Header Ads
Showing 87001 words to 90000 words out of 159513 words

Chapter 30 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1225

Ads at the middle of Article

ci amanar hakkin aure to kije ke da Allah,kuma da sannu zaki ga sakamakon tozarta aure da kikayi.
Abu na biyu da zan fad'a miki shi ne,tun wuri kuma muna shaida juna duk inda yarinyata take kiyi gaggawar nemo min ita tare da damk'ata a hannuna,idan ba hakaba zan sauya miki hallita sa'annan in damk'aki a hannun hukuma.
Abu na uku da zan shaida miki kuma na k'arshe shine daga rana irin ta yau ni MALAM BUBA SA'ADU na sake ki saki uku babu ni babu ke,zaki bar gidannan daga ranar da yarinyata ta dawo hannuna ina fatan kin gane ko?"


"Wayyooo Allah ni LADIYO wallahi MALAM baka isa ka sake niba na rantse sai ka zauna dani"


"Ke dakata da Allah idan kin manta abunda ya faru shekaru sha tara da suka wuce ni ban manta ba kin gane ko,ni bani da lokacin b'atawa bare har na tuna miki d'anyen hukuncin da kika sani aikatawa saboda sharri da kuma kaidi irin naki"
Yana kaiwa nan a zancensa ya fisge rigarsa tare da wucewa ya barta a nan tsaye tana faman taraddadin da tasani bata aikata masa abunda tayi ba tun farko yau ga shi abunda hakan ya jawo,tunani ta lula kan maganarsa....


《《》》


Sabuwar kulawa KHUBRA ke samu daga gurin MAMA dan yanzun kam ta mai data kamar y'arta data haifa tsakaninta da su ASHNA yanzun babu wata k'iyayya,sai dai kuma har yanzun ta kasa sakin jiki da su kamar yadda su en suke mata shishshigin ganin ta sake da su.

Ihu suke tayi suna murnan zuwan UMMI da tazo yanzun babu jimawa,bayan sun gaisheta kowannensu suka fashe daga parlor,hira sosai suke tsakaninsu irin ta k'awaye kamar ba sune da suka jima basa tare ba.
"Nikuwa MAMA'N yara da wata alfarma nazo nema gurinki"
UMMI ta fad'a tana kallon MAMA dake zaune tana ta faman sakin murmushi kamar ba ita tayi jinya ba
"Haba UMMI'N yara wace irin al'farma kuma,ai tsakaninmu ya wuce haka,ki fad'i ko me kike so ni kuma in sha Allah babu abunda zaki nema ki rasa a gurina"


"To shi kenan tunda kince haka,dama ba wani abu bane illa ina so ki bani KHUBRA na tafi da ita gidana kinga tunda Allah yasa mukayi aure d'a d'aya kad'ai muka mallaka,ke kuma kina da y'ay'a da yawa,dan Allah ki taimakamin ki bani ita kada kuma kice a'a,saboda ina son y'a mace sai dai Allah bai azurtamu da samun hakan ba"
Shiru UMMI tayi tana sauraren MAMA da itanma dai shirun tayi,ko me take tunani ohoo,sai da ta sauke wani dogon ajiyar zuciya sannan ta fara magana
"To UMMI ni me zance a kan wannan maganar,ina ganin yaran nan ko da bana raye na tabbatar ke kad'ai ce zaki rik'emin yarana saboda haka ko dukansu kike so a halin yanzu ni babu abunda zance miki"


Dad'i sosai UMMI taji dan yadda MAMA tayi maganar ba k'aramin farin ciki tajiba

Suna cikin firan ne driver'n gidan yayi sallama had'e da sunkuyawa


"HAJIYA dama wani ne yace a fad'a muku kuna da bak'o idan kun bada izini zai shigo"

Kallon-kallo akayi tsakanin MAMA da UMMI cikin wani yanayi kuma suka furta
"Bak'o kuma daga ina haka?"....................








*Ku canki waye a waje yake neman izinin shigowa.....* ☺☺☺




_Kuyi hak'uri da wannan wollah mura ke damuna jikina duk a mace yake shi yasa na kasa yin typing en yadda ya kamata...Luv u oll._ ❤








*~#TEAM KHUBRA.~*








*_#REAL SMASHER._*
💠







*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹










*©®2018*
*12/ʝųlყ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
_A kullum kuma a ko wane lokaci ina alfahari daku dan kun rigada kun zame min jinin jiki wanda idan babu ku to lallaine SMASHER bata tab'a moruwa,ina godiya sosai da addu'o'inku gareni,Allah ya bar k'auna.....#1❤ MY PEPs._
*~__________________________~*
_Fan's muna baran addu'anku akwai sister enmu da aka nema aka rasa dan Allah ku tayamu addu'a Allah ya bayyana mana ita.._
*~__________________________~*



*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










*4⃣3⃣*










*K* allon UMMI MAMA tayi kafin ta had'iyi wani irin yahun wahala saboda gaba d'aya tunanin MAMA ya tafi wani nahiya daban.
UMMI ce ta kalli driver'n da yake jiran umarni har lokacin tace
"Kaje kace masa Bismillah! zai iya shigowa"
Da sauri ya fita don isar da sak'on da aka bashi.
Har bayan fitansa MAMA bata koma dai² ba saboda firgicin da take ciki wanda ya hanata magana.

Da sallama ya shigo cikin shiga ta kamala wanda idan har wanda ya sanshi ya ganshi a cikin wannan kayan zai iya tsammanin ba shi bane wani ne daban,sosai kyaunsa ya dad'a bayyana ga wani classy da ya k'ara,har k'asa ya sunkuya ya gaidasu sannan ya zauna a kan rug,k'afafunsa a tank'washe kamar mai d'aukan darasi,wanda bai sanshiba idan ya kalleshi a wannan shigan zai iya tsammanin dama can haka yake.
Shiru cikin parlor'n na wani lokaci,su kuma suna masa kallon rashin sani dan babu wanda ya tab'a ganinsa cikinsu bare ya shaida shi.
MAMA ce taga shirun yayi yawa ta fara magana da fad'in
"Samari daga ina haka mu nan babu wanda ya shaidaka cikinmu"


Kansa ya d'an sosa yana d'an inda-inda dan bai san ta ina zai fara maganaba,kansa a k'asa yana shirin yin magana su BB suka shigo shi da KHALEEL
"Da farko dai HAJIYA ni suna na *SADEEQ* wanda wasu daga cikin mutane ke kirana da *BIGGY* na zone domin baku hak'uri tare kuma da neman gafararku bisa abubuwan da suka faru a y'an watanni sannan kuma zuwa wasu satittika da suka shud'e"


Kallon mamaki duka suka bishi da shi,inda su KHALEEL suka nemi guri suka zauna don jin abunda zai biyo bayan zancen da yake yi.


"A da HAJIYA ni ban kasance cikin mutane masu tausayiba bare imani....."


"Subhanallah!" UMMI ta furta
"Kai kuwa wane irin mutum ne da har kake furta baka da imani,ka san kuwa ma'anar wanda aka ce bashi da imani?
A duk lokacin da aka cewa mutum bashi da imani to tabbas wannan mutumin baya cikin jerin mutane masu imani,saboda ko me ka aikata ka rok'i yafiya daga gurin mahaliccinmu sannan ka nemi yafiyar wad'anda ka zalunta,tabbas ubangiji zai gafarta maka dukkan zunubanka,ina fatan ka gane ko?"


Kai ya kad'a mata sannan idanunsa na fidda hawaye kamar mace yace
"HAJIYA sam abunda na aikata ba shi da alak'a da abunda kike magana,kamar dai yadda kikaji na ambata ni na kasance ina yin aiki na marasa imani,kamar kuma yadda na kasance cikin marasa tausayi had'e kuma da aiki ga mutane marasa imani"


Wani kallo gaba d'aya mutane hud'un dake cikin parlor'n ke masa mai wuyar fassara,gaba d'aya hankulansu na kansa basu da burin daya wuce jin cikakken labarin wannan SARK'AK'IYA.


Dad'a duk'ar da kansa yayi k'asa ya goge fuskarsa sannan yaci gaba
"HAJIYA ni da kuke gani a da na kasance cikin mutanen da suke yin *GARKUWA* da mutane domin neman wani abu ko kuma asasu sace wasu sannan mutane su yasar wani yanki daban
Idan baku mantaba a watannin baya kun nemi y'arku kun rasa wacce kuka jima kuna nema ba tare da kun gantaba
Sannan a weeks da suka shud'e kuka sake neman wata kuka rasa,wanda ita kuma ta dawo gida kimanin sati kenan da samunta"


"Kaii da Allah dakata kada dai kace mana kai ne k'asurgumin b'arawon da ka sacesu duka"


Ba tare da ya kallesuba ya kad'a kai,yin hakan babu b'ata lokaci KHALEEL ya kalli BB daya ke kallon wannan bawan Allah mai matuk'ar k'arfin hali.
"Ammafa kayi k'ok'ari kuma ya zama wajibi a jinjina maka saboda bajintar da kayi,a saboda haka ni kuma nayi tunanin karramaka ta hanyar baka lambar yabo..."


Da sauri KHALEEL ya kalli BB cikin fad'a yana fad'in
"Haba MAN wane irin bajinta kuma?.........wane irin kuma karramawa kake magana ga azzulumi irin wannan?wanda makomarsa bata wuce gidan sark'aba,irin wad'annan mutanen makomarsu ma yaci ace tafi haka muni saboda ayyukansu......"


"Ya isa haka SON,me yasa zaka katse shi daga bayanin da yake yi bayan d'umbin nadama da yayi wanda har ya masa jagora akan yazo neman afuwarmu,ina ganin idan har ba dagaske yake ba babu abunda zai kawo shi gurinmu,mu bashi dama muji dame yazo tukuna kafin a yanke masa hukunci....."
Maganar da UMMI tayi ita tasa su yin shiru kowanne sai huci yake burinsu bai wuce a kyalesu su sab'a masa halittaba ko samu sassauci,idanun BB sun gama rinewa da b'acin rai ga tarin bak'in cikin dakatar da shi da akayi gurin hukunta wannan k'asurgumin mai laifin dake gabansa,kunnuwansa yasa hannu ya toshe duk dan kada yaji abunda ake fad'a idanunsa a lumshe kamar mai bacci haka ya jingina bayansa a jikin sofa...


Kallon matasan samarin BIGGY yayi da suke cike da zafin kai wanda a ganinsu idan har aka barsu da BIGGY to babu abunda zai yi saura a jikinsa..
Sai daya sake kallon mutanen parlor'n sannan yaci gaba
"Bisa wannan kuskure dana aikata a rayuwata kuma bisa ga dalilin had'uwata da d'aya daga cikin y'an matan dana sata zuciyata ta kasa nutsuwa wanda har tayi min jagora zuwa alkhairi,itace ta kawo haske cikin rayuwata wanda yayi sanadiyyar dana yanke shawarar dena aikata duk wani laifi dana ke tawa akan hakane na yanke shawarar dawo da ita gida....."
Daga nan ya kwashe duk yanda suka yi da ASHNA tun bayan daya sace ta da irin damuwar da ta shiga,har kuma yanda yayi nadama kan aikin nasa ya kuma dawo da ita a ranar da sukaje asibiti shi ne lokacin da suka tarar da MAMA'N ta samu sauk'i,sannan ya k'ara da yadda ya tafi ya bar asibitin wanda a ranar babu wanda ya kula dashi
acikin d'akin saboda yadda hankalinsu ya koma kan MAMA...
Shiru yayi bayan ya kai nan a zancensa yana jiran ganin matakin da zasu d'auka akansa.


"Alhamdulillah!da har haka ya faru kuma muna godiya ga Allah daya sa ka shiryu daga mugun aikin da kake aikatawa,abun farin cikine ace wani ya shiryu ta sanadinmu,wannanma kad'ai ya ishemu alfahari da har haka ta faru
Y'anzun shin kana da wata sana'a ne da za kayi bayan dena waccan mummunar sana'ar taka?"


"A'a HAJIYA amma dai zan ci gaba da k'ok'arin nema ko dan ganin ban koma wancan sana'ar dana bariba"


"To Alhamdulillah da haka ya kasance lallai wannan ya tabbatar mana da cewa da gaske kake yi ka tuba daga wannan d'anyen aiki,abunda zan maka albishir da shi shine idan har ka dena abunda kake gaba d'aya ka kuma yi min alk'awarin bazaka sakeba
Ni kuma in sha Allah nayi alk'awarin nema maka aiki,amma abunda nake son ji daga gareka.....shin kayi makaranta ne?"


Sai da yayi murmushin jin dad'i sannan ya furta
"Ehhhh!HAJIYA nayi karatu rashin aiki ne tun farko da kuma sharrin matar mahaifina ta d'orani a wannan hanyan tun bayan dana rasa mahaifana"


"Asshha! Allah ya kiyaye ashema ba hakanan ka fara wannan mummunar sana'ar ba,Allah ya tseratar damu daga sharrin masu sharri amma abu baiyi kyauba
Abun da nake so da kai yanzu shine ina so ka kawo min copy na takardunka nan da sati guda kaji ko,sannan kuma kasa a ranka gaba d'ayanmu mun yafe maka abunda kayi mana,Allah kuma ya yafe mana baki d'ayanmu...."


"Haba UMMI ta yaya zaki saurin amincewa da maganarsa daga fad'an magana har kin yarda,irin wad'annan mutanen wallahi munafukai ne akwai wani mugun nufi da suke zuwa da shi a zuk'atansu,sai su fake da neman yafiya nan ko wani abu suka hango shi yasa suka lallab'o da sun samu nasara zaki neme su ki rasa...."
KHALEEL ya k'are maganar had'e da zabga masa wata uwar harara,wacce shi kam BIGGY baima san yana yiba dan ko kansa a k'asa yake.


Hararar shima ya samu daga gurin UMMI sannan ta masa dak'uwa tana fad'in
"Ungo naka SON wato kai gaka sarkin fitsararru ko?da nace a bar maganar kai ne bazaka iya yin shiru ba kenan,kana gani d'an uwanka yayi shiru amma kai saboda futsara shi ne zaka ci gaba da magana ko?to Allah yasa na sake jin ka furta wata magana wallahi saina sab'a maka kaji dai na fad'a maka..."


Kame bakinsa yayi bai sake yin maganaba duk maganar da UMMI ke yi da BIGGY babu wanda ya kuma ko da tari a cikinsu,har suka kammala maganar da suke,godiya sosai BIGGY yayi musu sannan ya mik'e yayi musu sallama da niyyan komawa,babu wanda ya kulashi tsakanin BB da KHALEEL duk kuwa da yanda ya mik'a musu hannu da zai fita,haka ya fice jiki a salub'e dan sam bai ji dad'in yadda KHALEEL en yake aika masa da kallon tsanaba.....


Dai² bakin parlor yana shirin fitowa ta taho a guje tana waiwaye tana ihu da alama akwai wanda ta tsokano karo tayi dashi da sauri ta maida kanta dan ganin mene ta buga haka,idanunsa na kanta duk da lokacin da ya fito zuciyarsa babu dad'i amma yanzun kam da ya ganta yaji dad'i sosai wanda baya misaltuwa,a hankali ya furta
"BEAUTY......."
Saurin kallonsa tayi dan tunanin inda tasan mai wannan kamannin take sai dai ta kasa ganewa yanzun kam da yayi magana ta rigada ta gama gane ko waye shi en,da sauri ta mik'e daga jikinsa tana fad'in
"Kaiii ne?.......me kuma ya kawoka gidanmu?"


Dariyama tambayanta ta bashi a hankali kuma ya karkatar da kansa gefe cikin wani irin yanayi yake fad'in
"Neman yafiya nazo gurin family enki dama ke kanki"


Idanunta ta sake bud'ewa tana k'are masa kallo saboda yadda ya mata kwarjini a yau,kallon sama ba sosai take iyawaba,kanta a kasa zuciyanta na skipping,ga wani feelings da take ji tattare da shi a lokacin,maganar daya mata ne wancan ranar ya fad'o mata a zuciyanta ta furta
"Kenan dama maganar dayamin kan zai daina abunda yake yi gaske ne?........To amma wane azzalumi ne yasa shi aikata mana wannan rashin imanin.......?"


Duk maganar da ASHNA ke yi batayi tsammanin a fili take yintaba sai da taji ya bata amsa
"K'warai kuwa BEAUTY da gaske ne babu k'arya a ciki....Kina son ki san wanda yasani aikata hakan ne?"
Yayi tambayan yana kallonta
"A'a kawai dai nayi maganar ne amma ba haka nake nufiba"


'Dan murmushi ya sake yi sannan ya furta a hankali
"Noo!BEAUTY nasan kina son sani kawai dai kinamin alkunyane ko?"


Bata ce komaiba taci gaba da murza ring en dake yatsanta,shi dai BIGGY (SADEEQ) yana ta kallonta duk wani abu da za tayi ji yake tana k'ara burgeshi,musammama wannan y'ar kunya da take nuna masa.


"Shin kin san wata mata mai suna HAJIYA LAURA?"
Tambayar ta daki kunnen ASHNA wacce bata yi tsammanin jin hakanba,a firgice ta d'ago kanta tana kallonsa,idanunta ne suka cicciko da hawaye cikin rud'ewa tana inda-inda take shirin tambayarsa,ko kafin tayi magana har ya rigata ta hanyar fad'in
"To itace bak'ar azzalumar data sa muka sace y'ar uwarki wacce muka yar a k'auyen garin ZAKIRAI,sannan kuma ita ce wacce tasa muka sace ki akan wani buri nata da mu bamu saniba....."
Kafin ya kai k'arshen maganarsa tuni ASHNA har tayi fitar burgu ta fad'a cikin parlor tana rusa kuka mai ban tausayi.
Shi ko BIGGY dake tsaye ganin hakan da tayi yasa jikinsa dad'a yin sanyi,a hankali ya juya ya bar gidan,yana tafe yana tunanin halin da BEAUTY ke ciki...


Fad'awa'nta parlor tana gunjin kuka shi yasa BB bud'e idonsa d'aya yana kallonta,ko kafin yayi magana har sun tsinto maganar ASHNA cikin kuka tana bada labarin abunda BIGGY ya shaida mata yanzun.
Da sauri MAMA ta mik'e tana zunduma wani gawurtaccen zagi wanda gaba d'ayansu basu tab'a tsammanin jinsa daga bakinta ba,jikinta sai karkarwa yake kamar wacce ake kad'awa mazari haka ta hau sababi
"Lallai HAJIYA LAURA yau kam kin riga da kin gama janyowa kanki k'arshen bala'i,yau ni HAJIYA MURJA zan nuna miki k'arshen colour ena,saina bar miki darasi a rayuwa wanda ko sunana kika ji an ambata zai sa ki dinga gudu dan neman mafaka......ba dai ni kika tab'a ba shi kenan mu zuba mu gani shege ka fasa yau zaki tabbatar da kin tab'o ......... dodo
Maza ki shirya yau ga maza nan bisa kanki"


Gaba d'aya mutanen parlor'n sun shiga shock idan aka d'auke BB da ya sake maida eyes yayi closing,mamakinsu ya kasa

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads