Header Ads
Showing 144001 words to 147000 words out of 159513 words

Chapter 49 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1247

Ads at the middle of Article




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹






*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com


*©®2018*
*8/ɑմցմՏԵ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*




*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










6⃣2⃣










*S* higa'nsa d'akin yana ta sauri dan ganin ya isketa,har lokacin tana a yadda ya barta,sai dai kam har lokacin idanunta a rufe suke ta takure guri d'aya saboda sanyin da take ji,yadda ya taddata sai ya tuno ranarta ta farko a gidan,kamar haka ya taddata ta k'udundune jikinta guri d'aya,still yayi yana k'are mata kallo,nan ya shiga tuno yadda sukayi a ranar,tunawansa babu b'ata lokaci ya raba jikinsa da kayan dake sanye a jikin nasa,a hankali ya haura saman bed en,ta cikin duvet en ya zare mata kayan jikinta had'e da rungumeta tsam cikin jikinsa,cikin kunnenta yake mata magana lokacin daya ga tana motsi yasan ta tashi ne.
"JODI ina ke miki ciwo......? me kuma kike so...?"
Yana magana yana shafa k'asan cikinta dai² maranta,sosai take enjoying abunda yake mata duk da kuwa ba wani k'arfi a jikintan,kanta ta girgiza masa alaman babu komai..
"Kin tabbata..?"
Nanma nodding kanta tayi,ajiyar zuciya yayi yana fad'in
"Oyyaahh! sanarmin mene za kici to kinji nasa a kawo miki..."
Cikin wahalalliyar murya ta furta
"Nifa na k'oshi..."


"A'aa JODI kada muyi haka dake,na tabbata yanzun babu komai cikinki duk kin haras...look maza sanarmin..."


"To ai dai na fad'a maka ban son komai,ni bacci zanyi kawai.."


"Haba mana JODI kingafa cikinki yadda ya koma da ganin alamu kinsan kema babu komai,ko kuwa kina son barin baby'nmu da yunwa ne...?"


Juyowa tayi da k'yar tana kallonsa a fili kuma ta maimaita kalmar
"Baby'nmu kuma JAAN a ina kenan....?"
'Dan murmushinsa mai tsada yayi mata yana shafa mararta har lokacin ya furta
"A nan mana JODI....don't u know u are pregnant....?"
Wani murmushi ne ya sub'uce mata duk da irin halin da take ciki hakan bai hana murnarta bayyana ba,da sauri kuma ta maida fuskarta yadda take cikin magana irinta mai jinya ta kalleshi tana fad'in
"Yama akayi ka sani bayan ni banga alaman haka ba...?"

"Hahhhh! JODI kinji haushi ne dana fara sani....?"


"Nop! YAYANAH kawai na kasa yarda ne ace ina da ciki yanzun.."


Kallonta kawai yayi yana ci gaba da murmusawa abunsa shi kam ya tabbatar kuma da sannu itama zata tabbatar
"Baby DR nefa ya sanarmin yanzun,ko baki san ya zoba ne...?"


"Yanzu kuma..? yana ina DR...?"


"Ya tafi..amma kam abunda ya fad'a kenan ga can sakamakon binciken daya kawo..."
Ya mata showing inda resul en yake kan mirror,d'an kallon takardar kawai tayi,a ranta ko fata take Allah yasa haka ne dan ita babu abunda ta sani,hatta da zuwan DR en zuwa k'arin ruwan daya mata da allurai wanda BB ya cire mata time en daya k'are saboda haka ne yasa bata san da zuwan DR ba.
Hannunta ta d'ora kan nasa suka ci gaba da aikin shafa gurin,idanunsa ya lumshe yana jin ranar yau a matsayin rana wacce tazo masa da al-khairai wanda ba zai tab'a mantawa ba,cikin kunnenta yaketa sauke mata sinka-sinka,container's,trailer's,basket kai da duk ma wani abu da idan kuka zuba bare d'aukeba dad'ad'an kalamai gameda sa mata albarka yake,ita kanta duk da halin da take ciki tana jin kalamansa har k'asan zuciyarta,jin kalamansa take kamar tafi kowace mace dace a duniyar da take rayuwa.
Cikin awanni mafiya k'aranci har ta ji jikinta ya koma mata normal zazzab'in ya sauka,amma kuma har lokacin suna mak'ale da juna,kiran sallah ne ya tashe su daga hiran da suke,bayan yayi alwala ya fita masallaci,inda ya barta za tayi sallah nan cikin d'akin,bayan ta idar da salla'n tayi addu'o'inta,mik'ewa tayi ta d'auke pray mat en had'e da hijab en jikinta,bakin mirror en ta tsaya tana ware farar takardar da BB ya mata nuni d'azun,a hankali ta fara bin rubutun tana karantawa,farin ciki kam mara misaltuwa tayi shi,kan stool en ta hau hannunta rik'e da paper tana ta faman sakin smiling,hannunta ta mayar kan mararta tana feeling babynta dake kwance gurin,idanunta ta lumshe tana jan numfashi a hankali,k'arin hannu taji kan nata da sauri ta bud'e idonta duk da tasan ko waye wanda zai yi hakan,kallonsa tayi tana sake sakin murmushi,shima murmushin yayi mata sannan ya d'auketa suka fice a d'akin,suna tafe yana mata magana coz shi kam har yanzun bai hak'ura da maganar abinciba
"JODI kink'i fad'in abunda zaki ci ko...? Kin san bana son zama da yunwa bare kuma ke...Kinga JODI maza sanarmin kinji...."


Sai da tayi dariya sannan ta furta
"Ni fa babu abunda zanci..."


"A'a bana son jin wannan maganar daga bakinki idan kika ci gaba da fad'a zanyi fushi fa.."
Ya fad'a yana b'ata fuska
"A'a! a'a!! dan Allah kada kayi kaji YAYANAH cake kad'ai zanci da fruit juice..."
Y'ar dariya yayi yana fad'in
"Haba JODI wannan ai ba abinci bane kayan kwad'ayi ne..."


"Ni Allah in ba shiba baran ci komaiba.."
Cike da shagwab'a kamar za tayi kuka.
"Ok! ok! an gama JODI..Kar kiyi kuka kinji..bari mu tafi mu siyo an fasa aiken kowa ma,kinga daga nan sai mu wuce gida ko...?"


"Ehhh! kuwa dama ina son zuwa kawai ban fad'a maka bane..."
Hancinta ya lakace yana fad'in
"Ina fatan dai Babynah ba yawo zai sa mamansa ta koya ba..."


"Haba YAYANAH kawai dan nace ina son zuwa...?"


"Ehh! mana.....ammm! JODI kin san wani abu ma kuwa..?"
Kallonsa tayi lokacin da yake sauketa cikin palour,da sauri ya koma ciki ba tare daya fad'i abunda yayi niyyaba,k'aton hijab ya d'auko mata har k'asa da plat en takalmi,da kansa yasa mata,ita kuma sai dariya take ganin yau wani sabon abu daya b'illo da shi,ita da bata fita da hijab sai in zata skul,yau kuma shi ne ya d'auko mata saboda neman magana irin tasa.
"YAYANAH hijab fa ka samin.."
Bata k'arasa ba ya katseta
"Ehh! nafi sonsa yanzun gara ki saba saboda koda cikin ya fito bana son kina fita da vail wasu suna kallemin ke,kinsan a lokacin duk abunda zaki sa zaina showing jikinki sosai.."
Y'ar dariya tayi kafin ya kama hannunta suka fice cike da nishad'i,bama kamar BB da yau jinsa yake kamar sabon ango.
Sai da suka biya wani eatery suka siya cake da juice da take so,sannan suka d'auki hanyan gidan nasu suna tafe suna hira har suka k'arasa.
HAJIYA ZUWAIRA zaune parlour dan kam yanzun ta jima da tashi daga matsayin da take da,shigowarsu KHUBRA ta haye kan jikinta tana kwanciya tana fad'in
"UMMANAH nayi missing enki wollah kwana biyu kamar na shekara ban gankiba.."


"Ke ni dad'ina dake kenan baki da aiki sai na son jiki kamar kyanwa,har yanzu baki san kin girma ba kekam.."
BB dake gefe yayi dariya yana fad'in
"A'a kam UMMA'NMU ai mun girma yanzun..."
Kallonsa tayi tana fad'in
"Inafa girma anan kana kallon babu abunda ya chanja a halin matarka na shegen son jiki..Nikam wannan ko haihuwa kikayi ina ga saikin koyawa y'ay'an son jiki dubafa ba dama taga mutum zaune yanzun ta d'afe mutum kamar ta samu katifa..."
Dariya dukansu sukayi nan ta fiddo cake enta tana ci tana korawa da juice enta har taci da d'an dama,tana gamawa lokacin HAJIYA ZUWAIRA ta mik'e tayi kitchen,tashi KHUBRA tayi ta koma kusa da BB dake saman 3seater cuistion,ta kwanta kan cinyansa tana fad'in
"YAYANAH yaushe zamu gidan CWEETY..?"
'Dan b'ata fuska yayi yana kallon cikin idonta
"Wayyooo! YAYANAH mene ya faru naga ka canja fuska lokaci d'aya...Ko baka son kaini na ganta...?"


Fuskarsa ya yamutsa kafin kamar wanda akayiwa dole yace
"No...!"


"To mene ne kasan nifa har ga Allah banso naga canji irin wannan a tare da kai,gani nake kamar na maka laifi mai girma..Please dan Allah ka fad'a min kaji.."
Ta k'are maganar tata kamar za tayi kuka
"Ehhemm! laifinma aikinyi kam.."


Cikin d'an rikicewa ta mik'e daga jikinsa tana kallonsa lokacin har idonta ya gama cika taf da hawaye coz bata san laifin me tayi ba,ita kuma a rayuwarta abunda ta tsani ji kenan yace tayi masa laifi cikin rashin saninta,ranar ji za tayi rayuwarta ta mata k'unci
"Dan Allah YAYANAH kaji ka sanar dani ko dan na gyara..Please kaji HAYATEEY...!"
Banda dariya babu abunda BB yake k'unshewa saboda yadda tayi daf hawayenta suke da zubowa,shi kuma sai wainata yake,tunawa yayi da maganar DR inda yake shaida masa ba'a son mace mai ciki ta dinga shiga damuwa ko sa abu a ranta,hakan zai janyo mata matsala..
Da sauri ya saki fuskarsa yana kamota,kwantar da kanta yayi saman sholder ensa ta dama cikin rarrashi yake fad'in
"Sorry JODI ba wani abu mai tsanani bane da zaki tada hankalinki kinji ko...Kwantar da hankalinki kinji.."


"Ni dai ka fad'amin dan Allah..."
Dai² lokacin hawayen dake idonta suka sakko,d'uminsu ya jiyo saman sholder ensa da sauri ya d'agota yana zare ido
"JODI mene haka kuma..kin sanfa bana son haka ko..shi ne amma kike yi..."
Ya fad'a yana dad'a maida fuskarsa alamun da tasan babu wasa cikin maganar da tayi,kece masa tayi da kuka cikin kukan take fad'in
"To ba kaine kace na maka laifiba kuma na tambaya kak'i fad'amin...."
Kansa ya dafe yana fad'in
"Ya salaam...!"
_Ni da nake gefe nace "Kujimin d'an malfar uba bayan shi ya janyo take kukan kuma yake d'aure fuska,kai wannan koi mai murd'ad'd'en hali..ka ce an maka laifi kuma kak'i fad'a...bahago kawai.."_ 😣


Fuskarta ya rik'e da hannayensa,bakinsa ya kai dai² inda hawayen ke bi,nan ya shiga d'auke mata su,dalili kenan daya sa kukanta tsayawa tana kallonsa,murmushi ya mata bayan ya gama d'auke mata hawayen,idonta na dama ya sumbata sannan na hagu,bakinta ya nufo da sauri ta kulle bakinta tana raba ido.Kallon yadda tayi yasa shi b'ata fuska,kamar za tayi kuka ta furta
"YAYANAH bafa gida muke ba.."
Sai lokacin ya juya ya kalli inda suke,kunya ce ta kama shi ganin ya kusa aikata ba dai²ba a gidan surukai,amma ganin babu kowa yasa shi bata fake kan bakinta,wanda bata yi tsammanin samunsa a lokacin ba.
"Ni ka fad'amin abunda kake b'oyewa.."
Ta fad'a tana turo d'an bakinta gaba,bakin ya kalla yana murmushin mugunta
"Ok! amma ki daina min wannan turo bakin kinsan duk lokacin da kikayi ina kasa controlling kaina..."
Murmushine ya sub'uce mata nan ya sata gaba yana tsokana
*"MAI KUKA TANA DARIYA....AI MATA 'DAN KWA'DON DADDAWA...!*
*MAI KUKA TANA DARIYA....AI MATA 'DAN KWA'DON DADDAWA...!!"*


Dariya ta fashe da shi sosai,shi kuma nan ya shagala da kallonta yana kuma ci gaba da tsokanarta kamar wani k'aramin yaro..
UMMA'NSU ce ta fito da plate a hannu,zama tayi tana fad'in idan kin gama shagwab'ar to ga abinci can na jiranku a teburi.
Kallon plate en data ajiye gabanta tayi nan ko ta hango d'an wake da manja,ai tuni yahunta ya fara gudu,cikin sauri ta sauka kan jikinsa,gaban plate en ta isa tana zuwa kuwa ta sure shi babu ko magana ta zauna nan k'asa ta soma cin abunta har dasu lumshe ido,kallonta kawai sukeyi shi kam BB dad'i yaji sosai daya ga tana cin abincin,ita ko UMMA ZUWAIRA sakin bakinta tayi tana kallon ikon Allah,can kuma ta saki murmushi saboda wani tunani da tayi,a fili ta furta
"To to to..! ince ko dai mun samu k'aruwane take wannan zalamar...abunda nasan ba halinta bane..?"
Daroya BB yayi yana d'aga mata kai dan shi ta kalla tayi maganar,wani murmushin ta sake yi tana fad'in
"To! ko da naji...Allah ya inganta,Allah kuma ya raba lafiya.."
Fuskarta da matsanancin farin ciki na jin zasu samu jika kwana kusa,kallonsu suka maida kanta suna ta hira tsakaninsu,amma ina sam KHUBRA bata sanma abunda suke yiba har ta kammala sannan ta shiga tsotse yatsunta d'aya bayan d'aya,kallonta sukayi suna murmushi
"Haba KHUBRA zafa ki cire hannunki kan tsotsan da kike musu.."
'Dagowa tayi ta kallesu had'e da yin murmushi,sob'on data gani cikin cup ta d'auka ta tultulawa tumbinta,kan tsaban dad'in da yayi mata har lumshe ido take,da kyar ta mik'e tayi hanyan kitchen hannunta d'auke da plate data yashe abincin ciki,ko data fito BB ta nufa tana zuwa ko tayi pillow da cinyansa,take ko bacci mai d'ankaren dad'i ya kwasheta.
Sai after asr ta farka ta ganta kwance kan pillow na cuistion en,d'an waigawa tayi tana kallon cikin parlour'n,dai² lokacin ya shigo a hankali ta sauke k'afafunta k'asa ta mik'e tana tafiya inda yake,warm hug ta bashi tana dad'a lumshe idanu
"Baccin ne bai ishekiba ne...?"
Kanta ta d'aga masa,ok muje to kiyi sallah saimu tafi gida.."
Hannunta ya kama sukayi ciki,inda ya taimaka mata tayi alwala,a gabansa tayi salla'nta tana addu'ah shima ya d'aga nasa hannun,da yake su kad'ai ne cikin d'akin bayan ta k'are ya zare mata hijab en yana fad'in
"Kawo nan muje ki huta saimu tafi anjima ko..?"
Kai ta d'aga masa tana yin gaba a parlour suka dad'a rashewa ita kuma UMMA ta lek'o jin kamar magana
"A'a ashe ka dawo..."


"Ehh amma ban jimaba ma da shigowa ba."


"Ayyahh! sannu da dawowa.."
Amsawa yayi,ita kuma ta maida kallonta kan KHUBRA tana fad'in
"KHUBRATU zaki ci wani abu ne yanzun....?"

"A'a na k'oshi sai dai ko anjima.."
"To shi kenan.."
Kitchen ta koma taci gaba da aikin gabanta,kallonsa tayi nan ta tuna da abincin da aka ce suci d'azun,ita kam tun bayan data ci nata bata saniba ko shi en yaci,saurin kallonsa tayi tana fad'in
"JAAN kaci abincin kuwa...?"
Kai ya kad'a mata alamar a'a,da fuskarsa da ya maidata kamar wani yaro,da sauri ta sauke k'afafunta k'asa har tana neman fad'owa,saurin rik'eta yayi yana fad'in
"Easy JODI.....Ina zuwa kike sauri haka,bakya tsoron ki fad'i ne kam..ko kuwa kin manta yanzun bake d'aya bace...?"
Marairaicewa tayi kamar za tayi kuka
"Abinci fa zan kawo maka..."
Bakinta ya rufe da hannunsa yana d'an murmushi
"No kada ki damu naci abinci d'azun,UMMA ta bani kina bacci..."
Sai lokacin tayi sanyayyar ajiyar zuciya,sannan ta koma ta kwanta,can ta fara magana
"JAAN inafa binka bashi.."


"Uhhummm! ina jinki na mene bashin...?"


"Maganar d'azu..."
Ta bashi amsa a tak'aice


"Ohhh! ni kingama har na manta,amma ke da yake kin damu da ji kin kasa mantawa.."
Batayi maganaba sai wasa da take da yatsun hannunsa dake cikin nata,dai² kunnenta ya kai bakinsa yana fad'in
"Kin san laifin da kika min..?"
Har cikin ranta ta girgiza masa kai
"Kina kirana da suna biyu,so na kasa bambancewa wanne nawa wanne ne kuma ba nawa ba."


Kallonsa tayi shi kuma ya mata winking
"Duka mana...ai duk naka ne.."


Cike da shagwab'a yake fad'in
"Ni dai a'a gaskiya sai dai a zab'i d'aya...Kuma bana son wannan YAYA'N da ake fad'a.."
Y'ar dariya tayi tana fad'in
"As u wish yallab'ai..."


Ido ya fiddo yana fad'in
"Kinga ni ba yanzun ma kin sake k'aramin wani...ko..?"


Tana murmushi take fad'in
"To MY JAAN an daina daga yau..."
Dariya sukayi ta sake maida kanta ta kwantar tana hamma.."
A tak'aice dai basu suka tafiba sai wajejen 9pm shima ABBA ne ya korasu.
Suna tafe a mota ta zame ta kwantar da kanta kan cinyarsa,while shi kuma yana driving,bacci ne ya d'aukenta cikin alamu na magagin bacci can hannunta ta motsa duk a cikin bacci aiko nan ya tafi wata jiha ta daban,da sauri BB ya take burki,Allah ma yaso su titin babu yawan cinkoson abun hawa,gefe ya gangara sannan ya d'an dubata,gani yayi batama san abunda yake faruwa ba,d'an murmushi yayi ya gyara mata kwanciyar,sannan ya mik'i hanyan da zata maida su gida,har bedroom ya kaita,sai bayan ya ajiyeta ta bud'e ido
"Ina zaka tafi JAAN...?"
'Dan waiwayowa yayi ya kalleta
"No JODI zanyi wankane na dawo..."


"Shi ne kuma ni bara ka yiminba...?"


"Sorry naga kina bacci ni kuma kin san bana son abunda zai tada ki a baccin.."


"To ai na tashi yanzun,kasan baran iya bacci haka nan ba.."


"To tsaya na cire miki kayan ko..?"
Kai ta d'aga masa alamar toh,a hankali ya tako ya dawo gabanta,sannan ya cire mata,towel ya d'aura mata sannan ya d'auketa sukayi toilet.
Sun d'an jima ciki kafin suka fito,yadda suka fito yasa nace 'Ikon Allah wai nasara da gwado' kunsan me na gani....?


Towel ne guda d'aya sanye jikinsu KHUBRA ta rik'esa ta gaba,k'afafunta akan nasa,hannayensa zagaye da ita ta gaba,yana tafiya dasu a haka sunata faman shek'a dariya.Shi ya fara zama saman stool en sannan ita dake kan cinyansa suna kallon mirror
"Sauka na miki shafa ko..?"


"Tabbb! wollahi baran sauka ba,salon haka kawai kasa y'an group en *SMASHER & HUBBEEY 1&2,SHDG NOVELLA,SHDG COMMENT'S ONLY,LEEMA FAN'S GROUP,SAWWAMA FA'NS GROUP,BARKIN'DO & MUHIBBAT* 😜su k'aremin kallo,Allah babu inda zani,naga dai kaika cillamin nawa cikin ruwa,sannan kuma kace na sauka Allah saika samin kayana zan sauka.."
Dariya yayi mata yana mata gwalo ta cikin madubin
"Yarinya ai sun riga da sun ganki tun a toilet lokacin ina miki wanka..."
Kukan shagwab'a tasa masa tana

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads