Header Ads
Showing 153001 words to 156000 words out of 159513 words

Chapter 52 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1232

Ads at the middle of Article

sanya sunanta murmushi yayi sannan ya basu amsa da cewar
"Itace wacce nafi k'auna...Shi yasa na maida sunanta akan y'armu ta fari,kuma ko bayan haka sunan matar Manzon Allah ce ta fari (S.A.W)..."
Haka aka ci gaba da shirin hidimomin da aza gudanar a gobe na suna idan Allah ya nufa....


*RANAR SUNA...*


Tun da asuba bayan an idar da sallah aka sake jadadda sunayen yara kamar yadda suke,ABDULLAH,ABUBAKAR AS-SADDIQ sai kuma NANA KHADIJATU.
FATAHIYYA zaune ta tasa yaran a gaba dan tun da aka dawo da KHUBRA gidan UMMI itama ta dawo nan ta tare cikin shekaru biyu duk wanda ya kalleta sai yayi mamakin girman data k'ara ga class na musamman ba kamar daba da ba wani wayewa gareta ba.
Anyi taro lafiya wanda ya amsa sunan taro ba wai taron da yake na muna taroba,inda a ranar BB sai daya bawa mutane mamaki kan irin bajinta da yayi na kyaututtuka daya dinga bajewa ga abar k'aunarsa,duk kuma kan irin farin cikin data sashi a zamansu,haka taron suna ya watse da kyaututtukan da aula samu daga gurin y'an uwa da abokan arziki,haka taro ya watse inda aka bar mai jego da yaran hannun UMMI suna sake karb'ar gyara da kulawa....




Agogo juyi yake inda a kowane motsawar second sai kaga ci gaba ta wani bigire na daban a rayuwa,cikin kwanaki arba'in da haihuwar KHUBRA yara sun dad'a wayo musamman mazan da dama tun a haihuwarsu sunfi LITTLE KHUBRA girma.


Tun da safe a ranar kwana na arba'in en ne,BB ya kafa ya tsare a gidan UMMI jira kawai yake UMMI ta bashi approval na tafiya da iyalinsa,tun data ganshi tasan abunda yake nufi,nan ko ta had'e girar sama dana k'asa ta kuma k'i ce masa komai,tun safe har dare yana nan,ganin babu magana makamanciyar ya d'aukesu su tafi yasa ya bawa kansa hak'uri,kallon agogo yayi yaga yadda dare yayi cikin sanyi murya yace
"UMMI zan tafi..."


Bud'ar bakin UMMI tace masa
"To ka gaida gida ko..."


Shiru yayi kansa a k'asa ya rasa me zai ce mata,ita kuma tana kallonsa duk abunda yake sai dai bata k'ara maganaba daga haka,kamar zaiyi magana kuma sai ya fasa,cikin sanyin jiki ya mik'e ya mata sallama fuskarsa cike da damuwa ya tasamma hanyar fita daga parlour'n,har ya isa bakin k'ofa sai kuma ya bata tausayi tasan dai ita da kanta yayi hak'uri tunda bai tab'a tambayarta akan zai tafi da ita ko makamancin hakaba,dakatar dashi tayi tana kiransa,dawowa yayi kansa a k'asa dan ji yake kamar yayita kurma mata ihu ko Allah zaisa ta bashi matarsa,hak'uri kam yayi shi har yana neman ya gagare shi.


"Zauna nan...Ina zuwa.."


Abunda ta fad'a kenan ta mik'e ta shige ciki,y'an mintuna da basu haura talatinba ta fito rik'e da hannun KHUBRA data sha ado cikin wani rantsatstsen less mai kalar sea green sai yarfan duwatsu kalar gold,tana ta fana shek'a k'amshi,fuskarta tasha light make-up tana zuba murmushi ta cikin mayafinta daya rufe mata fuska,dan dama a ranar kam tun da yazo UMMI bata bari ya ganta ba,sai dai y'ay'ansa da yaketa faman yiwa wasa,idan ya d'auki wannan ya ajiye ya d'auka wannan,sai dai da gani kasan LITTLE KHUBRA ta musamman ce a gurinsa...
Fuskarta a lullub'e da mayafinta kalar duwatsun kayanta da plat shoe a k'afarta,a hankali har suka iso gabansa,idanunsa tun da suka fito yake kansu bakinsa yak'i rufuwa saboda tsanamin farin ciki har tsaye ya mik'e bai saniba,hannunsa UMMI ta kama ta d'ora na KHUBRA aciki ta damk'e a nata,cikin sanyi ta d'an yi musu tak'aitacciyar nasiha sannan ta k'ara da fad'in cikin zolaya tana dariya
"To SON ga matar ka nan na baka....Allah yasa ba a soma fushi daniba.."
Dariyar shima yayi sannan ya rungume UMMI yana fad'in
"Na gode sosai UMMI'NMU Allah ya biyaki da mafificin alkhairin sakamako.."
Duka suka amsa da amin,sannan ya d'auki yaransa biyu UMMI ta d'auko LITTLE har bakin mota ta rakasu,inda KHUBRA ta zauna sannan UMMI ta d'ora mata LITTLE kan cinyanta tana fad'in
"To Allah ya tsare hanya,ya kuma karemin ku daga sharrin abun cutarwa...Sannan kuma idan Allah ya kaimu cikin satin nan zansa a nemo y'ar dattijuwar da zata na taimaka miki...Kinji ko DOUGHTER..?"
Godiya suka mata sosai mayafin KHUBRA lullub'e har lokacin a saman fuskarta,tana tallafe da y'arsu dake bacci sai k'amshi na musamman yaran keta zubawa kamar iyayensu.Sai da taga tafiyarsu sannan ta koma cike da farin ciki a zuciyarta mara misaltuwa.
Suna fita a get en gidan yayi parking gefe,jin ya tsaya yasa KHUBRA murmushi dan kam tasan Ogan nata yau sai yadda Allah yayi da su,tasan babu batun hak'uri a lamarinsa yau kam.Tana cikin tunani taji ya d'age mayafin kanta,da sauri ta kulle idanunta tana murmushi,murmushin shima yayi sannan ya d'auke LITTLE daga saman cinyanta,kanta ta jinginar jikin kujeran tana sauke numfashi a hankali,kusa da y'an uwanta ya kwantar da ita a back seat,sannan ya janyo KHUBRA dake mak'ale jikin kujera kamar idol.
Idanunta dake kulle ya kalla yana sakin murmushinsa mai tsada kamar idon nata a bud'e yake,kissing pore head enta yayi sannan idanunta,a hankali ya gangaro saman lips enta,sun jima a haka inda ta samu ta k'waci kanta da k'yar tana mai da numfashin wahala,shi kansa gogan da k'yar ya samu ya daidaita gudun numfashinsa lokacin kad'an har ya tsinci kansa cikin wani duniya na daban,fizgar kan motar yayi yana ta faman murmushin da na kasa gane ma'a narsa......


《《》》


*GIDAN KHALEEL.*


Tun a wayewar garin ranar da KHUBRA take da kwanaki arba'in da haihuwa ZUHRA ta tashi da matsanancin zazzab'i mai zafin gaske,hankalin KHALEEL idan yayi dubu ya tashi saboda yadda jikinta yake ga amai da taketa fama da shi,yini guda har ta fita a hayyacinta,tausayinta duk ya cika KHALEEL,yana nan zaune rik'e da ita a jikinsa DR yazo,ko bayan da aka dubata DR ya gama y'an bicikensa nan ya tabbatarwa da KHALEEL tana da shigar ciki na kimanin wata uku da sati guda,murna gurin KHALEEL kamar zaiyi me dan dad'i.
Sai dai kuma wani abu cikin na ZUHRA da alamun mai wahalarwa ne,dalilin daya sa KHALEEL ya yanke shawarar tattara musu y'an kayan da zasu buk'ata,ya tattara ta suka nufi gidan UMMI..


Tafiyar su KHUBRA kenan babu jimawa motarsu ta kunno kai gidan,lokacin har UMMI ta gama shirin kwanciya kenan sallamarsu tasa ta fito.
Ganinsu a lokacin harda luggage's ta saki baki tana kallonsu.Bayan sun gaisa KHALEEL ya mata bayanin komai,murna gurin UMMI harda taka rawa saboda zata sake jin kukan jinjiri daga tsatsonta a karo na biyu duk da a yau ta rabu da wasu jariran sai dai fa wannan na musamman ne a gareta...
_Toh ZUHRA fatan Allah ya raba lafiya..._




《《》》


*INA LABARIN HAJIYA LAURA....??*


Nasan da yawa kuna da son jin yaya ta kasance a b'angaren HAJIYA LAURA....
Tun bayan da ta san illar abunda ta aikatawa HAJIYA MURJA da labari ya iskota da kuma rashin lafiyar ita HAJIYA MURJA'N,nanfa ta ttara inata-inata ta,duk wani abu na kud'i ta sai da shi da yake dama gidan na HAJIYA MURJA ne cikin abunda ABBA ya bari kafin ya bar k'asar,ta fice ta bar gidan da shirin tserewa k'auyensu,tana cikin tafiya da y'an kayanta cikin wata jaka,har Allah ya kawo ta tasha,cikin ikon Allah,tsautsayin ya afka mata a lokacin da take k'ok'in tsallaka titi,tana tafiya ba tare da ta kula da tahowar motarba,shi kuma mai motar shima baiga lokacin data shigo ba,take ko ya kad'eta kuma ba tare da ya tsayaba kasancewar a lokacin danja ta bawa gefensa hannu ya manni motarsa,suma HAJIYA LAURA tayi yashe a gurin wanda mutane suka samu suka maidata gefen hanya,taimakon gaggawa suka fara bata.Kafin daga bisani akayi asibiti da ita wanda likitoci suka shafe tsayin lokaci suna bata taimako.
Tsawon kwanaki biyu ta shafe a sume ba tare da tasan halin da take cikiba,sannan a kwana na uku ta farfad'o tana ta fana surutai kamar zararriya,da kyar likitoci suka samu suka shawo kan matsalar tata,sai dai fa wani abu HAJIYA LAURA duk k'ok'arin likitocin sun kasa hanyan da zasu tashi k'afarta,wanda a sakamakon had'arin HAJIYA LAURA ta rasa k'afarta d'aya da hannu.
Wannan abu ba k'aramin tada mata hankali yayi ba lokacin data koma hayyacinta,tayi kukan har hawayenta sun dena zuba,sai daifa tana nan da damuwa fal a ranta na rushewar lamarinta,haka dai take ci gaba da karb'ar kulawa daga malama'n asibitin kasancewar na gwamnati ne,batun magani kuwa sai dai idan Allah yasa sun samu kud'in dubiya daga gurin masu zuwa ziyara,idan kuma Allah yasa ta samu en sai ta samu ta fanshi magani da shi Wanda shima jimawa zai k'are....Abinci kuwa ba a maganarsa ma saboda bata da wanda zaiji k'anta ya d'auki d'awainiyar bata ko wane lokaci,bare kuma ayi maganar d'an jinya,wani lokacin sai dai ko a nan gadajen kusa da ita da suke tausaya mata su sanmata,a haka har Allah yasa ta shafe tsawon shekara guda a asibitin Wanda ba tare da an sallameta ba ta tsere.
Bakin danja ta samu nan take bara ta samu abunda za taci,tana yawo da sanda wanda ke taimaka mata tana tafiya,tayi bak'i ta rame bayaga kod'ewa da tayi wahala kullum k'aruwa take a kanta,kullum ta tuna abunda ya faru da ita sanadin rasa k'afar da tayi sai tayi kuka,ga dukiyar data tattara zata gudu tun da tayi had'arin bata sake ganin jakar tataba...
A kullum burinta a yanzun bai wuce zuwa neman gafarar HAJIYA MURJA ba sai dai tsoro ya hanata tunkarar gidan hajiyar.A haka har aka sake shafe shekara guda da fitowarta daga asibitin,kuma har wannan lokaci bata tara kud'in da a ganinta ta wannan hanyar zasu tarunba.K'ark'arinta ta samu abunda zata sai abinci ta ci.Gurin kwana ko ya zame mata abu mafi wuya ya kasance yanzun HAJIYA LAURA dake da d'akunan bacci iri daban daban yanzun sai dai bin rumfunan kasuwa........




*Alhaki kuikuyo kenan jama'a ga dai yadda k'arshen HAJIYA LAURA ya kasance,ta manta a sanadiyyarta ta jefa y'ay'a da dama cikin halin da yafi nata muni,tasa su kwana bakin kasuwa,da yawon neman abunda zasu rufawa kawunansu asiri tamkar mabarata,cikin garin da basu da kowa kuma basu da komai,ta manta da had'arin dake cikin bar in y'ay'ata mata a gaban iyayensu,wanda hakan dai² yake da siyan lasisin tarwatsa musu rayuwa..Duk ta manta da haka ta kuma toshe kunnuwanta a lokacin... Huh!!...Allah ya k'ara rufa mana asiri duniya da lahira..ameen...*









*COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃










*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*












*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠







*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com


*©®2018*
*11/ɑմցմՏԵ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*




*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










6⃣5⃣

*LAST PAGE.*







*I* sowarsu gida cikin mintunan da basu gaza arba'inba,ya fara bud'e mata k'ofan ta fito sannan ya bud'e back seat ya d'auko LITTLE dake bacci,mik'a mata ita yayi har lokacin yana sakin murmushi mai kashe jikin mai kallonsa,akan shoulder enta ta sata sannan tayi gaba,ABDUL da AS-SADEEQ ya d'auko ya d'ora su kan shoulder's ensa sannan ya tura k'ofan da k'afarsa,sai da ya tabbatar da ya kaisu har bed room ya kwantar da su,sannan ya koma don shigo da kayansu dake cikin booth.
Zama tayi gefensu tana kallon yadda yaranta suke k'ara girma,baccinsu suke hankali kwance kasancewar yaran basu da wani rigima shi yasa lokuta da dama ko a gidan UMMI ita kad'ai take kwana yaran kuma zaka tarar suna tare da UMMI.A nan ya sameta ta k'ure yaran da kallo cike da sha'awa da soyayyarsu,shigowarsa yasa ta kai dubanta gurin daya ke ajiye luggage set en nasu,ganin ita yake kallo yasa ta sakar masa murmushinta dake k'ara haske zuciyarsa,cikin d'an k'ank'anin lokaci ya k'araso gabanta,kusa da ita ya zauna yana sakin sanyayyar ajiyar zuciya,hannunta daya sha zanen henna ya d'ago yana kallo,sosai henna en ya masa kyau,kallonta yayi da alamar tambaya a fuskarsa ita kuma sai kawai tayi y'ar dariya tana fad'in
"UMMI tasa akamin d'azun..."
'Dan tak'aitaccen murmushi yayi yana kai hannun nata saitin bakinsa,kiss ya sakar ma hannun nata wanda ya haddasawa KHUBRA mutuwar jiki lokaci guda,idanunta ta lumshe tana sakin siririyar ajiyar zuciya,hayewa yayi ya kwanta kan bed en kansa na kan laps nata,ita yake kallo har lokacin bakinsa da magan-ganu masu girma sai dai yanzun kam ba lokacin yinsu bane,shi kad'ai sai sakin smile yake,idan ya juya ya kalleta ya sake juyawa ya kalli kid's ensu wani farin ciki ne mak'are a cikin zuciyarsa wanda ba shi da limit,mayafin data k'i cirewa tun shigowarsu ya kalla yana murmushi
"Yaushe kika zama matar liman kam....?"
Tambayan ya zo mata unexpectedly,sai dai data kalle shi kasa fad'in komai tayi,niko a raina nace ko dai KHUBRA bakin ya mutu tun a labour room ne..?
Ganin bata kula shiba yasa ya mik'e da sauri kamar ana fizgarsa,mayafin ya d'auke daga jikinta sannan ya sake komawa muhallin da yayiwa kansa ya kwanta,hannunta da yayi mata nauyi ta d'ora saman curly hair nasa da yake a gyare tsaf,ba kamar na samarin wannan lokacinba da za kuga yayi cukui² abun k'yama tana birkitawa,idanunsa ya shiga lumshewa dan dad'in abunda take masa a kansa yake ji kamar tana masa susa a kan,sun d'an jima a haka kafin ya mik'e yana fad'in
"JODI muyi wanka...ina jin bacci..."
Ita dai kawai ta kad'a masa kai amma magana tunda suka kamo hanya gaba d'aya kafafen sadarwa na bakinta suka tafi yajin aiki,kallonta kawai yayi da mamakin meke damunta kuma yau ta zama wata so speechless,k'ok'arin cire mata kayan ya shiga yi da sauri ta dafe tana kad'a masa kai,still yayi yana kallonta kuma bai fasa abunda yake niyyaba,kuka ta fara wanda sheshshek'ar kukanta yasa shi kallonta da matuk'ar mamakinta,yau kuma shi ne take yiwa kuka kan zai cire mata kaya to ko mene take nufi,hannunsa ta rik'e tana kad'a masa kai alamun bata so,har lokacin bai daina mamaki ba kallonta ya sake yi yana fad'in
"Me yake damunki kuma yau...?"
Shiru tayi masa kuma bata bar kukanba har lokacin,bai fasa tambayartaba yaci gaba dan ya kasa ganema kanta a yau kam,cikin sark'ewar murya wacce take cike da tsoro ta furta
"Ka bari zan iya da kaina...."


"Bakya so ne na cire miki kayan...?"
Kai ta d'aga masa alamar ehh
"Ok!....Shi kenan.."
Rabuwa yayi da ita cike da b'acin ran abunda tayi masa,kenan duk rawar k'afar da take akan d'ebosu ya tashi a banza ko me?? shi kam sam ya kasa gane nufinta,mik'ewa yayi yabar inda take amma sai yaga ko a jikinta wait an tsikari kakkausa,ficewa yayi inda yayi mata banging k'ofan,d'an tsorata tayi wanda a sanadin haka yasa LITTLE motsawa,sai dai Allah ya taimaka bata tashi ba,wani marayan kuka ta saki,cikin kukan take fad'in
"Wayyyoo! Allah shi kenan na jawowa kaina..Da na san ban masa haka ba,yanzun yaya zanyi...?"
_Niko nace mata ke kika sani kuma..._
Kukanta taci gaba da yi tana nan zaune ta sa yaran a gaba tana kallo hawaye na ci gaba da sauka akan fuskarta,yarfe hannayenta take zuwa can taci gaba da fad'in
"Ni dai gaskiya baran iya biye maka ba,haka kawai daga haihuwan nawa naje ka sake bani wani,dubifa duka shekaruna nawa amma da yara har uku,ni wallahi baran iya sake haihuwa ba wannan ma ai sun isa...."
Kukanta ne ya tsaya cak tunawa da tayi da yadda ya fita a d'akin,yanayinsa ya bata tsoro ita da basu tab'a samun sab'ani ba da shi,shi ne yanzun zata jawo ya fara tsanarta,kalmar *TSANA* data fad'o mata yasa tayi saurin mik'ewa tana kaiwa da kawowa,a fili ta shiga magana da kanta tana fad'in
"Wayyoo Allah! ya zanyi da shi,shi kenan na jawowa kaina fushin Allah zai sauka a kaina....
Idonta ta fiddo waje tana dafe kanta da sauri ta shiga cire kayan jikinta,cikin closet enta ta bud'e side en nightys enta,wani maroon colour silky ta fiddo wanda da ganin alama ba a tab'a amfani da suba sai data gama waresu tsaf ta kuma gama k'are musu kallo 3in1 ne kayan d'aya singlet ne,sai doguwa wadda zata kai har k'asa da mad'auri a gefen k'ugunta,d'ayan kuma rigane da wando do go,duka singlet en tsayinsa bare wuce saman knees entaba ta gabansa daga sama kuma wani ado aka masa

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads