Header Ads
Showing 156001 words to 159000 words out of 159513 words

Chapter 53 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1244

Ads at the middle of Article

da net,sawa tayi sannan ta tsaya kallon kanta ta cikin mirror dake gabanta,kayan yayi shara² sosai ta gaba kallon yadda suka bi jikinta take ta cikin kayan ana iya ganin hatta da nipples enta,gashinta ta tattara gefe ta masa tufka d'aya sannan ta kwantar dashi ta gefen necklace enta inda ya sauka har kan chest enta,sosai hakan da tayi ya mata kyau,idanta ta kalla yadda suka yi ja saboda kukan da tayi a hankali ta nufi toilet,sai da ta wanke fuskarta ta kuma sake kama ruwa da ruwan d'umi sannan ta fito,jingina tayi jikin k'ofan kanta a sama tana tunanin mafita,kanta tayi saurin d'agowa tunawa da abunda UMMI ta bata kafin ta fito da ita,da sauri ta nufi hand bag enta daya ajiye mata jikin abunda take sak'alesu,sai data d'auko abun a leda bak'i sannan hankalinta ya kwanta,wani ajiyar zuciya ta saki sannan a fili ta furta
"Sam na manta ma da wannan abun wallahi da duk haka bai faru tsakaninmu ba..."
Tunowa tayi lokacin da ummi ke mik'o mata abun bayan ta gama bata na gyaran jikin,tambayan da tayiwa UMMI da amsar data bata ta sake tunawa
_UMMI mene wannan..?_


_Karb'i ki ajiye zai miki amfani nan gaba.._


_To amma UMMI mene amfaninsa shi...?"


_Wannan da kike gani y'ay'an angurya ne...yana da amfani sosai ga macen data haihu,yana taimaka mata musamman gurin hanawa ta sake samun ciki da wuri,kinga ba sai kinyi planning ba ko dan gudun samun matsala da mai gidan naki,idan hair bai yadda ba za kuyi ta samun sab'ani,wannan zai taimaka miki har sai kin samu kin yaye wanda kike shayarwa..._


Karb'a tayi tasa a jakanta sannan ta mata godiya..
'Dan murmushi tayi da sauri ta d'ibo a hannunta tana dubawa,maidawa tayi da sauri kuma tayi parlour,ruwa ta d'auko da cup sannan ta dawo d'akin,a nan tasha sannan ta maida ragowar muhallinsu tana murmusawa,fuskarta ta gyara tare da murza powder kad'an ta shafa lip stick enta da yake matuk'ar k'auna.
Bakin bed enta ta koma ta d'auka d'ayan rigan wadda take doguwa har k'asa,ta d'ora a saman ta jikinta sannan ta kama mad'aurin ta d'aure,addu'a ta tofe yaranta da shi sannan ta fice tana nufan bed room ensa duk da irin yadda zuciyanta keta tsinkewa.
Cike da fargabar abunda zata tarar ta tura k'ofan da sallama a bakinta cikin sanyi,can k'asan mak'oshinsa ya amsa mata ba tare da ya kalli inda takeba,hakan da yayi yasa ta sha jinin jikinta,sai dai kuma tunawa da ita ta janyo komai yasa ta aro jarumta ta lik'a ta kuma ci gaba da shiga cikin d'akin,shirin kwanciya yake hakan yasa ta isa gabansa da niyyan taimaka masa,sai dai ko data k'arasa tana k'ok'arin taimaka masan matsawa yayi a gurin,cikin sanyin jiki dan kam ya gama kashe mata gab'ob'i ta furta
"Kawo na k'arasa maka...."


A tak'aice ya bata amsa da
"Barshi ban buk'ata..."
Sosai ta tsorata da abunda ya fad'a bata kuma ce masa komaiba ta nufi bakin bed ensa tana shirin zama,muryarsa da tambayan da ya watso mata suka sa ta kasa k'arasa abunda tayi niyya
"Me za kiyi a nan...?"


'Dan juyawa tayi tana kallonsa,shi enma itan yake kallo da fuskarsa da take d'aure tam kamar an aiko masa da sak'on mutuwa
"YAYA kwanciya zanyifa..."
Ta bashi amsa kamar za tayi kuka


"Su kuma yaran nawa wa kika bawa ajiya...?"


'Dan kallonsa tayi cikin rashin damuwa ta shiga ware mad'aurin rigar had'e da zareta a jikinta tana kwanciya saman bed en nasa ta furta
"Ai sunyi bacci..."
Kansa ya kad'a yana fad'in
"Na san sunyi bacci ai...Tambayar dana miki itace...Wa kika bama ajiyarsu...?"

"Kamar yaya...? naga dai ko can gidan UMMI ma ba tarefa muke kwana dasuba..."


Fuska ya dad'a tamkewa cikin fushi ya shiga mata fad'a
"Saboda kinga ina had'a shimfid'a dake shi yasa kika raina ni ko...Wato ga sakarai shi ne zaki dube ni kina gayamin ba tare kike kwanciya da suba....
Barin fad'a miki kuma ki bud'e kunne sosai kiji ni daga yau in sake miki magana ki bani irin wannan amsan na rainin wayo.....shi kenan dan kinga na miki ciki kin haihu sai ki ce zaki min abunda kika ga dama....wallahi idan baki maida hankalinki a jikinki ba zan daka ki,ki shiga hankalinki kinji dai na fad'a miki,kuma yanzun ba sai anjima ba kizo ki ficemin a d'aki...Ko an fad'a miki ni jarababbene da zaki kwaso jiki ki biyo bayan kin nunamin iyakata.... Wannan ya zama na k'arshe kada ki kuskura ki sake barin min yara su kad'ai da sunan su kad'ai zasu kwana,duk ranar da kika sake kuskuren yin haka Allah sai nayi mugun sab'a miki..."
Yadda ya bad'e idanunsa da toka yana ta zuba fad'a yasa ta fashewa da kuka mai cin rai,cikin k'unk'unin kuka take furta
"Dama nasan haka sai ya faru wata rana,duk wanda zai maka alk'awarin soyayya ba zai tab'a iya cikawa ba,tun dana taso na rasa wanda zai soni a rayuwata,na rayu da mahaifina wanda ya zame min uwa da uba....Duk duniya shi kad'ai ya soni....meye laifina a rayuwa da kowane lokaci idan na samu nutsuwa sai wani abu ya gilma tare da disashe farin cikina...? Ban san me nayiba a rayuwa da ko wane bayan zamani saina shiga k'unci,bayan duk irin rayuwar da nayi a baya tun daga gidanmu bare sa a tausaya minba...Haka na koma tamkar mabaraciya a lokacin da nake neman rufin asiri daga mahalicci wanda ya janyo har wasu suke zagina a matsayina na *Y'AR GARUWA* wacce bata da wani sauran gata,a lokacin kowa kallon y'ar iska yakemin wadda ta gudu daga hannun iyayenta,ba dan Allah yaji k'aina ba ya had'a ni da matar da ta rik'e ni a matsayin y'a ba,da haka rayuwata zata ci gaba da tarwatsewa kenan,shin yanzun kuma mene ne laifina dan nayi wannan maganar....?"
Ta k'arashe tana sake rushewa da matsanancin kuka,wani kallo ya shiga watso mata cikin k'unar rai ya furta
"Kada ki kuskura ki zageni ko mahaifiyata,dan naga rashin mutunci kike ji dashi,idan har kika kuskure kika zageta zan nuna miki iyakarki..."
Kukanta ne ya tsaya cak jin maganar da yake,da sauri ta goge fuskarta tana fad'in
"Ni ban isa na zagetaba,hasalima idan dan kana tunanin ina magana ne akan itace sanadin daya sa nayi wannan rayuwar a baya to ka daina,na sani tun ran gini ran zane,k'addarata ce kuma dole sai haka ya faru....Saboda haka kayi hak'uri ni ban isa zagin mahaifiyar kaba bare kuma kai..Ina rok'on Allah da kada ya bani ikon aikata haka...Kayi hak'uri ka yafemin nasan na b'ata maka rai,amma dan Allah ka yafemin..."
Bai sake kulataba dan yasan idan yaci gaba da magana to tabbas daren yau bazaiwa kowannensu dad'iba,saman bed ya zauna yayi addu'o'insa sannan ya kashe light en d'akin yayi kwanciyarsa.
Nan tsaye inda ya barta take har lokacin wasu siraran hawaye masu d'umi suka sake zubo mata,cikin sanyinta ta nufi hanyan fita tana kuma mamakin abunda ya faru,Wanda ko cikin bacci aka fad'a mata haka zai faru tsakaninsu zata k'aryata,har ta fice bai ko sake kallon inda take ba.
Saman bed enta ta zauna dafa'an ta shiga rera kuka mai ban tsoro da tausayi,cike da tashin hankali take kuka tana k'arawa,dan kanta kuma ta rarrashi zuciyarta sannan ta d'auko LITTLE tasa ta a gabanta sannan mazan dake kusa da LITTLE hannunta ta d'ora samansu tana sake had'asu da jikinta,da k'yar bacci ya d'auketa sai ajiyan zuciya take saukewa da k'arfi.


B'angaren BB ma hakan ce ta kasance,lokacin data fita a d'akin yana kallonta tana goge fuskarta akai²,maganganunta ne suka shiga yi masa yawo cikin kansa,tausayi had'e da soyayyarta lokaci d'aya suka kawo masa ziyara wanda suka sa sam sai yaga baiga laifintaba cikin abunda ya faru kuma gaskiya ta fad'a ba tare suke bacciba dan UMMI ma ta fad'a masa,kukanta ne ya shiga dawo masa a cikin kunnensa,mik'ewa yayi ya shiga safa da marwa cikin d'akin har dare yayi nisa idanunsa biyu ya gagara bacci,nan zuciyoyinsa suka shiga kawo masa shawarwari daban-daban sunata fafatawa akan yaje ya rarrasheta,d'aya kuma na fad'in hakan da yayi mata shi ne zaisa ta gane kuskurenta ko nan gaba,dan taga yana tsananin sonta ne yasa zata fara masa iskanci,hakan da yayi mata ko zaisa ta gane nan gaba kuma bazata sakeba,yayin da d'ayan gefen na zuciyarsa ke sanar masa da,idan ya duba halayyarta kuma da tsayin zamansu ai bata tab'a masa laifi makamancin haka na,tabbas idan yayi mata haka bai mata adalciba,kuma ina al'k'awarin daya mata na killace soyayyarta har k'arshen numfashinsa,zuciyarsa ce tayi wani irin bugu tunawa da alk'awarin,kasancrwarsa mutum mai girmama alk'awari,nan ya shiga tunani iri-iri akan yaje ya rarrasheta ko a'a,kwanciya ya sake yi lokacin da ya amshi shawarar kangararriyar zuciyar tasa.
Sai daifa a banza yadda yaga rana haka yaga daren ranar,sam bacci ya gagari idanunsa,ba shi ya samu bacciba sai wajejen k'arfe biyu,wanda ya haddasa masa yin sallah a makare.
Ko bayan daya idar bacci ne ya sake d'aukansa dan dama ba wani bacci yayiba sosai a daren.


Da asuba ta tashi tayi sallah kuma har lokacin yaran basu farka ba,baccinsu suke hankali kwance,sanin bata da mataimaki yasa bata yi tunanin komawa ta kwanta ba,fita tayi ta fara y'an aikace aikacenta,sai data gyara ko ina na cikin gidan sannan ta shiga kitchen da tunanin abunda ya kamata ta musu na break fast,markad'ad'd'iyar gyada ta d'iba ta dama dan kam kunun gyad'a kawai taji tana sha'awar sha a safiyar kuma dama ganin tana so yasa UMMI ta had'ota da gyad'ar.
Zuciyarta duk babu dad'i haka take aikin saboda abunda ya had'asu jiya ya tsaya mata a rai,sai data gama ta shirya komai a dinning,ta dawo zata wuce bed room da niyyan dubawa ko sun tashi,dan tun d'azun data fito tana aikin tana dubawa amma tsill saita samu sunata bacci abunsu.
Doorbells taji na k'ara da sauri ta nufi gurin dan dubawa a ranta kuma tana mamakin waye da wannan safiyar..?
Bata tambayaba sai data lek'a a hankali kuma ta bud'e k'ofar ganin wata y'ar dattijuwa tsaye yasa ta saki fuskarta tana fad'in
"Sannu da zuwa..."
Amsawa matar tayi da y'an kayanta cikin wata y'ar jaka tabi bayan KHUBRA,bayan sun gaisa cikin sakin fuska,matar ta shaida mata UMMI ce ta turota yanzun driver'nta ya kawota,kuma itace wacce zata kula da yaran,murna sosai KHUBRA tayi dan dama zuciyarta duk a dame take da tunanin yadda za ta dunga ma yaran wanka ta kuma shirya su.Godiya ta mata sannan ta d'auki kayan matar mai suna SABUWA tayi ciki ita kuma tana biye da ita har bed room enta inda yaran ke kwance,nan ta zauna tana kalle-kalle na yadda tun daga get en gidan ya zama abun kallo ashe tace bata ga komaiba,wanka KHUBRA ta shiga bayan ta fito ta shirya cikin riga da sket na wani atamfa daya matuk'ar yi mata kyau,ta kafa d'aurin d'ankwalinta kamar gwagwgwaro,sannan ta fad'awa SABUWA tana zuwa ga yaran nan ko da zasu tashi bata nan,nan ta nuna mata komai a sauk'ak'e sannan ta fice.
Ficewa tayi fuskarta tasha kwalliya sai dai kallo d'aya zaka mata ka gano bata tare da nutsuwarta haka nan dai ta isa d'akin nasa,kwance ta tarar da shi har lokacin yayi hugging pillow so tight,duk sai taji wani iri da bata aikata abunda tayi ba da tuni itace haka kwance jikinsa kamar ko wane lokaci na can baya,rashin jin dad'in ne ya rinjayi zuciyarta wani missing ensa ya taso mata daga can k'asan zuciyarta,k'afafunta taja cikin sanyi ta isa kusa dashi ta zauna,hannunta ta d'ora saman kansa tana shafawa murya k'asa-k'asa saboda kuka dake neman kufce mata ta furka
"Ka gafarce ni mijina na san ni mai lefi ce a gareka,amma banyi dan na b'ata makaba,sai bayan da nayi ni kaina abun ya dameni...Dan Allah kace ka yafe min ko zan samu nutsuwa da sukuni.In Allah ya yarda haka bazai sake faruwa ba da izinin Allah..."
Kamar wacce take magana da mutumin dake ido biyu taketa surutanta,hawaye na sakkowa kan fuskarta har ta k'araci maganganunta tayi shiru,mik'ewa tayi da miyyar komawa gurin SABUWA,taji an rik'o hannunta,da sauri ta juya ta kalleshi ga mamakinta idonsa har lokacin a kulle suke,mamaki ne ya cikata da ganin hakan,k'ok'arin zame hannunta taci gaba dayi,cikin siririyar murya ya furta
"Ina zaki jene...kike k'ok'arin k'wacewa..?"
Sake kallonsa tayi taga da gaske shi yayi magnar ko kuwa.? sai dai wannan karon data kalleshi sai taga ya bud'e idanunsa kuma ita yake kallo,kanta ta sauke k'asa ba tare da tayi maganaba,abunda KHUBRA bata saniba tun daga shigowarta d'akin BB yana ganinta ta tsakanin lashes en idonsa,kawai dai yayi mata fakare ne ta yadda za tayi tsammanin bacci yake,saboda haka duk maganganunta babu wanda bai jiba kuma sosai yaji ya samu nutsuwa a lokacin.
Dawo da ita yayi ta zauna sannan ya mirgina jikinta,kansa ya d'ora kan k'irjinta hannayensa zagaye da waist enta ya shiga sauke wani wahalallen ajiyan zuciya,a b'angarenta kam ko iya haka kad'ai yabar ta tabbas ya gama mata komai dan kam ji tayi kamar an mata gafara,da sauri ta rungume kansa tana sakin ajiyan zuciya,yanayinsu kad'ai ya isa ya bayyanar da yadda sukai missing junansu,kansa ya d'ago yana kallonta da sauri ya dad'a kusanta bakinsa da nata,bai jira jin komai ba ko shawara da kowaba ya shiga aika mata da zallar k'aunarsa cake sawa ta manta ita wace,suna yi suna exchanging word's da suke nuna tsantsar yadda sukayi kewar junansu.
Cikin lokaci k'ank'ani suka manta da duk wani abu daya faru dasu,sun yi nisa cikin wata duniyar ta daban da babu wanda suke tunawa face kawunansu,sun farantawa junansu inda suka manta da duk wani abu daya had'asu a wancan daren.


Haka rayuwarsu ta ci gaba da tafiya a yayinda kowanne ke kaffa-kaffa da gujewa b'atawa d'an uwansa,basu da aikin daya wuce farantawa junansu da kyautatama junansu,inda yaransu kuma suka ci gaba da samun kulawa k'arkashin jagorancin BABA SABUWA da tun zuwanta gidan yaran suka koma gurinta,komai ita ke musu idan ka gansu gurin KHUBRA to abincinsu suke nema wanda wani lokacin idan suka tashi tsiya lokaci guda zasusa mata kuka,ba dama ta fara karb'an d'aya sai sauran susa mata rigima,ita kuma abunda ke d'aga mata hankali kenan sai kaga ta fashe da kuka,idan an tambayeta sai tace
_"Ita bata san ya za tayi musu ba,shi kenan babu damar su kyaleta ta huta.."_
Haka za tayi ta fama,har sai BB ya rarrasheta tukun zata hak'ura tayi shiru,wani lokacin ko shima da kansa zai sata gaba yana tsokana musamman idan ta fara kumbura fuska tana k'unk'uni shima haka zai kwanta kan cinyanta cike da shag'wab'a yana fad'in
"MOMMAH....saura PAPA shima yana buk'atar ayi feeding nasa..."
Duk lokacin daya mata haka sakin baki take tayi ta kuka tana fad'in
"Shi kenan kuma na shiga tara..tunda so kuke ku na mutu sai ku kasheni ai sai ku rabani hud'u kowa ya huta.."
Shi ko nan zai sata gaba yana dariya,idan yaga ta tsananta kukan ne zai dena ya kuma koma rarrashinta...Ranar da kyar zai samu tayi shiru har ta sakko daga Fushin da take yi............








*EIGHT YEAR'S LEAP.....*




Kwance take saman bed da waya a hannunta tana latsawa,da ganin alamu kuma chart take,sai dai na d'an sake matsawa kusa dan ganin abunda take yi,nan ko na ganota tana shawagi cikin group en nasu da ba wani yawa gare suba,dan duka bana jin zasu haura su goma..
Hira suke cike da k'aunar kasancewa tare a haka har k'anshen rayuwa.
Shigowar BB yasa ta ajiye wayan a gefenta tana murmusawa.Cike da so da k'auna BB ya kalli KHUBRA data zama babbar hajiya yana kwanciya saman jikinta,cikin wani voice dake kashe mata duka gab'ob'in jikinta ya sake kallonta,ido d'aya ya kashe mata yana fad'in
"JODI yaushe zaki sake bani new baby ne...? ina son sake ganinki da babyna kwance a nan...?"


Ido ta fiddo tana rufe bakinta da hannu ta furta
"Haba MY JAAN....Yanzun har fatan na sake haihuwa kakemin...? yara biyarfa nake da su..Inama laifin kace na barshi haka ai nayi k'ok'arima hakan..."
Y'ar dariya yayi yana fad'in
"Haba mana dan kin bani biyar shi ne kike rakin kinyi k'ok'ari...?"


"Ehh! mana kaima kuma ai kasan nayin indai k'ok'ari ne,kallafa CWEETY har yanzun a uku take,dama dama ma ASHNA da muke kai d'aya,amma itama ai ta rigani haihuwan fari,kuma kana dai ganin CWEETY ko shirin sakewa bata da.Daga maza biyu mace d'aya face ya is a haka..tabbb! ni dai kayi hak'uri hakanma Allah ya raya mana su cikin aminci..."

"To ameen...Amma dai da kin daure kin k'aramin ko dozin biyu ne..."
Yadda tayi da fuska yasa shi kwashewa da dariya,pillow ta d'auka tana dukansa shima ya d'auka yana ramawa,zuwa can kuma suka zube suna maida numfashi game da dariyar farin cikin yadda rayuwarsu ta kasance...
Tsagaitawa tayi da tata dariyar tana shafa fuskarsa,da sauri ya kalleta yana d'aga mata gida alaman tambaya,a hankali ta motsa bakinta cikin coolness
"Kawai YAYANAH idan na kalleka da yaranmu sai na tuna rayuwata ta baya ne lokacin da nake matsayin *Y'AR GARUWA...* sam ban tab'a kawowa rayuwata zata zamo yadda nake a yanzun ba...Alhamdulillah! komai yayi farko da sannu k'arshensa zaizo...yau ni ce kwance jikin mijina abun alfaharina,baya ga yarana dake kewaye da ni a kowane lokaci...Tabbas Allah shi ne abun godiya..Allah na gode maka bisa ni'imomin da kaimin..."
Siraran hawayenta dake mak'ale a idanunta suka sakko.
'Dan murmushi yayi yana dad'a mannata da jikinsa,cikin kunnenta ya shiga fad'a mata magan-ganun da zasu sata ta manta da damuwar da ke neman kunno mata kai,sai da yaga ta ware sosai sannan ya furta

"Tohh! MR'S KHALEED SAFWAN yanzun komai ya wuce ai kuma maganar kin tab'a yin wani wahala da har ya kai ki zama matsayin *Y'AR GARUWA* ina so ya wuce,coz ban son

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads