Header Ads
Showing 1 words to 3000 words out of 139785 words

Chapter 1 - Albi Book Complete document by Hajjace.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

978

Ads at the middle of Article

ALBI
NA
ASMY B ALIYU*
DA
*HAJJA CE*👈


PAID BOOK..#(500)


*Account Details*
0004157137
*Jaiz Bank*
*Asma'u Buhari Aliyu*
Shaidar biya ta
08086207764


*Katin waya ta MTN.ta 07043079282 shaidar biya ta 07065283730 view WhatsApp*




*Free page 5*


Zaune yake cikin katafaren room ɗin da ya sauka na baki, ya dafe kansa da hannayensa duka biyu zuciyarsa na wani irin bugawa da ƙarfi da ƙarfi. Bai taɓa tunanin zai so Rahama Abubakar Galadanci farat ɗaya haka ba, sannan kuma ba shi da wani sha'awar auren zumunci ko kaɗan tun ta sowarsa. Abu ɗaya yasani, yasan tun tana ƙanƙanuwarta ya tsani halinta wato sangarta, kuma babban abunda yasa baya shiri da ita kenan. Ko ada can baya idan taje gidansu hutu Abuja inhar ya dawo school hutu baya doguwar magana da ita, ba kuma ya sakar mata fuska, duk akan karta rainasa, dan yasan yarinyyar nada tsaurin ido sosai bai taɓa tunanin zuciyarsa zata hango masa soyayyar Rahama Galadanci nan kusa bare har yakai ga san aurenta.
A can baya ƙanwarsa wato Deejah Galadanci na yawan yi masa hirar Rahama kasancewar kusan shekarun su ɗaya da Rahama Abubakar Galadanci, haka kuma kusan tare a suka taso da ita. Sosai suke kaunar junan su. Yaja numfashi a wahale yana tunanin yanzu ta wace hanya zai nunawa Rahama Abubakar Galadanci kulawa har ta fara sonsa? Dan tun ɗazu da ya baro ɗakin ta tunanin da kwakwalwarsa keyi kenan. Idan ya tuna kuma Rahama tace bata sonsa bata kaunarsa ba kuma zata aureshi ba, sai yaji gabansa ya faɗi. Hirar da suka yi a parlor ɗazu ta shiga dawo masa, lokaci ɗaya Ra'is ya faɗo masa arai.
Ƙarfe biyar ya shigo gidan lokacin mu'allem ɗinsu ya tafi wanda ke koyar dasu karatun addini a cikin gidan. Ummi kaɗai ya samu a parlorn ya ɗan russuna da respect ya gaisheta ta amsa cike da fara'a tana tambayarsa yana buƙatar wani abu ne? Ya ɗan shafa kai karo na farko da yaji wani irin nauyin Ummi ya saukar masa wanda bai taɓa jin hakan ba. Ya shiga tunanin kodan yanzu yana san gudan jininta ne? Tabbas dan tana mahaifiyar Rahama Galadanci ne yake jin wani irin nauyinta a ransa. ''Ummi Ra'is fa.?" Tace dashi, "Suna can tareda Hajja, kasan idan Hajja na gidan nan toh duk suna part dinta, duk da yanzu suka shigo gidan ko nan basu zo ba suna can." Bece komai ba ya fice. Part ɗin Hajja ya nufa wanda itama tana da part a cikin gidan saboda idan tazo nan take sauka. Ƙaton parlor ne sai kuma ɗakuna guda biyu da kuma ƙaramin Kitchen acikin parlorn duk da bawai girkin takeyi ba, sai dai wata rana idan bata son na masu aikin takan sarrafa abincin da takeso irin nasu na gargajiya. Suna zaune cikin parlorn Ra'is kadai ne keyiwa Hajja hira, Rahama tana ɗaya daga cikin bedroom ɗin Hajja da wayar Hajjan a hannunta tana ta ƙoƙarin gwada ƙiran Imran Matawalle amman still number baya zuwa. Farooq ya zauna yana faɗin. "Ra'is Hajja kake tayawa hira da fara'a haka?" Ra'is ya juya idanuwa yana faɗin. "Ehhh Yah Farooq." Ya kalli Hajjan yana faɗin. "Zamu fita da Ra'is zamu zaga gari me zan siwo maki Hajjaju?" Hajja tayi murmushi tana faɗin. "Kayan marmari zaka zo min dasu da kuma tsire mai zafi." Wani irin murmushi yake yiwa Hajja murmushin da ya tsayawa Hajja arai ta kuma rasa kona menene.


Mamakin Farooq take. Meya canzashi farat ɗaya haka? da sauri Ra'is ya miƙe tsaye yana faɗin. "Yaya Farook na kira Yayah Rahama mu fita tare?" Da sauri Farooq ya girgiza masa kai yana faɗin. "No need! kyaleta Kawai Ra'is." Da haka suka yiwa Hajjah sallama ta bisu da addu'ar Allah ya saukesu lafiya. Tun a mota Farooq Galadanci cikin hikima yake jan Ra'is da zancen Rahama. Shi kuma amsa kawai Ra'is ke basa yana front seat zaune yana game da wayar Farooq ɗin. A wani babban mall yai parking yace suka shiga Farooq yace ya dauki duk abunda yakeso. Washe baki Ra'is yayi ya shiga kwasar kayan daɗi tun daga kan sweet, chocolate, biscuits masu tsadar gaske da sauran abubuwan kwalama. Sai da ya gama ɗaukar nashi Faroonk yace ya ɗaukarwa Rahama itama. Ai kuwa babu musu Ra'is ya shiga zabarwa Rahama favourite ɗinta da ya sani. Sai kusan magrib suka koma gida cike da tsaraba duk ta dalilin Yaya Farook. Suna dawowa parking motar kurum yai ya fito tare da rufe motar. Alwallah yai acikin compound ɗin gidan. Shima Ra'is akan dinning area yabar ledojin yaje yai alwala shima. Tare suka nufi masallaci shida Farook Galadanci wanda yake a cikin layin.
Suna dawowa kai tsaye Ra'is Kitchen ya nufa wajen Ummi dake tsaye tana haɗa dinner itada mai aikinsu. Baiga Rahama a Kitchen ɗin ba, sai kawai ya nunawa Ummi kayan da Farooq ɗin ya siya masa shida Rahamar. Da fara'a Ummi ta karba tana ganin abubuwan tace. "Toh Allah yayi albarka, idan Abba ya shigo sai ka nuna masa shima ya gani." Ra'is ya ɗaga kai ya fice daga Kitchen ɗin, kai tsaye dakin Rahama ya nufa, samunta yayi akan sallaya tana bitar haddarta, dan yau sauran ƙiris tasha duka a wajen mu'aleem, sabida rashin iya hardar da ya karɓa. Shi yasa tana idar da magrib bata ɗaga kan sallayar ba take yin bita. Da kallo ta riƙa bin Ra'is wanda ya zauna kan soofa yana washe mata baki, a hankali ya shiga buɗa mata ledojin da ya Farooq ya siya masu chocolate. lokaci ɗaya Rahma ta haɗe rai ta ɗauke kai tana faɗin. "Tashi ka fita ni bana so." Da mamaki Ra'is ke faɗin. "Yaya Rahama meyasa?" Ta zare masa ido tana faɗin. "Ka tashi ka fita da kayan nan Ra'is kafin ranka ya ɓaci." Ta faɗa tana daka masa tsawa tamkar shi yayi mata laifin. Ra'is ya kwashi ledojin shaye da toka yake faɗin. "Kinyiwa kanki ai." Ya faɗa yana nufar ƙofa. Wani kallo ta riƙa yi masa mai cike da haushi, caraf kuma suka haɗa ido da Farook Galadanci, tayi saurin ɗauke kanta, zuciyarta na zafi tayi bala'in haɗe rai lokaci ɗaya.
Farooq ya kalli Ra'is dake shirin fita yana cewa. "Ajiye mata ta ta ledar Ra'is." Babu musu kuwa Ra'is ya dawo ya aje mata ya juya yabar ɗakin. Tsaye yayi tare da jingina bayansa jikin ƙofar, hannayensa a zube cikin aljihun wandonsa. Wani irin ni'imataccen ƙamshin turarensa ne ya cika mata hanci wanda yasa dakyar take iya catching breath ɗinta. Wannan karon zama yayi da ɗuwawunsa akan marbles ya lankwashe ƙafafunsa yana kallon cikin idanun Rahama Abubakar Galadanci, wacce zaɓar ɓacin rai yasa ta yi masa kallan cikin ido. Zuciyarsa na bugawa da wani irin azababbiyar soyayyarta, sai faman cije lips yakeyi.


Runtse ido tayi hawaye suka fara rolling akan face ɗinta, matsawa tayi can ƙarshe tana jin kusancin su yana hanata yin numfashi dai dai saboda bayyanar Farooq Galadanci a wajen, yaja numfashi tare da shafar lashes ɗin dake kwance a face nasa.
"Duk saboda nine ake wannan zubar hawayen Rahama?'' Yayi maganar da rashin amo acikin muryarsa. Ƙin buɗe ido tayi haka kuma bata basa amsa ba, sai duk yaji babu daɗi ganinta cikin wannan yanayin. Ya tausasa murya yana faɗin. "Bance dole sai kin soni ba Rahama, ni kaina nasan kinyi min ƙanƙanta a soyayya yanzu, kinga karatu kike so kiyi yanzu, haka kema baki shirya yin aure yanzu ba right?'' Da sauri ta buɗe ido tana kallonsa da wani irin yanayi dan ya taɓo mata inda yake mata kyaikyayi. Cikin rawar murya take faɗin. "Abba yana so yayi min aure, kuma ni bana son yin aure karatu nake so nayi." Farooq ya ɗan saki murmushi yana shafa sumar kansa da take cikin wani murɗaɗen style ganin plan ɗinsa zai fara aiki akanta. Ya sauke ajiyar zuciya yana faɗin. "Toh share hawayenki ni zanyi magana da Abba a bari har sai kin gama jami'a keda yin aure, amman da sharaɗi. Da sauri ta kallesa cikin rawar murya take faɗin. "Sharaɗin me Yaya Farooq?" Farooq Galadanci ya ɗan saki murmushi cikin zuciyarsa, kallonta yai yace. "Zakiyi ƙawance dani, ma'ana na zama best friend ɗinki." Rahama ta girgiza kai da sauri tana faɗin. "No Yaya Farooq, Imran Matawalle shine best friend ɗina, canza wani abun banda wannan. "Kallonta yake da dukkan idanunsa yana karantar yanayinta yace. "Kenan shi ba saurayinki bane? Ko kin manta kince shine a zuciyarki?" Rahma ta girgiza kai tana faɗin. "Ya Farooq yace dani shi ba saurayina bane shi best friend ɗinane, yace ban san ma'anar soyayyah ba, haka yake ɗaukata bayan kuma ni nasan ina sonshi." Ta faɗa tana wani haɗe rai. "Oh my God, kenan Rahama Imran Matawalle bai taɓa cewa yana sonki ba right?" Wannan karon zuciyar Farooke Galadanci bugawa takeyi saboda fargaba, addu'a kawai yakeyi Allah yasa tace bai faɗi yana sonta ba. Rahama ta turo baki tana ta ware masa manyyan idanunta tana faɗin . "Eh bai faɗa min ba, yace min sai zuwa nan gaba, wai yanzu kwakwalwata bata isa ɗaukar waɗannan abubuwan masu girma ba, kuma ni nasan soyayya tunda ina kallan yadda akeyi acikin indian series, amman suma duk ya hanani kalla wallahi, ban san meke damun Imran Matawalle ba wani lokacin." Nannauyar ajiyar zuciya Farooq ya sauke yana cewa.
"Ke kuma kika daina kallon saboda shi?" Rahama ta ɗage kafaɗa tana faɗin. "Toh Yaya Farooq yana iya? Kai bakasan rigimar Imran Matawalle bane " Girgiza kai yai ya haɗe rai yana faɗin. "Toh naji idan har bazamu zama friend's dake ba ni kuma bazan yiwa Abba maganar yai hakuri kici gaba da karatun ba, kinga sai ya aura maki duk wanda yaga dama, ni dama na haƙura dake tunda kin faɗa min da bakin ki cewa bakya so na, so duk wanda Abba yaga dama sai ya baiwa aurenki Rahama." Hankali a tashe take faɗin. "Dan Allah ka rufamin asiri Yaya Farooq, naji na amince zamu zama friend's ɗin ni da kai." Ta faɗa tana miƙa masa hannun damarta da wani irin murmushi acikin kyakkyawar fuskarta wanda ya kusan zautar da zuciyar Farooq Galadanci.
Yabi farar fatar hannunta da take miƙa masa da kallo, a hankali ya miƙa masa nata sukai holding. Farooq yaji wani sassanyan shock, besan lokacin da ya sake matse hannun nata ba. Rahama ta shiga zarewa yai saurin kallonta idanunsa na wani canza launi yace. "Promise me." Kawar da fuska tayi, so take kawai ya cika mata hannunta saboda wani zafi da taji ranta yana yi dan sun haɗa hannun. Tana ƙaƙalo murmushi tace. "I promise you Yaya Farooq bazan baka kunya ba." Kasa sakar mata hannun yai saboda wani irin feeling da yaji yana ratsa ilaihirin jikinsa. Muryarta ce ta katse mai shauƙin da ya fara lulawa ciki, yaji tana cewa. "Yaya Farooq my hand." Kunya ta kamashi ya saketa yana janyo ledar da sukai mata shopping mai dauke da sunan mall din ajikinta yana faɗin. "Kiyi amfani dasu for our new friendship." Ta shiga gyaɗa masa kai alamun zatayi ta kara da cewa. "Thank you so much Yaya Farooq." Dogon hanci yaja ya miƙe tsaye idanunsa akanta yace. "Ki fito dinner anjima." Rahama tace, "Toh." Farooq ya fice tabi bayansa da harara tana ture ledar daga gabanta. Kwanciya tai akan sallayar tana rintsa ido a fili take cewa "Naji kirjina yana zafi, nasan rashin ganinka ne Imran, shin dagaske Matawalle ya rabamu? Ina ya kaika Imran? Gashi nan za'ai min auren dole ina zansa zuciyata?" Hawaye suka shiga zirarowa daga cikin idanunta, a hankali taji ansa hannu ana share mata fuskarta, a zabure tai saurin buɗewa dan sanin waye.....




(Akwai giveaway a last free page, zamu gaya muku kona menene Allah ya bawa mai rabo sa'a)












#Asmy B Aliyu
Da
#Hajja ce 👈
[11/12, 9:31 AM] Asmy B Aliyu😘: *ALBI....*
(My Heart❤️)


NA
*ASMY B ALIYU*
DA
*HAJJA CE*👈


PAID BOOK..#(500)


*Account Details*
0004157137
*Jaiz Bank*
*Asma'u Buhari Aliyu*
Shaidar biya ta
08086207764


*Katin waya ta MTN.ta 07043079282 shaidar biya ta 07065283730 view WhatsApp*




*Free page 6*




Hajja ta gani durƙushe a gabanta tana share mata hawayen fuskarta, cikin sauri Rahama ta shige jikinta wani irin kukan bakin ciki yana sake fitowa tun daga cikin zuciyarta, tace da Hajja wacce ke shafar bayanta alamar lallashi. "Meyasa Yaya Farooq zai min haka Hajja? Nasan lokacin da ya tsaneni wallahi, har idan nai magana ya daka min tsawa ya koreni daga wajan, shine yanzu zai nuna yana sona? Why Hajja? Meyasa ya amince lokacin da aka ce za'a bashi ni?" Hajja taja numfashi ta sauke a hankali, hannun Rahama ta jayo cikin sanyin murya take ce mata. "Duk abinda yai miki a baya ya wuce ki dinga yin afuwa a rayuwarki Rahama. Sannan wannan haɗin da za'ai muku kowa yana so a cikin dangi, zumunci kuma zai sake ƙulluwa tsakanin iyayenku, zan kuma fi kowa jin daɗi da hakan." Rahama ta janye jikinta daga na Hajja, cikin kuka take faɗin. "Bana san Yaya Farooq Hajja." Cike da mamaki take tambayarta.
"Ai har yanzu baki san meye so ba Rahama, ki kwantar da hankalinki, kuna yin aure gaba kika ƙara mallakar hankalinki zakisan cewa anyi miki gata." Ran Rahama Galadanci ya sake ɓaci da kalaman Hajja, ta shiga dafe kirji jin yana mata wani irin bugu, cikin murya mai ban tausayi take faɗin.
"Kema ashe bakya san farin cikina? Hajja dake za'a yi min aure yanzu? Wayyo Allah na ina zan saka rayuwata?" Hajja ta sake janyota jikinta tana faɗin. "Kemeyasa bazaki so namu farin cikin ba Rahama? Kinganni nan? Lokacin da akai min aure shekaruna tara, na dawo daga islamiya aka ce na tube kaya ai min wanka, Allah yaji ƙan rai mahaifiyata ta shirya ni tsab aka miƙa ni ɗakin miji da bansan waye ba. Amma fa yaga shirme tunda lokacin bansan me ake nufi da auran ba. Haka mijina yai ta kula dani, bamu taɓa rabuwa ba har Allah ya ɗauki rayuwarsa, Allah yaji ƙan Galadanci."
Rahama ta ɗago ta kalli Hajja da jajayen idanunta wanda still basu dena zubar da hawaye ba. "Yanzu irin auranki za'ai min Hajja? What about Imran Matawalle da nakejin damuwa akanshi Hajja? Wannan abun da nakeji akansa duk ba love bane? Tell me Hajja ya ake gane so? A ina akejin love idan har aka farayi." Cikin takaici Hajja take kallanta tace da ita. "Wai Rahama har guda nawa kike yanzu? Dududu shekararki nawa da har kike san jefa kanki cikin fitinar soyayya? Anya ba wani abu akai miki ba Rahama?" Share hawayen tayi tace. "Allah yasa Yaya Farooq ya riƙe alƙawarinsa, Hajja cewa yai ya hakura dani zaijema ya gayawa Abban mu."
Yadda Hajja taga yanayin Farooq Galadanci a ɗazu, yanayin ya nuna mata Farooq ɗin yana cikin budurwar soyayya, ta gane cewa ya shiga fagen yakin samun Rahama Abubakar Galadanci, bata tunanin zai haƙura ya barwa wani ita dan ta fara hango tsantsar soyayyar Rahma a gurinsa tun randa sukazo gidan nan. Tasan lokacin da suna Abuja koda akai masa zancen Rahama cewa yai bazai auri ƴar yarinya ba, infact shi yana da ƴan mata masu aji kuma balagaggu ba kwaila ba.
Da kyar ma ta samu yabiyota zuwa Kano, sai gashi suna cewa zance ya canza, Farooq har ya fara rasa nutsuwar shi akan Rahama.


Hajja ta kalli Rahama "Kici gaba da addu'a Rahama kinemi zaɓin Allah akan karatun ko auran, da kuma alkairin dake tare da hadin ku da Farooq." Rahma ta turo baki. "Babu wani alkairi nida Yaya Farooq Hajja, Imran ma alkairi ne a wajena." Ture ta Hajja tai daga jikinta tana faɗin.
"Ke kinfisan mashayi kenan? Haba Rahama kowace uwa ana so ta samarwa yaranta uba nagari, kinsan da cewa Imran ɗin nan mugun mashayi ne kowa yasani a unguwar nan, shine ke kike shirin shiga rayuwarsa? Wai Rahama baki san cewa Matawalle baya kaunar mahaifinki ba ne? Da yanzu Abubakar ne a matsayin Matawalle amma yai masa fin ƙarfi, duk baki gani ba Rahama kike kokarin debo mana ɗan iskan ɗansa matsayin suruki kome? Shi yana sanki ko kuma kece kike wahalar da kanki?"
Shiru Rahama tayi tana zirarar da hawaye, itama batasan meyasa Imran yaki furta mata kalmar so ba, ta rasa dalilin da yasa idan tai masa maganar yana santa? Sai yace ba lokacin maganar bane ta bari sai nan gaba, toh yaushe yake nufi.? Ganin tayi shiru ne yasa Hajja miƙewa tace da ita. "Ki fito kici abinci tun kafin kisa ciwon damuwa ya kamaki, shi yana can be hana kanshi ci dasha ba sai ke zaki matsawa rayuwarki." Hajja bata jira Rahama tayi magana ba ta fice daga cikin ɗakin tana ta mita ita kaɗai.


Tsabar yunwar da takeji ne yasa ta miƙewa, parlorn ta sakko inda ta tarar duk sun hau kujerun dining Hajja ce kaɗai a can tsakiyar parlor an kai mata nata can dan ta tsani zuwa dining cin abinci, a cewarta banda irinta masu jiran mutuwa yau ko gobe. Kai tsaye Rahama ta nufi wajan Hajja dan taga Farooq a gurin su Ra'is ita kuma bata ma san ganinsa bare ta zauna kusa dashi. Tana zama kusa da Hajja taji Farooq ɗin na mata magana. "Rahama dawo nan." Cikin ɓacin rai da take neman haɗiyewa tace.
"Yaya Farooq zamuci da Hajja anan." Farooq ganin zata yi embracing ɗin shi yasa yace da ita. "So kin manta alƙawarin mu?" Ranta a mugun ɓace ta miƙe ta nufi wajansu, taja kujerar kusa da Ra'is tana haɗe rai. "Let me save you my new friend, me kike son ci? Tuwo ko white rice?" Rahma tai saurin ɗaukar wani plate ɗin tana faɗin.
"Zan zuba da kaina Yaya Farooq." Kafin yai magana tuni ta fara zuba abinda takeso, ganin haka yasa shima ci gaba da cin nashi yana kuma zuba mata ido, duk wani reaction nata yana kansa har ta gamaci ta tashi tabar wajan. Koda Abba ya dawo hira suka sha da Farooq, maimakon yai masa maganar da sukayi da Rahama sai yaki saboda dama can ba wai zaice da Abban ya hakura da ita bane.
Farooq Galadanci ya yi hakan ne dan Rahama ta saki jikinta dashi har su saba ta haka yake tunanin zai cusa mata soyayyarsa.


*****


Shirye ta fito cikin uniform ɗinta ta shiga room ɗin Ra'is tana cewa. "Kai kullum sai

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads