Showing 72001 words to 75000 words out of 159513 words
Chapter 25 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt
ciwon jikin da take fama da shi cikin satin....
Sai da BABA ZUWAIRA ta tab'ata sannan ta tashi ta zauna had'e da karb'ar maganin tana juyashi a hannunta...
Da kyar ta samu tasha maganin sannan ta tashi da nufi yin sallah....
Tun misalin k'arfe 8:30pm tayiwa BABA ZUWAIRA salamma ta shige d'aki,ita ko BABA'N a lokacin tunaninta duk jikin ke damunta,ta dai bita da fatan samun sauk'i fuskarta duk alamun damuwa da halin da y'ar tata ke ciki...
Ko da ta shiga d'akin bayan ta kwanta nan ta shak'i kukanta har ta godewa Allah...
Sai bayan ta gama kukan ta tsaya tunanin menema wai yasata kuka haka?
Tana wannan tunanin bacci ya d'auketa cike da mafarkai iri-iri....
《《》》
Gari na wayewa suka hau shirin barin garin,misalin k'arfe 10:00am suka yiwa UMMI sallama suka mik'i hanya bayan d'umbin nasiha da suka sha a gurinta sannan ta musu fatan dawowa lafiya...
Sai da suka biya suka ga jikin MAMA,sai daifa har zuwa wannan lokacin MAMA bata sanma wanda yake kanta ba,bare ta samu damar yin magana.....
Daga nan suka d'auki hanya sai garin na JIGAWA DUTSE......
乛乛乛乛乛
Safe trip BB and KHALEEL.....
*~TEAM KHUBRA.~*
*_REAL SMASHER._*
💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*1/ʝųlყ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Matso maza kuji mutanen arziki,wollah a duk inda kuke ina k'aunarku irin wacce bazata fad'uba kuma ina alfahari daku_
*MISS ABATCHA,ZAINAB (ZEE MA'DAGWAS & KHADIJA (FRESH KHADEEY)*
_Kuyi komai ba komai mutanena Allah ya bar k'auna....*ME LUV U* ❤ irin tottaly ennan..._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*3⃣8⃣*
*T* afiya ta mik'a a b'angarensu BB,inda babu wanda ke wata magana hakan ne yasa tafiyan nasu ya zama kamar na kurame...
K'arfe 1:15pm Motansu ya parker k'ofar wani madaidaicin gida,ginin gidan dai² na talaka dake cikin rufin asirin ubangiji,a cikin garin na DUTSE unguwan shiru babu hayaniya,fitowa BB yayi ya tsaya yana tunanin ko ina ne gidan daga cikin jerin gidajen?...
Sun shafe tsawon lokaci suna jira a gurin ba tare da ganin kowaba,sai zuwa can wani d'an dattijo ya fito daga zauren d'aya daga cikin gidajen,da alamun shima kamar gona zai tafi duk da wannan tsufan nashi...
Ganin mota tsaye bakin k'ofar gidan ya d'an kalli motan da mamaki a tare da shi...
Da sauri KHALEEL ya kalli BB
"MAN ya kamata fa mu tambayi wannan datijjon tun kafin mu rasa wanda kuma zamu tambaya"
Kallonsa BB yayi tare da murmushin k'arfin hali,sannan ya sake bud'e motan motan karo na biyu ya fita cikin sauri..
Matsowa yayi kusa da dattijon yayi masa sallama fuskarsa da fara'a,shima dattijon ya mayar masa da murmushin tare da amsa masa sallaman da yayi masa...
Bayan BB ya gaida shi ya amsa masa,sai kuma shiru ya ratsa tsakaninsu,tunanin BB ta ina zai fara masa bayanin abunda ya kawosu,shi kuma dattijon yana kallonsa ne irin na rashin sanin nan...
"Samari daga ina haka?sai dai kuma ban shaida kaba"
Sai da BB ya sake yin wani murmushin kafin ya fara magana
"BABA daga kano muke,to dama akwai wani gida da muke nema kuma dai gaskiya BABA gidan ne ya b'ace mana,saboda shekarun da yawa"
Murmushi dattijon yayi irin nasu na manya kafin ya tambayi BB
"'Dana wane gidane kuke nema haka?"
"Ehhh to BABA gidan MALAM ABDU MAI AL-MAJIRAI muke nema,ko nan ne unguwan da yake?"
Murmushi dattijon ya sake yi masa tare da gizgiza masa kai
"K'warai kuwa nan ne unguwan da yake gama gidan da kuke nema nan kusa da kai"
Ya fad'a tare da nuna k'ofar gidan da ya fito yanzun
"To amma wa kuke nema a gidan shi kuke nema ko wani daban kuke nema?"
Sosai BB yaji dad'in samun gidan da suka yi ba tare da sun sha wata wahalaba,fuskarsa d'auke da jin dad'in hakan ya furta
"BABA yana raye ne ko kuwa?"
"Sosaima kuwa d'an nan,sai dai ya jima yana jinya dan a halin da ake cikima yana kwance ne sai dai a tayar da shi saboda k'afafunsa da suka samu matsala"
"Eyyyahhh!Allah ya bashi lafiya....
Amma BABA idan da hali muna son ganinsa ne dan shi muka zo garin nan"
"To to kada ka damu yaro,bari na shiga na sanar masa da yana da bak'i tukuna"
Da sauri BB ya amsa da
‘’To BABA mun gode sosai‘’
Sai da ya ga shigan dattijon tukun ya juyo,ta saitin window en da KHALEEL yake ya tsaya tare da knocking..
Sauke glass en yayi yana kallonsa
"Yahh!ina fatan dai munyi nasara"
"Sosaima kuwa Allah ya taimakemu wollahi,ashema a k'ofar gidan muka tsaya"
"Kaiiii!ammafa naji dad'i sosai wollahi,to amma KAKA yana raye kuwa?"
Sai da yayi wani k'ayataccen murmushi kafin ya amsa
"K'warai kuwa,sai dai kuma ance bashi da lafiya yanzun hakama"
Yanayinsa ya d'an sauya lokacin da ya fad'i hakan,shima KHALEEL en yanayin da yake kan fuskarsa kenan lokacin da yaji hakan...
"Allah dai yasa ba wani seriuos ciwo ne da zaisa ya kasa fuskantar dalilin zuwanmu ba"
KHALEEL ya fad'a yana sauraron yaji me BB zai ce kan hakan..
"Ameen kam dan wallahi har murnan da nake ya soma b'acewa,gaskiya ina cikin damuwa yanzun haka da naji wannan maganar"
"Tohh!Allah yasa dai babu wani abu da zai mayar mana da farin cikinmu baya"
Suna cikin maganar dattijon ya fito yana waigawa yaga ina saurayin ya nufa kuma,bayan ya barshi tsaye a k'ofar gidan....
A jikin motan ya hango shi ya jingina,k'arasowa yayi da murmushi a fuskarsa
"To samari zaka iya shiga yana sauraren zuwanka"
Kallon KHALEEL yayi da yake k'ok'arin fitowa daga motan,sukama juna murmushin k'arfin hali sannan sukabi bayan dattijon zuwa cikin gidan....
Mata ne da k'ananan yara wad'anda bazasu iya aikin gonaba sunata aikace-aikace a tsakar gidan,gaisuwa kam su BB sun shata musamman da aka gansu da shiga data bambanta da yanayin y'an garin...
Haka sukaita wucewa har suka isa turakar mai gidan,shigansu suka tarar da wani DATTIJO da yafi wanda ya rakosu tsufa a kwance k'afafunsa sun kumbura sosai suna tsatstsafar da ruwa ta jikinsu...
Da tausayawa suke kallonsa wanda duk mai raunin zuciya idan ya kalli k'afafun sai yayi masa hawaye,inda tafin k'afar tasa yayi wani irin sai wata irin sab'a yake kamar jikin maciji.....
Kallon yanayin da yake ciki yasa jikinsu dad'a yin sanyi,dan har sun yanke tsammani da cewa wannan dattijo zai gane duk wani bayani da zasuyi masa a wannan lokacin,sai dai kuma maganarsa ta basu mamaki matuk'a...
"Marhaban lale"
Juyawa sukayi suka kalli juna da mamaki,sannan kuma suka kalli dattijon dake kwance...
Guri suka samu suka zauna,nan dattijon da ya rakosu shima ya samu guri ya zauna daga gefen wannan dattijo dake kwance...
"Samari daga ina haka?ban shaida fuskokinkuba"
Sai da suka sake kallon juna sukayi murmushi tukun BB ya juya ya kalli dattijon tare da fad'in
"BABA mu bak'i ne daga garin KANO,sai dai kuma ba lallaine dama ace ka ganemu ba"
K'ura masa ido dattijon yayi da alama akwai wani abu da yake son karanta akan fuskarsa da har yasa yake masa irin wannan kallon k'urilla,yanayin kallon da yake masa ne yasa shi yin shiru yana binsa shima da ido had'e da murmushi...
"Yaka nan zo maza,matso kusa dani kaji zo?...
Ina ji ajikina wannan yaron duk inda ya fito jini nane shi duk inda ya fito"
Da mamaki suka sake kallon juna shi da KHALEEL,inda KHALEEL en ya d'aga masa kai alamar yaje gurin dattijon...
Matsawa yayi kusa da dattijon,shi kuma sai k'ok'arin mik'ewa yake ya zauna,da sauri d'aya dattijon da ya rakosu ya mik'e ya kamashi ya zaunar...
Hannunsa ya mik'a ya rik'o BB yana dad'a kallonsa...
"Tabbas ko tantama babu wannan yaro duk inda ya fito jinin SAFWAN ne....
Allah sarkin hikima,yaro ina ka baro SAFWAN en?
Yana raye ko kuwa ya mutu ne?
Iya tsawon wannan lokaci SAFWAN ya watsar damu sam yak'i zuwa ya ganmu duk tsayin wad'annan shekaru,ina ya shiga haka?"
Ganin bai bashi amsaba yasa shi sake fad'in
"Yaro ka sanar dani ko dai da gaske SAFWAN en ya rasu kamar yadda nake mafarki?"
A lokacin da yayi wannan maganar idanunsa har sun kawo ruwa,wanda suke shirin zubowa,saboda rashin sanin amsar da za a bashi...
"A'a BABA yana raye"
BB ya fad'a wanda fad'ar hakan yasa KHALEEL ya kalleshi,zuciyarsa cike da tunanin
‘’Too kaji mutumin nan yana neman b'allo mana ruwa,idan har ABBA yana raye a wane bigere yake rayuwa,ko kuwa yasan inda ABBAN yake da har ya fad'i haka?‘’
Saurin katse tunaninsa yayi ya sake maida hankalinsa kan abunda BB zai fad'a...
"Too Alhamdulillah da har kuwa yana raye,amma me ya faru tsawon wannan shekaru ya kasa zuwa ya ganmu bayan yasan muna raye kuma muna cikin garin nan,idanma ace bana raye shin ba ga y'an uwansa nanba da suke ciki d'aya,ko kuwa shi kenan ya yanke zumunci da mu?"
Jin maganar BABA ABDU yayi kamar zubar wuta a jikinsa,cikin zuciyarsa yana jinjina kalaman da zai sanar da BABA a wannan halin da yake....
Sai da BB yayi k'arfin hali sannan ya fara magana,duk wani labari daya shafesu tun daga barin garin har zuwa wannan lokacin da yake zaune a gabansa bai b'oye masaba ya sanar da BABA ABDU,amma banda labarin b'atan ASHNA...
Al'ajabi da mamakin abunda ya faru cikin labarin da BB ya sanarma da BABA ABDU yasa shi kuka yana fad'in
‘’Lallai wannan al'amari daya faru tabbas muk'addari ne daga Allah,Allah ya tsara haka sai ya faru daku a rayuwarku,babu kuma wanda ya isa ya tsallake K'ADDARA.....
To amma ina ita mahaifiyar taku da sauran y'an uwanka da kace suna nan?
A wane hali suke yanzun?kuna tare gaba d'aya a guri d'aya ko kuwa?"
Duka tambayoyin BABA ABDU ya jerowa BB ba tare da ya jira ya amsa wasu ba....
"Ehh!BABA muna tare dasu can garin kano,sai dai kuma ita mahaifiyar tamu a halin yanzun bata da cikakkiyar lafiya,wanda ta kaiga har bata iya shaida wanda yake kanta"
"Subhanallah!wannan wane irin ciwone haka ya sameta?"
"BABA muma dai gaskiya bamu san wane irin ciwo bane,tun da likita ya shaida mana suna buk'atar ganin wani babba daga zuri'ar mu dan suyi magana dasu,to mu kuma babu kowa a tare da mu,shi yasa muka yanke hukuncin nemanku mu sanar muku halin da muke ciki"....
Dattijon dake gefe ne ya mik'e tsaye cikin fushi
"Wato da can baku neme muba sai yanzu da al'amura suka gama cukurkud'e muku kuka lallab'o gurinmu....
To kuma tashi ku d'ebi tsummokaran jikinku ku k'ara gaba mu ba abunda zamu iya yi muku a halin yanzu,muma fama muke da namu mahaifin kun dai ga halin da yake ciki...
Saboda haka maza ku tashi ku koma babu abunda zamu iya yi muku a halin yanzu,ita mahaifiyar taku zata iyayi muku komai ai na rayuwa ciki kuwa harda samar muku wasu dangin uban‘’....
Jikinsu duk yayi sanyi da jin furucinsa,suna sauraron yadda yaketa fad'a..
Shi kuwa BABA ABDU yana zaune yana kallon ikon Allah yadda d'an nasa yake ta fad'a kamar zai ari baki...
Murmushi yayi ya sake kallon d'an nasa da ya kasa yin shiru har zuwa lokacin,ganin bai gane me shirun nasa yake nufiba ne yasa shi yin magana
"Ya isa haka KHALEED"
Kallon-kallo sukayi tsakanin KHALEEL da BB,sannan kuma suka juya suka kalli mutumin dake fad'a ganin yayi shiru a lokacin,suka sake kallon BABA ABDU...
"Banda abunka KHALEED ina kai ina fad'a ga wad'anda basu da laifi?ko ubangiji idan muka masa laifi yana hak'uri damu ya kuma gafarta mana....
Kuma ubangiji baya tab'a kama bawa kan laifin da ba nasaba"
"Kayi hak'uri BABA raina ne ya b'aci shi yasa‘’
'Dan murmushi yayi sannan yayi gyaran murya
"Allah sarki MURJA Allah ya bata lafiya,shi kuma SAFWAN idan yana raye Allah ya bayyana mana inda yake"
Gaba d'ayansu suka amsa da ameen...
"Da gani dai wannan da yake zaune kusa dani shu ne KHALEED ko?"
KAKA ya tambaya yana murmushi shima,duka suma suka murmusa tare da amsa masa,juyawa yayi ya kalli KHALEEL
"Shi kuma wannan abokin nawafa?
Ya tambaya yana y'ar dariya
"KHALEEL suna na KAKA"
"Ahhhh!IBRAHIM KHALEEL kenan...
To Allah ya muku albarka da kuka zo nemanmu bayan lokaci mai tsaho".....
"KHALEED kasa a kira sauran y'an uwanka da mutanen gida yanzu ina son ganinsu"
BABA ABDU ya fad'a yana kallon d'ayan dattijon dake tsaye har lokacin,da sauri ya fita don aiwatar da sak'on BABA....
Bayan wucewar wani lokaci cikin turakar ta d'inke da jama'ar gidan manya da yara kowa ya matsu yaji me BABA zai sanar musu haka mai muhimmanci da ya tarasu gaba d'aya....
Sai da yayi gyaran murya yana jingine jikin pillor sannan ya kallesu d'aya bayan d'aya ya fara da fad'in
"Alhamdulillah da Allah ya nunamin wannan rana da na jima ina sauraron zuwanta a tsayin rayuwata...
Dalilin daya sa na taraku a nan ba komai bane face sanar daku wani muhimmin al'amari game da SAFWAN da iyalinsa,wanda wasu daga cikinku sun sanshi wasu kuma basu saniba"......
Take BABA ABDU ya jaddada labarin SAFWAN da iyalinsa ya sanar dasu da duk wani abu daya faru dashi bayan barinsa garin kamar yadda BB ya sanar da shi,yana gama basu labarin turakar tasa kowa dake ciki ya d'auki salati,masu kuka nayi masu jinjina lamarin nayi...
Bayan wani lokaci aka samu kowa yayi shiru sai jimami da kowa keyi da abunda ya faru...
BABA ABDU ya kalli BB dad'an murmushi a fuskarsa yake fad'in
"Kaga wannan?" ya nuna dattijon daya rako su d'azun
"Sunan sa KHALEED shi ne babba cikin y'ay'ana,sannan wannan shi kuma sunansa SULAIMAN,sai kuma wannan AYUBA kenan,sannan sai mahaifinka,daga shi kuma sai k'anwarsu da ta rasu shekaru bak'wai da suka wuce wato FALMATA"...
Wad'annan kuma ya nuna matan dake gefensa matansu ne,haka yayita nuna masa su d'aya bayan d'aya yana gabatar dasu a gurinsa,sannan shima ya gabatar da shi a matsayin d'an uwansu da basu saniba sai wannan lokacin....
Hira sosai tsakanin mutanen parlor'n anata dad'a gaisawa,sannan BABA ABDU ya sallamesu kowa ya fice aka barsu daga shi sai su BB zaune cikin turakan nasa...
Nan da nan aka tashi girki na musamnan a gidan saboda zuwansu,tarba da karamci kam sun samu gurin mutanen gidan wanda basu tab'a tunanin samunta daga gurin mutanenba.....
*2 DAY'S LATER.*
Kwanaki biyu kenan da zuwansu garin wanda suke sa ran a washe gari za suyi haramar barin garin idan Allah ya kaimu ko dan sanin yanayin da jikin MAMA yake a halin da take ciki ko an samu ci gaba ko kuma akasin haka Allah shi ne masani...
Farin ciki kam suna cikinsa tun daga zuwansu garin har zuwa wannan lokacin,kullum cikin hira suke da KAKA da kuma su BABA KHALEED suna dad'a basu labarin zamansu da ABBANSA,wani abun idan sun fad'a sai dai suyi dariya wani ko har da k'walla saboda rashin tabbas akan ABBA'N yana raye ko akasin haka.....
Yau tun safe suke shirin komawa KANO kamar yadda suka sanar da KAKA dama kwana 3 suka zo da niyyan yi....
Sai da ya had'asu yayi musu nasiha sosai kan su rik'e zumunci...
Sunyi masa godiya tare da alk'awarin dawowa nan da wani lokaci ba mai nisaba...
Sosai yaji dad'in hakan,sannan yayi musu alk'awarin da sun koma zai turo su BABA KHALEED suzo su dubasu...
Sunji dad'i sosai da yadda aka karb'esu,sannan sukayi sallama dasu suka d'auko hanyan dawowa KANON DABO......
《《》》
Kimanin kwanaki biyu (2) KHUBRA bata samu ta fita gurin sana'ar taba kamar yadda ta saba...
Duk jikin ya takura mata da ciwo a kwanakin da yasa ta kasa fita,dalilin da ya sa BABA ZUWAIRA ta dad'a sa ido kenan kanta tana dad'a bata kulawa ta musamman saboda yadda take ganin jikin nata....
Yau ta tashi jikin da sauk'i sosai har tana iya yin komai da kanta....
Tashinta da sassafe ta share gidan ta gyara ko ina sannan ta shiga tayi wanka,ta fito kenan daga toilet en BABA ZUWAIRA itama ta shigo gidan d'auke da robber a kanta...
Sororo ta tsaya kallonta tana kuma kallon gidan,dan tana da tabbacin ita tayi wannan