Showing 108001 words to 111000 words out of 159513 words
Chapter 37 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt
mata yafiyar mahalicci...
An yafewa juna an kuma maida abunda ya wuce ya riga ya wuce,sannan an rungumi juna,dangi ya dad'a had'uwa bayan d'umbin lokaci da aka d'auka a tarwatse,tsintsiyar data tarwatse ta koma cikin mad'aurinta....
Sai yamma lokacin duka gida an had'u kowa nata murna da farin cikin ganin d'an uwansa,KAKA ya sake gabatar da su a matsayin y'ay'a da jikokinsa da ba kowa ya sansuba...
ABBA'N KHALEEL ne ya matsala kusa da KAKA nan ya sanar da shi dalilin zuwansu garin,na neman auren KHUBRA da KHALEEL yake son yi,sosai gidan kowa yayi murna da jin hakan,bayan an gama magana aka dank'a alhakin yanke ranar auren ga KAKA a matsayinsa na SHUGABA,yaji dad'i sosai bai yi wata-wataba ko ya dank'ara yanke lokaci nan da makonni takwas wanda yayi dai-dai da watanni biyu kenan masu zuwa.....Nanfa murna ta dad's k'aruwa fiye data farko.
BB kam jin wannan maganar da kuma hunkuci na KAKA ba k'aramin tada masa da hankali yayi ba,da k'yar yayi ta maza ya danne damuwarsa a lokacin,har aka gama duk maganar da za a yi kansa na k'asa dai-dai da sau d'aya baiyi kuskuren d'agowaba bare wani ya fuskanci yanayin da yake ciki..
Wajejen Maghreeb sukayi sallama da kowa kan zasu koma,bakin KHALEEL kam sam yak'i rufuwa saboda farin cikin da yake ciki a yau,bayan sunma mutanen gidan sallama kan zasu koma amma zasu dawo bada jimawaba,har bakin mota su OLD KHALEED suka rakosu sai da sukaga barinsu a line en sannan suna koma gida cike da murna da far in cikin al-amarin d'aya wakana a wannan rana.
KHALEEL ne ya amshi driving tunda a zuwa BB ne ya kawosu garin,godiya BB yayiwa Allah daya sa ba shi zaiyi driving ba,dan yana da tabbacin idan shi ne to babu makawa kam k'arshe sai dai su tsinci kansu a jirkice gefen k'walta.........
Tafiyar yau ta zama tarihi a garesu gaba d'aya family'n kowa na farin cikin yadda tafiyar ta kasance idan aka cire BB da wani gefe na zuciyarsa babu komai cikinsa face tsantsar k'unci,idanunsa da take jin sun masa nauyi ya rufe kamar mai bacci duk wani yanayinsa KHALEEL yana kula da shi,shi kam sababbin halayen da aminin nasa ya bijiro da su a kwanakin suna bashi mamaki matuk'a,shiko BB gani yake hakan da yayi shi yafi masa,a gurinsa kam cewa yayi wannan itace MAFITA a tare da shi....
*TAMBAYOYI......*
_Game da littafin *Y'AR GARUWA*.._
1-Shin a cikin wannan littafi wane ne jarumi & jarumar ku??
2-Wane mutum ne yafi burgeka/burgeki??
3-Wane mutum ka/kika fi tsana a ciki???
4-Wane mutane kukafi so a cikin wannan littafin???
5-Mene ne kuskuren mabuciyar a cikin labarin nata??
6-Shin yaya matsayin wannan littafi yake a gurinku???
7-Idan akace ka/ki bawa wannan littafi mark,mark nawa kuke ganin zai karb'a daga gurinku??
8-Shin kuna son wannan littafin ko kuwa??
_Sai munji daga gareku......_
*Comment for more page's....* 💃💃💃
*~#TEAM KHUBRA.~*
*_#®EAL $MASHER._*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*23/ʝųlყ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
_Naga comments enku kuma naji dad'in hakan sosaifa,sai dai k'orafinku gareni akan *MAMA'N KHUBRA* mafi yawancinku amsarku iri d'aya ce *"BAI KAMATA NACE TA MUTUBA"* sai dai abu d'aya nake son tunasar damu shi ne,itafa mutuwa wajibice akan ko wane bawa,walau ka shirya ko baka shiryaba,tabbas idan lokacinka yayi dole ne ka amsa kiran mahalicci,kuma wannan novel en da kuke gani ba wai zance muku true life story bane,just na k'irk'ire shi ne amma kumin afuwa tunda haka ya faru,dama tun farko haka na tsara labarin so ina ganin ba abun damuwa bane dan an rasa mutum d'aya a cikin labarin,sannan hakan shi ne solution ga MAMA'N KHUBRA dama su kansu ahalinta coz koda ace tana raye tofa kada ku manta abunda aka mata k'azafinsa ba zai tab'a gogewa ba,kunsan k'azafi a kwai ciwo sosai,so ina neman afuwanku..._
_Fatan Allah yasa muyi kyakyawan k'arshe....Ameen._
*Really luv u fan's..* ♥
*~__________________________~*
*DON ALLAH INA ROK'ONKU DA KU DUBI GIRMAN ALLAH DA YANAYIN YADDA NAYI MAGANA DA MANYAN BAK'AK'E,DAN ALLAH KUYI HAK'URI DA YA'DA JITA-JITA AKAN WAI ANYI KIDNAPPING SIS ENA,SISINA TANA NAN CIKIN K'OSHIN LAFIYA KUMA BABU ABUNDA YA SAMETA CIKIN HUKUNCIN ALLAH TANA NAN SAIMA K'ARIN LAFIYA DA KWANCIYAR HANKALI DA TAKE DA'DA SAMU FIYE DA BAYA,MASU YI DAN ALLAH KUYI HAK'URI HAKANAN,DAN BAMU SAN DAME ZAMU JIBA DA SAK'ONNINKU KO KUWA DA CIWON MAGANAR KIDNAPPE EN,INA FATAN ZAKU FUSKANCI NUFINA...MUN GODE.*
_Stay wealthy *CWEET SIS HABIBA IDREES (HUBBEEY)* nd now i turn ur name into *INDO K'AFAR.........* 😉💔
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
5⃣1⃣
*S* ai misalin k'arfe 10:00pm suka iso gida,a gida'n UMMI suka fara yin branch inda ABBA'N KHALEEL da KHALEEL suka fara sauka,bayan sun musu sallama kuma BB ya amshi driving,ikon Allah kad'ai ya kaisu gida,yana yin parking bai tsaya jiran fitansu ba ya fice a motan ya nufi cikin gidan.
Yanayin yadda yake tafiya kad'ai ya isa yasa a gane akwai matsala a tattare da shi,saboda yadda yake tafiya a durk'ushe dafe da side en k'irjinsa na hagu.
Da yake kowa a gajiye ya dawo saboda zaman motan da suka d'iba coz tafiyan yini guda akwai wahala,babu wanda ya lura da yanayinsa kowa ya shige nasa gefen.
ABBA kad'ai aka bari tare da ABBA'N KHUBRA,shima bayan daya nuna masa gefen da zai zauna sukayi sallama ya wuce shima.
Gidan shiru daga dukkan alamu mutanen gidan sun jima da yin bacci,hakan ce kuwa ta kasance dan wasu kam a lokacinma basu san inda kawunansu sukeba.
HAJIYA MURJA na d'aki ta kishingid'a,tana nan ta jiyo shigowansu gidan da motsinsu amma sai bata yi yunk'urin fitaba,har zuwa lokacin da ABBA ya shigo,nan ne tayi masa barka da dawowa,da mamaki ya kalleta yana fad'in
"A'a dama bakiyi bacci bane madam?...da naji gidan shiru haka nayi tsammanin ko har kunyi bacci nema..."
'Dan murmushi tayi kafin ta bashi amsa
"Uhmmmm! ta yaya zan iya bacci yanzun bayan ban san a wane hali yarana suka kasanceba..."
Teasingly ya kalleta da salon tsokana fal saman fuskarsa lokacin yana shirin zama kusa da k'afafunta
"Ke dai fad'amin gaskiya y'ay'anki kikafi damuwa da su ko kuwa mijinki....?
Baki bud'e take kallonsa
"Wane irin kuma miji y'ay'an dai...."
Dariya sosai maganarta tasa shi wanda ganin yanayin yadda yake yasa ita da kanta itama sai data dara
"Tohh! tunda kince haka let's see the truth....."
"Wane irin gaskiya kuma kake buk'atar gani a wannan maganar....?"
Winking yayi mata
"Ahhhh! ya wuce na nemi wani d'akin na kwana,tunda ni ba a buk'ar sanin nawa damuwan..."
Cikin sauri ta katse shi
"Aaaaa! nifa ba haka nake nufiba,kawai dai nace haka ne saboda kaga su yara ne ba wani girma garesuba,bayan haka ma kuma basu tab'a tafiya dogo kamar hakaba...."
Duk maganar da takeyi tana yi ne da kanta a langab'e kamar wata yarinya,koda yake za a iya ce mata yarinya,ammafa a gurin mijinta.
Cike da nishad'i suna tsokanar juna suka kwanta,bacci mai cike da kwanciyar hankali kam wannan family sun same shi,musamman b'angaren ABBA'N BB,ABBA'N KHUBRA,KHALEEL,dama sauran tawagar tafiya except one person.
A b'angaren BB kuwa tun daya samu ya shige bed room nasa,yayima Allah godiya kan bed ya zube zuciyarsa kamar zata faso chest ensa ta fito,duk lokacin daya tuna abunda ya faru a yau sai yaji zuciyarsa na masa k'aik'ayi ji yake inama bai san KHUBRA da KHALEEL ba a tsahon rayuwarsa da ya fi masa alkhairi sama da wannan al'amarin daya faru..
Da k'yar ya samu bacci ya d'auke shi shima sai gabanin salla'n asubah,bacci yake amma duk wanda ya kalleshi zai iya gano babu komai cikin baccin nasa face zallan wahala....
《《》》
Tun daga ranar da BIGGY ya yankama yaransa warning dai-dai da sau d'aya babu wanda ya kuma kuskuren yi masa shaye-shaye,tun daga ranan suka shiga hankalinsu,saboda tun kafin wannan lokacin suka san halinsa bare kuma yanzun da suke ganin ya canja wasu sabbin halaye dan yanzun ba kamar da bane..
Ranar Mondy kamar yadda aka buk'aci yaje *REVENUE OFFICE* en,aiko ya shirya da takardunsa a envelope ya fice,bai jira d'aukan motaba don a cewarsa idan suka ganshi a mota da matsala danko yana da tabbacin ba zasu tab'a bashi offer en aikinba.Babban dalili kenan da yasa BIGGY yake faman yawo a NAPEP.
Cikin hukuncin Allah aka masa interview ya kuma samu nasara inda suka mik'a shi b'angaren accountant da yake fannin *ECONOMICS* ya karanta,kuma babu laifi result ensa yayi kyau.
Aiki yake ka'in da na'in,babu damuwar komai a tare dashi hakane yasa shi bayan samun wannan nutsuwar da gyara halayensa da yayi ya yanke shawaran ziyartar danginsa,bayan zuwansu garin nasu ya tarar da baffaninsa na cikin matsananciyar buk'ata da rashi,taimako ya basu wanda su da kansu sai da wasu cikinsu suka zubarda hawaye saboda suka banzatar da rayuwarsa a bayan rasuwar mahaifansa wanda gini ya zubowa lokacin da suke tsaka da bacci,daga lokacin kuma da rik'onsa ya koma hannun kishiyar mama'nsa wacce ta azabtar da dashi na tsayin wani lokaci bai sake samun kulawa daga gurin dangin mahaifin nasa ba bare ya san muhimmancin su gare shi,wahalar yau daban ta gobe daban har ta kai da tana sa shi y'an sace-sace da haurawa gidajen mutane yana kwasowa yana kawo mata,ganin babu abunda take bashi ko da ya sato mata goal ne kuwa shima daga bisani ya gudu coz ko abinci ta girka rabonsa a ciki k'anzo ne,babba'n dalili kenan daya sashi guduwa don neman na kansa kuma ya tsaya da k'afafunsa ta hanyar ci gaba da wannan sana'a,wanda a lokacin daya baro k'auyen nasu ya kammala makarantar primary har ya shiga k'aramar secondary,bayan dawowarsa birnin kano'n dabo kuma bai zauna hakaba sai da yayi duk wani k'ok'ari da zaiyi ya maida kansa makaranta babban gata kenan da BIGGY yayiwa kansa a rayuwarsa ta baya.
Yasha sa albarka gurin dangi da suka guje shi abaya,wanda kafin ya dawo bakin aikinsa sai daya sanarwa baffanin nasa buk'atarsa ta zuwa nema masa aure cikin wani sati,babu musu bare jan lokaci duka suka amsawa buk'atarsa tare da yi masa alk'awarin zuwansu cikin weekend,ba don komaiba kuwa sai dan ganin yanzun yana cikin rufin asiri sannan kuma shi zasu mora ba shi zai moresu ba..
_Duniya kenan...._
《《》》
A safiyar ranar ta lahadi gaba gidan basu iya tashi da wuriba kasancewar akwai gajiyar tafiya tattare da su wannan dalili yasa gidan yake shiru,misalin k'arfe 10:00am suka fara fitowa d'aya bayan d'aya.ZUHRA data riga su tashi ta nufi d'akunan baccin nasu tana tashinsu,gurin KHUBRA ta dawo data bari a bed room coz su tare suke kwana suke tashi tun bayan bayyanarta komai nasu tare suke yinsa.
"Yawwa CWEETY ki tashi kinga yanzun ABBA yace yana son ganinmu duka a parlor.."
Juyi tayi tana bud'e idanunta da suka mata nauyi coz baccin bawai ya isheta bane,da kyar ta tashi ta shirya,a parlor ta tarar da su sun hallara suna shirin yin break fast.
Kusa da ZUHRA ta zauna ABBA ta fara gaisarwa sannan MAMA,sai kuma sauran y'an uwanta data tambaya lafiyarsu da yadda suka tashi.
Fuskokinsu babu alamun damuwa suke break,ABBA ya kalli yaran gaba d'aya cikin so da kulawa
"Ina BB ne kam...? Gaba d'aya kowa yana nan banda shi ko baccin ne bai sake shiba har yanzun...?"
Dariya sukayi duka gurin
"ABBA kaima ka koma ce masa BB ne?"
ZUHRA tayi tambayan tana dariya dan tasan ABBA da tsokana ya fad'i hakan
"Aaaaa! to nima ba dole na koma fad'in haka ba,nima ai naga BB ena ne ko....?"
Yayi tambayan yana kallon MAMA da take dariyan drama'n nasu
"To ai ABBA baka san me yasa muke fad'an hakaba...."
Kallonta yayi yana murmushi
"Ku rik'e dalilinku nima na rik'e nawa....Kuma dai duk da haka nima da BB zan kira shi ko kuna so ko baku so.."
All family en they were happy da wannan moment's da suka tsinci kawunansu aciki,MAMA ma ba a barta a bayaba dan ABBA ya sanar da ita komai game da matsayin KHUBRA a gurinsa,sai yanzun idan ta kalleta take jin kunyar abubuwan da suka aikata mata ita da su ASHNA lallai ta dad'a tabbatarwa da ubangiji baya bacci kuma duk wanda ka zalunta yana gaggawa tare da saukar maka da naka isharar,ta kuma dad'a godewa Allah daya sa KHUBRA'N ta bayyana ba tare da wani yaci zarafinta ba,da ace wani abu ya sameta to tabbas bata san kuma da wane ido zata kalli ABBA ba saboda gungun laifuka da ta aikata,ita kam wannanma kad'ai ya isheta hujja da zata kafa idan taga wani mai irin halinta.Har yau kuma tana dad'a neman afuwar Ubangiji kan laifuffukanta.
Bayan sun gama break aka koma hira,suna tsaka da hira KHALEEL yayi sallama,ZUHRA ce ta dunguri KHUBRA cikin rad'a take mata magana
"CWEETY ga oga nan ya zo ina fatan zaki bashi kulawa ta musamman"
Uwar harara KHUBRA ta maka mata,d'an bakinta ta dad'a tsukewa tana kallonta k'asa-k'asa ta furta
"Bafa nason iskanci kin sani..."
"Dillah wane iskanci,madam idan zaki zage ki bashi kulawa to idan kuma ba hakaba to y'an matan zamani sayi miki k'afa d'aya...."
Still tayi tana kallon ZUHRA da bakinta a bud'e
"Heeyyy! beb ki rufe bakin kada flies su cike miki shi..."
"Uhmm! Allah ya baki lafiya dan naga kina buk'atan addu'ah..."
Aiko ZUHRA ta amsa da ameen tana mata gwalo,bata sake kulata ba duk yadda taita tsokanarta,ganin tak'i biye mata yasa ta mik'e ta nufi bed room enta,cikin closet enta ta bud'e tana duba wani gown nata da take mutuwar so,a jikinsa leda en ta fad'o,da sauri ta tsuguna tana d'auko ledan tunanin inda ta same shi take,can kuma ta tuna yadda akayi ta mallakeshi ita sam ma ta manta da shi sai yanzun data gani ta tuna da tsawon lokacin daya d'auka a ajiye,d'an bud'ewa tayi tana fiddo kwalin ciki phone ne sabo mai maituk'ar kyau,zaroshi tayi duka tana dad'a dubawa,daga bayansa wani farin paper ya fad'o da mamaki ta d'auka ganin kamar letter ne ciki nan ta shiga ware shi a hankali kuma ta shiga bin kalmomin dake rubuce
*DEAR CWEET SIS.*
_"Am so sorry lil sis! nasan hukuncin dana yanke baza kiji dad'in saba sai dai babu yadda zanyi hakan ya zamemin dole,ba komai yasa na rubuta miki wannan short note enba sai kan wani dalili nawa......na yanke hukuncin tafiya don barin k'asar saboda samun nutsuwar zuciya ba don komaiba sai dan soyayya da take neman salwantar da ruhina....sai dai kash na makaro saboda wadda nakeyi dominta bata sanma ina yiba,behind kuma wani ya rigani,ina rok'onki daki tayani da addu'ah sannan kuma kada ki bawa kowa labarin abunda ya faru duk da nasan a lokacin da zaki samu wannan sak'on nayi nisa da ku......ga phone nan ko da wani abun ya faru a gida zamu dinga magana dake,idan na sauka a inda naje zan nemeki,ina muku fatan alkhairi...na barku lafiya.._
_Ur's BB..._
Ai ZUHRA na idar da karatun wasik'ar hankali tashe ta fice daga d'akin bata zame ko inaba sai hanyan bedroom ensa tana rafka masa kira,har ta shiga bata dena kiransaba,kaf d'akin ta kalla babu kowa ciki hankalinta a mugun tashe ta zube a gurin tana sakin kuka..
"Me yasa BB zakamana haka....ko mai yayi farko ai yana da k'arshe,ni kam bazan tab'a bari ka rasa farin cikin kaba,indai har akan soyayya zaka tafi ka barmu na tabbata wannan abun yafi komai muhimmanci a tare da kai....."
Kuka sosai take ta kife fuskanta da hannayenta biyu,dafa ta akayi ta baya a d'an tsorace ta d'ago tana kallonsa ganinsa gabanta yasa tayi saurin goge fuskarta paper en ta mik'a masa,karb'a yayi yana dubawa,bayan ya gama dubawa kafin tayi magana sai gani tayi kawai ya d'aga paper ya yagashi,sai da yayi masa gutsi-gutsi sannan ya rabu da shi..
"BB me yasa.......?"
Da sauri ya dakatar da ita,ta hanyar d'aga mata hannu alamar tayi shiru,shirun kuwa tayi itama tana binsa da kallon mamaki,tafiya ya soma yi har ya isa bakin bed ensa ya zauna,tana kula da yanayin yadda yake tafiya da gani kasan dauriya ne kawai yake yi,da tausayawa take fidda wasu sabbin hawayen cikin kuka ta fara masa magana
"YAYANAH! me yasa bazaka fad'i abunda ke damunkaba ka b'oye mana, shin baka tunanin akan ko zamu iya nema maka mafita...kana ganin