fad'in haka ya juya zai fice,take ta doka tsalle ta mak'alk'ale shi tana sakin sabon kuka
"Allah kuwan nama fasa wankan gaba d'aya..Shi kenan dan bani da kowa sai kace zaka barni nan salon suzo su d'auke ni nima..Kuma Allah saina fad'awa ABBA su zo su maidani gida tunda haka ne..."
Sake baki yayi yana kallon sabon salon tab'aran nata,komai nata cike da yarinta take yinsa,shi kam bai san kuma ya zai mataba,amma kam tabbas bai iya jiranta cikin toilet en kome za tayi kuwa.A kaikaice ya kalleta har lokacin tana faman matse idanu,fuskarta duk ta sauya tayi ja saboda azabar kuka data sama ranta fitina.
"Haba mana duk abun bai kai nanba ta ina zaki fad'awa ABBA akan wannan d'an maganar shi ne zaki kai musu k'arana....?"
"To ba kaine kace baraka jiraniba nayi wankan.."
"Haba mana sai kace k'aramar yarinya zakiyi wanka gabana ko baki jin kunya tane...?"
"Ina ji amma wollahi baran iya zama ni kad'ai cikiba...Sai dai ka zauna ka jirani..."
"Lallai BABY kina da rigima ta ina namiji kamata zan tsaya kallonki kina wanka a gabana...Da sake wollahi 'wai an bawa mai kaza kai' idan kuma bani kike so nayi miki wankan ba to kam ya zama tilas ki kyaleni nayi waje..."
"Tabbbbb! Allah ya sawak'e ta ina zan wani tsaya k'ato da kai ka wani yimin wanka,yo to ko ina jinya ai bakamin wankaba,k'arshe kam sai dai wollahi a bari idan na samu sauk'i nayi...Gara nayita zama da datti..."
Bud'e baki yayi yana kallon yadda take zuba mishi fitsara,harda su murgud'a masa bakii,hannunta dake sak'ale da nasa ya dank'a sosai har sai da tayi y'ar k'ara
"Ba dai kin iya fitsara ba,zan gyara miki zama soon....Kin ce ko kina jinya babu maiyi miki wanka ko...?"
"Eh en to da akwai ne...?"
Murmushi ya saki ganin har lokacin bakinta yak'i mutuwa,duk da irin yadda ta rintse idanunta kan zafin rik'on da yayi mata
"Oyaahh! sake min hannu na fice wanka kuma kada kiyi,ki fito haka nan kiga yadda zanyi dake..."
"Allah baran sake maka hannu ba...sai ka jirani tukuna.."