Header Ads
Showing 111001 words to 114000 words out of 159513 words

Chapter 38 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jul 2024

1235

Ads at the middle of Article

hukuncin da kayi yayi kenan?please dan Allah kayi magana kaga ina jin tsoron kada wani ciwon ya kamaka please.....!"


Murmushin k'arfin hali yayi
"Noo! CWEET SIS babu abunda ke damuna yanzun kam wancan letterma k'arya ne a da ne yanzun kam babu wanda nake so ko yake sona,wancan lokacin ne kawai kuma kema ki kwantar da hankalinki dan wacce nake so en tuni har iyayenta sun mata aure kinga ko bashi da amfani na fad'a,abunda kawai nake so dake ki tayani addu'ah Allah ya yayemin abunda ke damuna...."
Sosai ta gama yarda da maganar daya fad'a cikin wani yanayi na tsananin tausayi take kallonsa idanunta suna dad'a kawo ruwa
"Shi kenan BBNAH amma sam ban so akace haka ya faru da kaiba na so ace ka samu ABINDA RANKA KE SO (SAWWAMATEEY),Allah ya maka canji mafi alkhairi....amma! Amma ai ka fasa tafiyan ko?"


A fili ya amsa da ameen ya kuma tabbatar mata d'aya fasa tuni,a zuciyansa ko fad'i yake "Lallai yaro yarone yanzun ta yarda da abunda na fad'a kenan"

"Amma YAYANAH meya sameka kake tafiya ahaka da alama wani abu kuma na damunkafa...me yasa baka je kaga DR ba kake zaune da rashin lafiya?"
Tambayan nata ya zo masa a bazata shi yasa sai da ya d'auki wasu minutes kafin ya iya bata amsa
"Sorry CWEETY na bige ne a toilet yanzun shi yasa kikaga haka"


"Eyyahhh! sannu YAYANAH nayi tunanin ko wani abun ke damunka daban shi yasa na damu...."


"Noo! babu komai kam ki kwantar da hankalinki yanzunma idan na gama abunda nake yi zanje naga DR ko da wani matsalan da ban wanda ban san da shiba.."

"Yawwa YAYANAH barin je to sai ka dawo Allah ya kiyaye hanya"


Kallon tausayi yabita da shi har ta fice karo na farko kenan da yayi mata k'arya shi kam sam ya rasa dalilinma daya sa yayi mata hakan sai kuma yanzun yake jin haushin kansa da faruwar hakan.Har ya kammala shiryawa ya fito still tafiyan shi bai koma normal ba,duk wanda ya kalleshi zai gane hakan a tare da shi,kaf sai da suka kalleshi ganin yadda yake tafiya a duk'e kamar wani tsohon daya shekara d'ari.d'an dakatawa yayi ya gaida ABBA da MAMA,daga bisani kuma ya mik'awa KHALEEL hannu fuska babu yabo bare fallasa,sauran kuma suka gaida shi,amsawanma da kyar yake yi,ya kama hanyan ficewa daga parlor
Maganar ABBA ta dakatar da shi wanda yasa shi dole ya juyo ya kalleshi fuska a dame
"SON me yake damunka kake tafiya haka....?"


Kafin ya bashi amsa ZUHRA data b'illo daga corridor tace
"ABBA bigewa yayi a toilet yanzun nima muka gama magana da shi..."


"Eyyahhh! Allah ya kiyaye....To amma ina zaka je kuma kana irin wannan tafiyan?"


"ABBA hospital fa yacemin zashi yaga DR ko da akwai wani abun daban da yake damunsa ko...?"


"Ehh to hakanma yayi Allah ya kiyaye gaba"
Da ameen suka amsa duka nan BB ya sauke ajiyan zuciya mai nauyi saboda shi da kansa yasan Allah ne ya taimakeshi da ZUHRA tazo at the right time kuma tayi saving ensa a hannun ABBA da bai san me zai biyo baya ba,side en da take zaune ya kalla sun wani had'e kai da ZUHRA suna matsa phone,a hankali ya juya da niyyan ficewa daga parlor'n again KHALEEL ya sake dakatar da shi ta hanyar fad'in
"Lemme help u MAN,muje tare hospital en"
Ganin yadda idanu suka masa yawa yasa bai k'i amsan tayin KHALEEL enba amma kam da niyyansa yace bai so sai dai ya mazeee suka fita tare inda KHALEEL yake driving ensu har sukaje hospital suka dawo,sai dai duk k'ok'arin KHALEEL na sanin matsalan aminin nasa hakan bai faruba dan BB ya hana DR fad'an matsalan a gaban KHALEEL kawai ya ce masa ya bashi maganin da yake ganin shine zai masa maganin rashin lafiyansa,after kuma suka kamo hanyan dawowa duk motsinsa yana kula da shi kam sam bai yadda da abunda ZUHRA ta fad'a yana damun KHALEED enba kawai dai yayi shiru ne,ko da suka dawo gida BB ya kalli KHALEEL tare da fad'in
"Thnks!..."
Daga haka ya fice bai kuma magana yayi bedroom a nan ya duba prescriptions en nasa,aiko nan ya tsorata da ganinsu.....


《《》》


Kwanaki suna ta dad'a wucewa inda ya zama a lokacin har family en BIGGY sunzo sun kuma gana da iyayen BEAUTY'NSA a take babu b'ata lokaci 3ple ABBA suka tsaida rana dai² da bikin KHALEEL da KHUBRA wanda KAKA ya tsaida da kansa...


Musamman BB ya d'auki hanya bayan dawowansu daga DUTSE inda ya koma don ganin jikinsa da kuma maganan kaishi a duba lafiyan k'afan nasa,tunda yajema da BAFFA'N nasa da maganar ya kalleshi da fuskar damuwa yake fad'in
"Kayya dai takwara nan da kake ganinmu babu maganin da bamu kawo masa ba amma yak'i amfani da shi,shi nan BABA da kake gani magani ko wane iri ne ba sonsa yakeba,shi yasama kaga mun zuba idanu muma tunda babu yadda za muyi..."


"To amma BAFFA kam ai wannan ciwon nasa bana a zuba masa ido bane...ko kuwa bai damu da lafiyar k'afafun nasa bane?"


"Ehhh to nima dai abunda na kasa ganowa kenan,da yake ku y'an zamani ne la'alla idan kayi masa wani dabaran ma samu ya amshi maganin a wannan lokacin,amma muma kanmu ciwon nasa na damunmu kawai dai babu yadda za muyine kuma yak'i yarda akaishi asibiti a duba k'afar..."


"Shi kenan in sha Allah komai zai zo da sauk'i,bari na masa sallama a yau nake son komawa kuma gashi yamma ya kawo jiki..."


Koda suka koma gurin KAKA sallama kad'ai yayi masa sannan ya kamo hanyan dawowa gida,tun daga lokacin ya k'udire niyyan nemo masa magani daga na asibiti har zuwa na gargajiya dan bai san da wanne za a daceba saboda masu iya magana kan ce "idan dama yak'i to sai a koma hagu"


Neman magani yayita yi bayan dawowarsa sai daya tabbatar ya samu magungunan daya aminta dasu sannan ya kama hanyan komawa garin,da taimakon Allah ko bayan gumurzu da suka sha da KAKA ya amince ya karb'i prescriptions en dan kafewa yayi akan magungunan suna kisa shi ko haka kawai bai shirya mutuwa yanzuba.....


_Kunjifa KAKUS da gigin tsufa...._




Lokaci baya jira sai dai a jira shi,haka yake inji masu iya magana kuma su kan ce "duk abunda kaga bai zoba to tabbas ba a sa masa lokaciba" k'warai kuwa dan ko idan har ansa masa lokaci sai ya zo kuma harma ya wuce.


Biki nata dad'a matsowa ko wane gefe suna shiri babu ji bare gani,zuwa wannan lokaci duk wanda yaga ASHNA da BIGGY sai ya so sake kallonsu saboda soyayya,shak'uwa gami kuma da yarda da juna dake tsakaninsu,b'angaren su KHALEEL kuwa ba a cewa komai saboda sanin su nasu tsarin ba irin na kowa bane abun dai sai wanda ya gani,biki na k'aratowa amare da angwaye hidimomi sai dad'a shan kawunansu suke haka lokacin yaci gaba da kusantowa..........












*COMMENT FOR MORE PAGE'S......*
💃💃💃








*~#TEAM KHUBRA.~*








*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠







*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*




🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹










*©®2018*
*24/ʝųlყ,2018*






*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹




_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*




*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_




*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._










5⃣2⃣










*Y* au gaba d'aya abunda yayi saura a kwanakin da suka rage musu baifi kwanaki goma ѕhα hud'u ba,duka gidan ya dad'a hautsinewa,kowa ka gani ba shida lokacin zama aikace-aikace da hidima duk sun sasu gaba,hatta da su kansu amaren ba wani lokacin zama garesu ba,yau suna nan gobe can.

Cikin mota suke tafe sai surutu suke su uku KHUBRA,ZUHRA sai kuma ASHNA,shi kansa KHALEEL da yake driving hiran nasu har hawan masa kai yake saboda yawon da suka sha yau gashi duk ya gaji,ba shida burin daya wuce su isa gida ko Allah zaisa ya samu nutsuwa.
Daf da sallan isha suka iso gida,yana ajiyesu ko bai tsaya hiraba yayi musu sallama gami da juyawa,su kansu da yake a gajiye suke da shigansu gida,basu tsaya ko inaba sai d'aki,a kan bed ZUHRA ta zube tana fad'in
"Wash! wallahi duk joints d'ina ciwo sukemin haka wannan yawon raba I.V en yake....tabbb wallahi idan na tashi aure bazan iya wannan wahalarba,gara mutanen kada su zo."


ASHNA dake zaune kusa da ita ta kalleta tana fad'in
"Lallai yarinya ce ke,ta ina zaki wani sakowa mutane zancen aurenki bayan samarinma koransu kike,kenan wai gaki malama to waima ni da wane suna zanna kiranki ustaziya ko me....?"


"Ke kika sani kuma wannan,ni rabani da SAMARIN BANA (ASY KHALEEL) ba komai a cikinsu sai k'arya kamar ragowar yak'i....Fatan dai Allah ya zab'a mana mafi alkhairi.."


"Wollahi kin gama magana tunda kika nemi zab'in mafi alkhairi,da sannu zaki ganshi wollah...."
KHUBRA ce tayi maganar dan duk hiran da suke bata sa bakiba sai lokacin,saboda lokacin da suka shigo tana k'ok'arin cire kayanta,shirin shiga wanka ta gama nan ko tayi hanyan toilet..


Mintuna k'alilan ta fito jikinta jik'e gada ita sai towel iya cinyanta,sai k'arami data d'aure kanta ta gaba ya bada shape na harafin V.
"Ha'aaa! ya kuma naji kunyi shiru ko har kun gama hiran ne?"
Ta tambaya tana coge k'afa d'aya,ASHNA dake faman chart ta juyo tana kallonta
"Uhmm! nikam abunda nake yafi min wannan firan da kike magana"


Dariya tayi dan tasan me take nufi,batayi maganaba ta wuce tana fad'in
"To ai sai ku tashi kuyi wankan dan ni ina gama abunda nake kwanciya zanyi.....wallahi dana shiga wankan nanma kamar kada na fito saboda dad'in ruwan da naji...."


"Kina iya komawa ai in yaso sai muyi using wani toilet en.."
Hankalinta na kan waya tana chat take bada amsa,da sauri ko ASHNA ta kalleta ehfa tunda ke baza kiyi wankanba ai kya fad'i haka dubi irin gajiyar da muka kwaso amma nice haka,bari kiga ke idan kin gama chart en kyayi nan da talatainin dare"
Wayan ta ajiye tana shirin core kayanta,kafin tayi yunk'urin mik'ewa ai har ZUHRA ta dire a guje ta shige toilet en,baki ASHNA ta saki KHUBRA ko me za tayi mata ba dariyaba,tana cikin dariyan aka bud'e k'ofan hankalinsu duka ya tafi kan k'ofa suna son ganin waye haka babu knocking ya danno musu kai..
FATAHIYYA ta shigo tana fad'in
"BRIDE AUNTIES.....Ashe kun dawo amma ko ku nemeni..shi ne kuka gudo nan kuna hira babu ni..."


"Allah sarki k'anwarmu yi hak'uri kinji shigowanmu kenan muma.."


"Kai AUNTY KHUBRA shigowa'nkufa kenan kika ce bayan gashi nan har wanka kikayi kinga kenan kun jima da dawowa...Shi kenan ai tunda kuna nuna min triberlism dama ni nasan ba wani damuwa kukayi da niba....wa ya sanima ko idan kunyi aure zaku neme ni..."
Fuskanta a shagwab'e tayi maganar cike da nuna damuwa


"Yi hak'uri kinji....me zaisa mu kuwa bazamu nemeki ba,k'arewa ma ni dake tare zamu tafi kinji..."
KHUBRA tayi maganar tana rik'e hannunta..


"Su tafiya tare manya,ai ga hanya nan zaku iya abunda yafi hakama...Amma ko dai angon a ranar zai ce ku koma inda kuka fito.."
Yanayin da tayi maganar yasa su darawa dukansu,dai² lokacin kuma wayan dake saman mirror ta hau ruri,kallon gurin KHUBRA tayi had'e da tab'e baki,banza tayi suka ci gaba da hiransu har kiran ya katse,zuwa can aka sake kira nanma wayan sai ring yake
"Haba sis kina jifa ana kiranki kuma kin share kamar ba ke ake kiraba..."
ASHNA tayi magana cike da tuhuma kuma take kallon KHUBRA'N da tayi kunnen uwar shegu kamar bada ita take ba.Ganin bata da niyyan motsawa yasa ita ASHNA'R nufan gurin da wayan yake ta d'auka tana duba mai kiran,YAH KHALEEL ta gani a rubuce saman phone en sai lilo sunan yake
"Ungo ni YAH KHALEEL ke kirankima ashe kika wani share kamar bake ba,nifa wannan gulmar ne banso idan zaki amsa ki amsa,mata tana so sai wani kaucewa kike...Allah yasa ayi ai auren nan naga yadda zaki yi..Ni wallahi har so nake naga yadda zaki koma idan anyin auren..Zaki ci gaba da yi masa duhun kai ne ko kuwa ya za ayi nema ohoon muku..."


Ita dai KHUBRA shiru tayi mata bata tankaba sai wayan data karb'a ta ajiye gefenta ba tare da tayi tunanin d'aukaba,saima hira da take k'ok'arin sako musu.
FATAHIYYA ta kalleta lokacin da kira na uku ya shigo wayan nata
"AUNTY da kin d'auka kinji me zai ce miki...Kinga yanzun kada kisa shi tunanin ko wani abu ya faru..."


"Ke kyale shi ai yasan a gajiye nake ni kuma yanzun baran iya d'aukaba.....Dan yanzun yana ganin na amsa zai tsare ni da surutu ni kuma gaskiya bacci nake ji...."


"Aifa shi yasa naga kinyi baccin yanzun..kina nan kin wani yi gwaraf a gaban k'anwa zaku dasa surutu shi ne harda wani cewa bacci kike ji....Allah dai yana kallonki kuma sai dai ki tunasar da wani wulak'anci babu kyau.."


Ita dai FATAHIYYA tana kallonsu idan wannan yayi magana ta juya ta kalle shi idan wannan ya amsa sai ta sake juyawa,rashin d'aukan wayan da KHUBRA tayi yasa FATAHIYYA d'auka a hankali ta furta
"Hello! YAH KHALEEL ina wuni....?"


"A'a FATAHIYYA ya kike...? Ina AUNTY'NKI fa?"


"Lahh! YAH KHALEEL damafa gani nayi kana kira ita kuma tana shigowa tayi bacci.."


"Ok! to shi kenan na gode k'anwata,da safe mayi magana da ita dama kiranta nayi naji lafiyanta,amma tunda tayi bacci shi kenan kada ki tasheta,na gode sosai.."


Sallama sukayi ta ajiye wayan,sai lokacin hankalin KHUBRA ya kwanta saboda tunda ta d'auki wayan hankalinta bai kwantaba sai da taji sunyi sallama kuma duk abunda suka fad'a taji tunda wayan a handsfree ta sata.
Ajiyan heart tayi ASHNA kam shiru tayi musu amma lamarin na KHUBRA na bata mamaki musamman da auren ya dad'a gabatowa..
Bata kuma kulasuba har suka gama abunda za suyi k'arshe kuma kowacce ta kwanta.Ita dai tana kan waya suna chart da nata prince en kuma tana cikin garin ciki........


*ONE WEEK TO MARRIAGE....*


A gurguje ya fito daga mota ya nufi cikin gida dan dama a kwai abunda ya shigo dashi yanzun da yake ta sauri kada wani ya tsaida shi.
Karo suka yi da sauri ya d'ago dan ganin me ya faru haka,kallonta ya tsaya yi ganinta yake kamar cikin mafarkin daya saba a y'an kwanakin da auren nan ya matso,sam baya son abunda zai had'a shi da ita bare ya kawowa ransa wani tunanin ko yasa damuwanta a ranshi,sai daifa hakan da yake ba k'aramin azabtuwa yakeba,duba da yadda rashin ganin nata ya dad'a jefa shi cikin wani hali,ganin da ya mata a yanzunma duk da a rashin sani hakan ya faru,sosai ta dad'a yi masa kyau musamman da bai gantaba cikin y'an kwanakin da suka wuce,kamar an dasa su zuciyarsa sai sak'a masa abubuwa da dama take a kanta,cikin sauri ya d'auke kansa tare kuma da ci gaba da tafiya abunsa..
Kallonsa kawai tayi ta tab'e baki sannan ta juya tana tafiya abunta zuciyarta na fad'in
"Anya ko YAH ba wani abu ke damunsa ba?...Ko kuwa dai ni kad'ai nake ganin haka?....To amma idan har ba gizoba naga ya rame sosai ba kamar yanda na sanshiba...."
Da sauri kuma ta d'age kafad'a tana fad'in
"Kai to ni ina ruwana ma da damuwa'rsa....Shi ya sani ko wani abu na damunsa...Can ta matse masa ni banda damuwa...Allah yayi mutum sai d'an karen nunk'ufurci..."
Hanyan guarding ta nufa tana shiga ta nemi guri ta zauna,bata jima ba a gurin ko ZUHRA ta shigo gurin
"Ki ce nan kika yo yau kuma nan kika tuno bayan da kin daina zuwa"


"Ehh fa na gaji da zama cikin d'aki ne kawai shi yasa na yanke shawaran zuwa nan nasha iska....
"Wallahi dai kam nima haka nan nake jin zuwa nan yau shi yasa na fito ban kuma yi tunanin kina nanba..."


Suna cikin hiran motan KHALEEL ta kunno kai da sauri KHUBRA ta kwanta a k'asa saman grasses en tana rufe ido,dan ita kam bata son surutun KHALEEL a yanzun sam bata shiryawa jinsu ba,a nan ya tarar dasu shima ko ya zauna,mafi yawanci hiran tsakanin KHALEEL da ZUHRA ne dan dama ita ce abokiyar kuma y'ar rakiyar zance duk lokacin da yazo hira.Ita kam KHUBRA ko magana yayi mata amsanta tsaf sai mutum ya k'irga su saboda yadda take magana a tak'aice..


Labari suke sai dariya suke duka ta window ya hangosu su uku a cikin lambun,da yake

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads