Showing 75001 words to 78000 words out of 159513 words
Chapter 26 - YAR GARUWA COMPLETE.BY REAL SMASHER.-1.txt
aiki...
K'arasowa tayi cikin gidan tana son yin magana...
"Sannu da dawowa BABA"
"Yawwa y'ar nan"
Ta fad'a tana bin KHUBRAN da kallon mamakin yadda ta ganta,bayan a kwance ta barta ta yaya kuma yanzun zata ganta ta mik'e kamar ba itaba...
"Sannu kin tashi?"
"Ehhh!wallahi BABA,ai jikin da sauk'i sosai har ina jin yauma zan iya fita"
Da sauri BABA ZUWAIRA ta katse ta tana fad'in
"Haba haba KHUBRA me zai hana ki k'ara hak'uri zuwa jikinki ya sake warwarewa,in yaso sai ki fitan ko kuwa?"
Cike da tab'ara irin ta y'ay'an fari kuma na k'arshe ta hau buga k'afa tana fad'in
"Ni wollahi a'a ban yardaba,nafa samu sauk'i sosai"
Kallonta BABA ZUWAIRA take tana sake bud'e ido tana kallon ikon Allah
"To ai shi kenan tunda kin dage Allah ya bada sa'a,kuma Allah ya k'ara sauk'i kinji"
Tsalle ta hau yi sosai tana ta murna BABA ta amince mata zata koma gurin sana'ar tata....
Cikin zumud'i ta hau shiryawa,yau da yake ita take son fitan bata b'ata lokaciba tayi ta gama shirinta,sannan tayiwa BABA ZUWAIRA sallama,dai² lokacin itama ta gama shirinta tana jiran al-majiran da zasu d'ibar mata kayan abincin zuwa bakin kasuwa....
Tafiya take cike da kuzari had'e da karsashi saboda yau kam tana jinta cikin k'oshin lafiya,sai dai d'an abunda ba a rasa ba da yake damun zuciyarta....
Har ta k'arasa bakin rafin ta d'ebo ruwa,ta kuma juyo don komawa cikin gari,tana tafe ta kare kanta da hat ta gargajiya saboda rana da ake tsulawa ga zafi.....
Yayinda wani gefen na sararin samaniya ya had'a hadari wanda yake ta gangamowa lokaci guda har garin ya had'e,da alamun yau kam za a iya dacewa da ruwan sama....
Wani iska ne ya taso mai k'arfin gaske,wanda sakamakon haka yasa wasu daga cikin mutane suketa guje-guje,bayan k'uran ya lafane kuma wani iskar cike da yanayi mai dad'i ya sake tasowa...
Cikin nutsuwarta take tafiya tana kuma ci gaba da tura kuranta ita d'aya a hanya....
Wani bak'in PRADO ne ya yanko kan kwaltan da mugun gudu sosai,dai² kafin motan ya k'araso inda take aka tsaya,tare da jan brake da k'arfi wanda ya bada wani mugun sauti ji kake KUUUUUUUUUUUU!!!...............
*_~KEEP FOLLOWING.....~_*
*~#TEAM KHUBRA.~*
*_REAL SMASHER._*
💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*2/ʝųlყ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Jinjina ga d'aukacin mabiya novel en *"Y'AR GARUWA"* a duk inda kuke ku en masoyanane na hak'ik'a,ina godiya sosai da k'aunar ku gareni Allah ya barmin ku a duk inda kuka kasance ina al'fahari da ku.._
*~__________________________~*
_Mun gani kuma mun yaba,danko hausawa na cewa "yaba kyauta tukuici" tabbas garemu muma hakan take,sanin masoyi sai Allah *CWEET LEEMA* muna godiya tare da jinjina gareki lallai ke d'in ta daban ce,ki jima kiyi k'arko a kullum kuma a ko ina SMASHER da HUBBEEY naki ne ke d'aya,Allah ya bar mana zumuncinmu daga nan har a Al-jannah muna fatan ci gaba da kasancewa tare.._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*3⃣9⃣*
*T* ana daga gefen titin tana ci gaba da tafiyanta wanda jin k'aran motan da tayi baisa tayi yunk'urin tsayawaba saima ci gaba da tayi kamar ta samu sak'on k'in tsayawar.
Yanayin yanda garin yake ne ya bata damar k'ara sauri saboda wasu irin thunderstorm da ke tashi akai-akai.
Tsayawan da motan yayi a dai² lokacin hakan ya farune sakamakon motan dake fidda hayak'i bayaga engine en motan da ya d'auki zafi,fitowa suka yi suka bud'e gaban motan ko dan su samu hayak'in ya sarara,wannan dalilin shi yaja musu tilas suka tsaya a gefen hanya'n.
Bayan motan suka duba cikin irin galan da masu mota ke zuba ruwa saboda gudun ko ta kwana irin wannan a tafiya.
Shiru sukayi suna kallon juna,saboda rashin ruwan a tare da su sannan suka kuma maida hankalinsu kan hanya'n da yarinyan nan tabi,can nesa dasu sosai suka hangota dan kam tsakaninsu da ita da tazara mai nisa.
"MAN wai ya zamuyi ne kam kanafa kallon yadda garin nan yake dad'a had'ewafa kuma ka tsaya anan kana wani kallona"
Harara BB ya bankawa KHALEEL dake magana,yanayin yadda yayi masa ne yasa shi shek'ewa da dariya,sai da yayi mai isarsa sannan ya kama hanya cikin sauri don tsayar da ita tun kafin ta b'acewa ganinsu.
Cikin sauri yake bin bayanta wanda da k'yar ya samu ya isa bayanta a dai² lokacin da take k'ok'arin karkatawa ta shiga hanyan da zai sadata da cikin gari.
Sallama yayi mata yana daga bayanta dan yasan hakan dai shi ne kad'ai abunda zaisa ta tsaya.
Cikin sa'a kuwa ya samu ya tsaya tare da juyowa don ganin waye ne mai maganar duk da tasan hanyan babu mutane sosai,duba da yanayin da aka tashi da shi a garin.
Idanu KHUBRA ta bud'e sosai ganin fuskar dake tsaye gabanta,tunani ta d'an tsaya yi kanta d'age a sama tana son tuna inda tasan fuskansa.
Magana yake yi wanda sam ta kasa bashi amsa saboda yadda ta lula duniyar tunani,har sai da yayi magana da d'an k'arfi sannan tayi firigigit da dawo duniyar da take tare da fad'in
"Ammm!kace mene?"
Shiru yayi yad'an tsaya yana binta da kallon mamaki da kuma tunanin inda yasan mai wannan muryan,kallo sosai ya k'ureta da shi sai dai bai gano komai kan fuskartaba,dalilin daya katse shi kenan daga tunanin da yake.
Yana shirin yin magana BB ya iso gurin yana fad'in
"MAN lafiya ka zo ka zauna ka wani shanyani a jeji bayan kana ganin yadda garin yake"
Shiru yayi lokacin da ya k'araso ya gansu tsaye suna kallon-kallo tsakanin su.
Kallonsu yayi sun kafe juna da ido,a hankali KHUBRA ta maida kallonta kan BB da isowarsa gurin kenan,dad'a fiddo idonta waje tayi da sauri kuma ta maida kanta k'asa had'e da dafe chest enta jin yadda zuciyanta keta skipping kamar zai fito waje.
Tun daga sama har zuwa k'asa BB yake kallonta a zuciyarsa yake magana
"Ina nasan mai wannan kamannin?anya ko itance ko kuwa mafarkine nake yi?"
Sake kallonta yayi da yadda take tsaye jikinta na vibrating da gani kasan akwai abunda ya bata tsoro wanda yasa ta shiga yanayi irin na rashin gaskiya haka,da sauri ya katse shirun ta hanyar magana da ya sasu kallonsa
"Ammm!baiwar Allah taimako muke buk'ata"
Ba tare da ta kalleshiba ta furta
"Taimako akan me kenan?"
Sake kallonta yayi yanzun kam ya samu shaida ta biyu da take bayyana masa hasashen da yake yi akanta,abu d'aya yake nema don tabbatar da gaskiyar lamarin.
"Muna buk'atar ruwane zamu sa a mota,mun d'an samu matsala ne so motan yana can kan hanya"
Har lokacin duk maganar da yake yi yana yine idanunsa na kanta,yayin da ita kuma duk take jinta a takure saboda yadda take jin idanunsu a kanta.
KHALEEL ya koma kamar wani idol yayi shiru yana sauraren muryanta dake masa yawo cikin kansa,so yake ya tuna inda yasan wannan muryan,yayin da a b'angaren BB shima hakan take dan shi kam gani yake a yanzun yana da yak'inin itance da kashi 50%,babban abunda yasa bai gama amincewa da itanceba ganin yadda wannan take b'aka,ga yanayin suturan dake jikinta sannan ya tsinceta cikin yanayin da baya tunanin KHUBRA zata shiga.
Duk sunyi shiru har sai da yayi k'arfin hali tare da danne zuciyarsa kan lallaifa wannan ba waccan KHUBRA'N da suke tsammani bace,kawai dai yanayin halittane da kuma su d'in da suke cikin yanayi na rud'u yasa suke ganin kamar itan ce da gaske.
Kautar da tunanin yayi tare da fad'in
"Amm!ina fatan dai ba zaki damuba dan da d'an tafiya tsakanin nan da gurin da mukayi parking"
"A'a babu komai,muje kawai"
Ta fad'a tana juya akalar kuran nata da niyyan komawa bayan garin inda suka bar motan nasu.
A baya suka shiga binta tana tura kuran nata,duk wani motsi nata akan idanunsa hakan yake yana ankare da ita,suna tsaka da tafiyan ne wata matashiya ta taho kanta d'auke da robber yellow da alama daga rafi take ta gansu suna tafiya,kallon mamaki tabisu da shi kafin tayi magana
"A'a KHUBRA ina kuma zaki nufa haka bayan kin d'ebo ruwan kike k'ok'arin komawa"
Cak!KHUBRA ta tsaya a gurin kamar anyi pausing enta ba tare da ta k'ara one step forward ba.
"Shi kenan HAFSAT kin tonamin asiri,wayyyo Allah ka kawomin d'auki"
Abunda ta furta kenan k'asa-k'asa idanunta a runtse ba tare da tayi tsammanin wani cikinsu zaiji me ta fad'aba.
A hankali ya furta
"ALHAMDULILLAH ALAA KULLI HALIN!
ALHAMDULILLAHIL-LAZIIY BI NI'IMATIHI TATIMMUS-SALIHAT!!!"
Yanzun kam ya gama samun shaidan da ya bayyana masa itan ce dai wacce yake hasashe d'ari bisa d'ari yanzun ya tabbatar da hakan.
"Amma to ya akayi ta koma haka ne kam?"
Yayima kansa tambayan ba tare da tunanin samun amsa daga gare shiba.
Matsawa yayi a hankali ya d'auke hat en dake kanta tare da sake k'ureta da kallo,ko tantama baya yi yanzun kam daya ga fuskarta ya gama yin amanna akan yak'ininsa gaskiya ne.
"Why KHUBRA zaki nuna baki ganemuba a yanzun?me yasa?me yasa za kiyi haka??"
Cike da tsawa ya k'arashe maganar tasa.
Kuka ne ya kufce mata wanda daga ji kasan mai yinsa cike yake da fargaba da kuma tsoron halin da take ciki,ta jima tana kukan wanda su dake tsaye gurin suka kasa magana sai kallonta kawai da suke yi,ganin bata da niyyan dainawane yasa KHALEEL yin magana
"Ina tunanin yanzu kam ba kuka ne abunda ya kamata kiyi ba,godiya ya kamata kiyiwa Allah da yayi sanadiyyar had'uwarmu,kafin mu wuce gida kuma"
"A'aaaa!! babu inda zani........ni kam babu inda zani........bazan biku ko inaba.........kawai kuyi tafiyanku ku k'yaleni a nan.........bazan biku ba!"
Ta fad'a lokacin da kukanta ya dad'a tsananta,tana ta kuka mai tsuma zuciya.
HAFSAT dake tsaye har lokacin duk abunda ya faru akan idonta,duk wani furucinsu da maganganunsu ya tabbatar mata da akwai wata alak'a tsakanin wad'annan samari da *KHUBRA Y'AR GARUWA* ,cillli tayi da robber dake kanta take ta felle k'afafunta ta yanki hanya sai cikin gari,gudu take shek'awa wanda ba ita ta tsaya ba sai gaban BABA ZUWAIRA dake ta hada-hadar sallamar customer's,cike da haki take maganaa
"BABA kiyi sauri ga KHUBRA can a bayan gari da wasu samari sai kuka take yi kuma"
Ambaton sunan KHUBRA da tayi shi ya dakatar da ita daga abunda take yi ta mik'e tsaye cikin firgici dafe chest enta
"Y'ar nan maza sanar da ni inda kika ganta tun kafin wani abu ya sameta"
Cike da rud'ewa take musamman jin ance KHUBRA'N tana kuka shi ne babban tashin hankalinta saboda tunanin BABA ZUWAIRA a wannan halin samarin tareta sukayi zasu mata "FYA'DE".
HAFSAT a gaba BABA ZUWAIRA a bayanta yayinda tayi k'wallo da kayan abincin ta marawa HAFSA'N baya sunata faman fakaka sauri kamar wad'anda zasu tashi sama..
Kukanta take tuk'uru yayin da ta kuma jajirce kai da fata ba inda zata bisu itakam,suna tsaka da wannan tak'addamar su BABA ZUWAIRA suka iso gurin,har kuma lokacin ta kasa yin shiru daga kukan da take yi.
"Y'ar nan ina fatan kina lafiya"
BABA ZUWAIRA ta fad'a tana shafa jikin KHUBRA'N dake tsaye.
Da sauri KHUBRA ta k'ank'ameta tana sake sakin kuka
"Ni bazan bisuba,a nan zan ci gaba da zama gurinki"
Maganarta ta d'aurewa BABA ZUWAIRA kai cike da mamaki ta d'agota suna kallon juna ta kuma furta
"Yi shiru ki sanar da ni,ina ne baza ki bisu ba?"
"Gida zasu maida ni,ni kuma ba zan bisu ba,ni gaskiya a nan zan ci gaba da zama gurinki"
Kallonsu tayi d'aya bayan d'aya,sai yanzun ta soma d'aukan haske game da lamarin nasu da kuma inda maganar KHUBRAN ta nufa,cike da jin dad'in Allah ya kawowa y'ar tata k'arshen wannan rayuwar k'uncin take fad'in
"ALHAMDULILLAH!Lallai Allah shi ne abun godiya a kowane irin yanayi,Allah ya amshi rok'onmu da addu'o'inmu da muka jima munayi,Allah mun gode maka"
Idanunta d'auke da k'wallar farin ciki take ta magana,kafin talli KHUBRA
"Bai kamata muci gaba da tsaiwa a nanba,muje gida tukun sai muyi magana ina ganin hakan zaifi"
Fuskarta d'auke da wani irin expression da ba zai fassaruba suka mik'i hanya da niyyan komawa cikin gari,inda KHALEEL yayi saurin zuba ruwa a motan ya biyo bayansu dan su kam har sunyi gaba basu tsaya jiran shiga motaba....
《《》》
Shigowanta gidan kenan daga hospital,shima daga dukkan alamu ta dawone dan yin wasu uzurorin kafin ta koma.
Wayanta ne ya shiga kuka a parlor saboda nan ta ajiye hand bag en da ta shigo da shi yanzun,tana shirin shiga kitchen kasancewar gidan babu kowa duk yaran sun tafi skul saboda yau en ta kama monday ne shi yasa take ta komai cikin sauri duk dan ta kammala kafin dawowarsu.
Kukan wayan da ta jiyo shi ya fito da ita daga kitchen en cikin sauri ta d'auka dai² lokacin da kiran ya zama missed,d'an janye key en tayi sannan ta duba number da aka kiratan da shi,kafin tayi wani yunk'uri wani kiran ya sake shigowa cikin sauri ta d'auka
"Assalamu alaikum!SON mutanen DUTSE ince dai ba cewa za kayi kuna hanya ba ko?"
Sai da yayi wani murmushi mai cike da sauti wanda yake nuna yana tattare sa tsantsar farin ciki sannan ya amsa mata
"UMMINAH barka da safiya da fatan duk kuna lafiya"
"Lafiya k'alau muke SON ya mutanen gidan?"
"Wallahi suna lafiya UMMI duk suna gaidaku"
"Muna amsawa kun samesu lafiya dai ko?"
"Ehh!to lafiya k'alau dai za ace,amma dai kam UMMI KAKA ba shi da lafiya kuma ya jima cikin ciwon,ya jikin MAMA?"
"Too HAJIYA MURJA dai kam da sauk'i za ace,ammafa har yanzun tana nan kamar yadda kuka tafi kuka barta,bata san waye akanta ba ni kam wannan ciwo nata yana bani mamaki wollahi,yanzun jiran dawowarku nake muji yanda za ayi gaskiya ciwonta baya buk'atar a zuba ido hakanan,tunda nan en babu wani ci baba da ake samu"
"To UMMI in sha Allah muma muna nan kan hanya nan da anjima kad'an,yanzunma akwai wani abu ne mai muhimmanci da ya tsaidamu,amma idan mun k'araso za kiji labarin koma mene ne wannan abun"
Sai da tayi murmushi sannan ta ce
"To SON Allah ya kawo ku lafiya kuma Allah yasa muga Alkhairi"
Su duka sukayi dariya sannan ya amsa da "Ameen" yayi mata sallama akan sai sun k'araso...
《《》》
Yau tun da ta tashi jikinta yayi zafi saboda zazzafan zazzab'i data tashi da shi,kusan sati uku kenan tana fama amma ta kasa fita taje asibiti ko dan samawa kanta sauk'in ciwon dake damunta..
Shigowar babban mutumin kenan ya shiga cire kayansa kamar ko wane lokaci da hakan ya zame masa d'abi'a,da duk inda yaje ya dawo tofa yana shigowa zai hau tub'ewa kamar wani k'aramin yaro dake son mahaifiyarsa tayi masa wanka.
Saman gadon ya shiga haurowa yana shafata kafin ya d'age gefen duvet en data rufu da shi,cikin jikinta ya shiga k'ok'arin shigewa,ita kuma sai dad'a matsawa baya take saboda a yanzun kam bata jin zata iya tab'uka komai a rayuwanta,sosai ya manna jikinsu da juna duk uban zafin da jikinta yayi hakan bai hana shi fara abunda ransa ke soba,cikin wahalalliyar murya ta bud'e baki iya k'arfinta
"Dan Allah ka k'yaleni yau kam bana jin dad'i gaba d'ayafa kana jin yadda jikina yayi zafi ko wanka na kasa yi saboda rashin k'wari da jikina ke fama da"
Duk maganarta hakan baisa ya saurara mataba,saima shinshinata da yake yana wani fiddo da harshensa kamar kare tare da sakin wani irin numfashi.
"Kinsan dai a yanzu kam yadda nakai wannan matakin ba zan iya jurewaba,babu wani hak'uri da zan iya yi a halin yanzu,kawai dai kiyi hak'uri ki bani had'in kai mu ragewa juna zafi"
Ko d'aya cikin maganganunsa babu ko guda d'aya wanda ta iya ganewa saboda ta kai mak'ura gurin wahala,shi kuma duk da haka bai d'aga mata k'afa ya kyaleta ba,saima dad'a k'ok'ari tare da himma da yake gurin ganin ya cimma burinshi na biyan buk'atarsa.
Ba shi ya kyaletaba sai bayan da ya tabbatar da he is well satisfied,sannan ya sauka a kanta had'e da cilla mata damin kud'i
"Ga shinan kije kiga likita,ni fita zanyi idan kin dawo muyi waya"
Daga haka bai jira jin komai daga bakinta ba ya shige toilet en hotel en,har ya gama