Header Ads
Showing 75001 words to 78000 words out of 139785 words

Chapter 26 - Albi Book Complete document by Hajjace.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

1007

Ads at the middle of Article

Baki da idanuwa ta buɗe tana kallon Rahama haka tabi bayanta da kallo ko da wani ta shigo, cikin sanyi murya Rahama ta gaisheta cike da respect. Malika ta amsa tana kallon Rahama. A sanyaye Rahama ta ƙarasa cikin parlorn gabanta na mugun faɗuwa, lokaci ɗaya ta haɗa ido da Hajiya Babba dake zaune cikin parlorn ita da Aunty Kausar. Saurin saukar da kanta tayi ƙasa tana jin kafafunta na kasa ɗaukar ta, haka kuma hawaye na cika idonta lokaci ɗaya. Zubewa tayi cikin rawar murya kukan da take ƙoƙarin riqewa yazo mata, baki Hajiya Babba ta buɗe tana kallonta, Aunty kausar tace. "Kuka ma ai yanzu kika fara don ubanki, ba dai ke kunnen ƙashi gareki ba? tukuna ma kukan uban me kikeyi mana haka?" Aunty Kausar ta faɗa tana wani daka mata tsawa, Rahama ta qarasa gaban Hajiya Babba tare da faɗawa jikinta ta fashe da kuka mai cin rai, kukan da duka ya karya musu zuciyoyansu. Malika ta girgiza kai cike da takaici ta nufi stairs dan zuciyarta bazata iya ɗauka ba. Ɗazu ta gama nunawa su Aunty Kausar katin ɗaurin auren Imran matawalle da Humaidahn, "Sabida zaiyi aure kike wannan kukan?" Aunty Kausar ta faɗa tana tafa hannayenta duka tana sakin wani irin wide smile acikin fuskarta. "Uhmm duk ina soyayyar da Imran Matawallen yake nuna maki? soyayyar da ya saka kika gujewa iyayenki sabida ita? Ai wallahi kuka ma yanzu kika fara Rahama, tabbas nayi farin cikin wannan Aauren da yayi, kin ga ya nunawa duniya cewa mahaifinsa yana da muhimmanci acikin rayuwarsa. Kinga ai duk soyayyar da yake yi maki bai guji mahaifinsa ba, kota wannan fannin yayi maki wayau, yanzu da kika wanko ƙafa kikazo mana uban me zamuyi maki bayan kin nuna masa mu ba komai bane?" Rahama na goge hawayen idon ta, cikin rawar murya take faɗin. "Ni dai wallahi nagama auren Imran Matawalle koda kuwa shine autan maza a duniyar nan, mun rabu dashi rabuwa ta har abada yaje can dashi da Humaidah su cinye junansu." Hajiya Babba ta shiga girgiza kai tana faɗin. "Ai kuma kinyi kaɗan yarinya, anan gidan dai bakida masauqi, sannan aurenki na har abada ne kedashi babu saki babu yaji, zakiyi hakuri ki zauna ne kamar yadda ko wace macce ke hakuri a gidan aurenta." Hajiya Babba ta kalli Aunty Kausar tana faɗin. "Ki shiga da ita ciki kuyi magana." Tare suka nufi stairs ita da Aunty Kausar da fuskarta babu walwala acikin ta. "Kinga idan kina jin shawara kukan nan da kikeyi dama kin ajeshi a gefe, aure dai an riga da an daura sai zaman hakuri, kuma yarinyar ma naji ana faɗa a gari ƴar duniya ce, so idan baki sakko daga wannan kishin naki na tsiya ba zata shigo ta kwace maki miji tunda na lura ke har yanxu sakarya ce, kaɗan daga cikin halin maza kenan waya sani ko jikin ki kawai yakeso, da kuma ya samu abunda yakeso ba shikenan ba." Ita dai Rahama batace komai ba sai faman sharar hawaye take,." Aikin banza kawai, kinyi sa'a ina cikin farin ciki dan haka zan taimaka miki zanje na karbo maki maganungunan mata masu azabar kyau da aiki a wajen Ummu Ammar, matar nan tasan abubuwa, na girmeta amma na yadda cewa ta girmi tunaninta, saboda baiwar da Allah yai mata ina matuƙar karuwa da lectures ɗinta da kuma tasirin magungunnanta. Rahama wannan karon sai mun tashi tsaye, haka dan Allah zanyi miki ba dan mugun halinki ba, saura idan abu ya shige maki karki kira ki tambaya. Kuma dole ne ki sauke wannan dolancin naki ta yadda zaki ƙara kama mijinki a hannunki. Zan baki numbern Ummu Amma saboda ki dinga karɓar wasu abubuwan nasan idan kika fara amfani dasu tabbas bazaki sake amfani da wani abu na karawa mace kima da daraja a wajan kowa ba sai wajanta. 08030644073. Wasu irin topics na zaman aure ta riqa yi mata masu zafin gaske, dan ba wanda bai san halin Humaida ƴar bariki bace, idonta a tsaye suke duk wani kalan dirty talks sai da Aunty Kausar ta zayyana mata, kamar dai yadda suka koya a wajan Ummar Ammar 8030644073 ta gwada kuma taga tasirinsu hakan yasa take sanarwa da duk matar da ta ganta cikin matsalar aure. Harda text ɗin da zaka turawa miji dan ko a office yake ta tura masa saqo na dirty maganar da zaisa dole ya dawo gida, haka wajen kwanciya karta zamar masa doki itama ta riqa sarrafa jikinsa ta kowane fanni. Jin Aunty Kausar kurum takeyi amma kam bazata baiwa Imran matawalle budurcinta ba tunda ya bari wata tayi gigin shiga cikin rayuwarsu. Kwanciyarta tayi akan bed lokacin da Aunty Kausar ta gama bata shawara. Har abinci aka kawo mata amma ko kallon abincin bata yi ba. Sai kusan 10 Imran ya kirata a waya gashi a ƙofar gida, nan fa Hajiya babba ta kara bata shawara ta haɗa mata khumra masu sanyi da daɗin ƙamshi. Haka tace ko cikin weekdays ne idan bata shiga school ba ta riqa leko su zatayi magana da Ummi akan matsalarta duk da tasan Ummi ta damu da matsalar Rahama saboda kwanakkin baya har jininta sai da ya hau akan haka. Abba ne dai har yanzu bai sauko ba. Wannan karon a back seat ta zauna ko kallonsa bata yi ba sabida bata ma son cin karo da kallon fuskarsa. Har suka isa gida babu mai magana acikin su, kai tsaye cikin closet ɗin su ta nufa ta fiddo da doguwar rigar bacci mai ɗan kauri kalar black da hula ta ɗauki duka abubuwan da zata buƙata ta nufi nata ɗakin, Kallonta kawai Imran keyi ya kasa cewa komai, ɗakinta ta nufa tana shiga ta murzawa ƙofar key. Da sauri ya biyo ta bugun duniya Imran ɗin yayi dan ta buɗe ƙofar amman ko kulasa batayi ba. Ransa yayi mugun ɓaci, zuciyarsa ta fara zafi, babu abunda yake son sha irin beer a wannan lokacin, dan haka nashi ɗakin ya shige a daren tatil ya kwana.....


*************************
Kusan ƙarfe goma ta fito daga nata ɗakin da kayan bacci ajikinta, kallo ɗaya zakayi mata kasan cewa ba tayi wanka ba, yunwa takeji sosai addu'a kawai take Allah kar ya haɗata da Imran. Kai tsaye kitchen ta nufa ruwan zafi ta ɗora ta haɗa tea ta ɗauko biscuit a store, anan cikin kitchen ɗin ta zauna tanaci. Ƙarar door bell taji, mamaki ya kamata, ta aje mug ɗin hannunta tayi window dake cikin parlorn ta buɗe duka. Motocin Imran ne a cikin parking lot. Jiki a sanyaye ta buɗe ƙofar, kallo tabi manyan matan dake tsaye a ƙofar parlorn nasu dashi. Kallon rashin sani take yi masu, lokaci ɗaya Hajiya Batula ta haɗe rai wacce itace ke biwa Mommy, sai kuma ƙawayen Mommy guda biyu, nan take zuciyarta ta bata cewa itace matar da Imran ɗin ya aura. Rahama na riqe da ƙofar tana jiran taji wajen wa suka zo. A ƙufule Hajiya Batula ke faɗin. "Ki bamu hanya mu shiga malama kinzo kinyi mana tsaye kamar icce..." Ta gefenta sukabi suka wuce jiki, asanyaye Rahama ta ƙarasa cikin parlorn, ganin sun nufi ɗakunan dake ƙasa yasa gabanta yayi wani irin bugawa, nan take zuciyarta ta bata masu jere ne. Da gudu ta nufi stairs tana jin zuciyarta tamkar zata fito waje sabida zafi da raɗaɗin da taji tana yi mata. Kusan cin karo sukayi da Imran wanda shima fitowarsa kenan daga nasa ɗakin, agigice ya riqeta yana kallon fuskarta dake jiqe da hawaye. Fisge kanta tayi tana yi masa wani irin mugun kallo, kai tsaye ɗakin nashi ta nufa acan tayi wanka ta shirya yau komai bala'insa bazata sauraresa ba school zatai tafiyarta tunda da gaske Humaidah za'a kawo mata acikin gidan nan. Hajiya Batula ta kalli Imran da mamaki wanda ya fito daga cikin kitchen ɗin da mug a hannunsa yana sipping coffee, ta qaraso wajensa tana faɗin. "Wai daman kana cikin gidan nan.?" Ya shafa kansa yana kallonta, daman tasan ba gaisheta zaiyi ba, dan haka tace. "Ya kuma naga parlorn da kujeru Imran? Toh su na amaryar ina za'a jerasu?" Ya ɗage mata kafaɗa yana yi mata wani kallo yana faɗin. "Bakya gani ne? Ko baki duba kinga akwai kujeru acikin parlorn ba?." Da wani bacin rai Hajiya Batula ke faɗin. "Sai ka kwashe ai ajera mata nata." Wani kallo ya riqa yi mata ya juya ya nufi stairs bai qara saurarenta ba. Hajiya Batula ta ɗaga waya ta kira Mommy tana faɗa mata. Mommy rai a ɓace ta kira Matawalle. "Ku barshi da gidansa Hajiya ku dawo da kujerun ajera a gadajen kawai dan Allah ku riqa lallaɓasa, ba dai an samu anyi auren ba?." Matawalle ya faɗawa Mommy hakan, kashe wayar Mommy tayi dan takaici ba tare da ta baiwa Matawallen amsa ba, haka ta kira Batula a waya tana faɗin, su jera gadajen kawai su dawo da kujerun. Da masifa Batula ke faɗin. "Toh kayan kitchen ɗin gidan ubanwa yakeso a jera su? ni wallahi kafiyar Humaidah ma tayi yawa dan banga uban me xatayi da wannan yaron ba, ai gashi nan ya raina mu baya ganin girman kowa a cikin mu." Ta kashe wayar tana banbamin faɗa. Shi kuwa yana zaune akan soofa yana sipping coffee yana kallonta gaban mirror dressing tana shafa mayyuka, fuskar nan tata tamkar hadari. Bin santala-santalan cinyoyinta ya shiga yi da kallo har zuwa kan bom-bom ɗinta da sukayi wata irin cika tamkar an hurasu. Wasu irin yawu ya haɗiya har ta saka kayanta a jikinta. Wani ɗan ƙaramin veil ɗinta wanda gaba ɗaya bai rufe mazaunanta ba shi ta sa ta ɗauki handbag wacce ta dace da kalar shigarta. Kallonta kawai yake har ta gama ta nufi kofa, a fusace taji ya fisgota yana yi mata wani irin banzan kallo zuciyarsa na mugun tafasa yake faɗin. "Ina zuwa da wannan shigar? Baki da hankali ne.?" A haukace ta fisge jikinta tana jadabaya tana faɗin. "School zanje ko sokake na zauna a gidanka bakin duniya da naka ya kasheni a cikin gidan nan? Toh kayi kaɗan wallahi." A fusace ta riqe ƙofar ya qara fisgota yana jin ransa na qara ɓaci. "Saboda baki da hankali ko? da izininwa zaki fita? Sannan da wannan shigar kike tunanin zaki fita ko wane kato yana binki da kallo yana haɗiyar yawu? inada kishi bana wasa ba ya kamata ki san da wannan, kuma makaranta sai wani satin banda yanzu, na gama magana." Ya faɗa yana zare mata manyyan idonsa masu cike da wani irin bacin rai. Hawaye na zubar mata ta cakumi wuyan rigarsa tana faɗin. "Ka sakeni Imran! ka sakeni a yau idan kai dan ha...." Hannu ya ɗaga a fusace ya xabga mata shegen marin da yasa ta fita daga cikin hankalinta na wucin gadi, jikinsa babu inda baya rawa dan ɓacin rai ya shaƙota gamida haɗata da bango yana zaro mata ido, yadda taga ya dawo ne yasa taji tamkar ta saki fitsari acikin wandonta, tamkar ba Imran Matawalle ba mai tsananin sonta da tausayinta, muryarsa a hargitse yake cewa. "Idan kika kara furta min kalmar rabuwar mu zan ɗauki mummunan mataki akanki, dan sai na koya maki mugun hankali, kisani auren mu na har abada ne babu rabuwa a tsakanin mu kinji ko bakiji ba?" Ya faɗa yana daka mata wata irin tsawa, da sauri Rahama ta shiga ɗaga kai dan bata taɓa ganinsa a haka ba, Lokaci ɗaya kuma ya jawota ya wani irin rungumeta a cikin faffaɗan kirjinsa. Tana jin yadda zuciyarsa ke tsananin bugawa da sauri da sauri. "Please don't mind Imran Matawalle." Ya faɗa yana ɗago kanta daga jikinsa ya riqe fuskarta yana ganin shatin hannunsa jikin kuncinta, a ruɗe ya riqe fuskar yana wani irin shafa fuskar yana faɗin. "Kinga Imran ɗinki bai da kirki ko Albi? Oh God meyasa kika bari ya kai hannunsa jikinki? meyasa bakyaji Albi? ina sonki ina son komai naki. Na faɗa maki idan nace ga abunda za'ayi ki amsa min da Toh kawai, dan Allah karki ƙara wani abun da zan kai hannuna jikin ki." Ya faɗa da wata irin rawar murya yana kara rungumeta tamkar zai mai da ta cikinsa duka. Ya ɗora kanta akan kafadarsa hawaye na zubar masa a jikinsa. Wani irin shegen zazzabi taji yana rufeta, lokaci ɗaya, dan marin da ya xuba mata ba qaramin shigarta yayi ba. Wani irin tsoron Imran ɗin taji ya shigeta lokaci ɗaya jin irin yadda ya kama mata wuya wurin sai zugi yake yi mata. Maganganun Umminta suka riƙa dawo mata a hankali na cewa, _Bazaki taɓa farin ciki a gidan Imran Matawalle ba._ Ya ɗago fuskarta yana kallonta. "Faɗamin min ina kike son zuwa yau?" Ya faɗa yana kallonta da brown eyes ɗinsa wanda shaye-shayensa ya gama maidasu hakan, duk da hakan Rahama na mugun son idanunsa dan wani irin kyau suke yi mata a hakan saboda har wani maiqo ke fita acikin su. "Jirani nayi wanka." Ya faɗa yana shafa fuskarta, ɗaga masa kai kurum tayi kai tsaye toilet ya nufa cikin minti goma sha biyar ya fito daga wankan, tana kallonsa ya shirya cikin farar shadda gizna sai maiko ke fita acikin ta, tayi bala'in karɓarsa. Wannan karon harda ɗora hula saman kansa ya fito sak ango mai cikar zati da kamala. Wata trolley taga ya jawo ya shiga jera masu kayan su ciki. Har ya gama Ita dai batace komai ba ya samo wani babban mayafi ya bata, babu musu ta ƙarba, toilet ta nufa ta wanko fuskarta tazo ta ƙara murza powder. Ya kalleta yana faɗin. "Jibi Humaidah zata tare sabida kayanta sun iso, and da sun gama jere zata tare, yanzu dai zamuje a Abuja na kwana huɗu zamu dawo Lahadi Monday ki koma makaranta kina farin ciki?" Ya faɗa yana kallonta cike da so, ta ɗaga masa kai kawai dan ko ba komai ba ya nuna mata tana da muhimmanci cikin rayuwarsu, amarya zata tare babu ango ko anan kawai ta ɗaga tutar mata. Ya jawota jikinsa yana ɗan shafa bayanta yana faɗin. "Ko bakya farin ciki?" Bata ce komai ba yana riqe da ita a haka suka sauko daga stairs daman ya baro bag ɗin a ɗaki sai da ya kai ta har mota ya zaunar da ita ya koma cikin gidan dan dakko trolley ɗin ya rufe ko'ina na gidan a hankali yayi knocking ƙofar ɗakin da yake jin hayaniyar su, ƙawar Mommy Hajiya Murja tazo ta buɗe ƙofar. Ya wani haɗe rai yana faɗin. "Kayan kitchen ma ku koma dasu za suyi using da wannan kar wacce ta fitar da wani abu acikin sa." Dukan su shiru sukayi suna kallonsa. "Idan kun gama ku baiwa maigadi key ɗin parlorn." Ya faɗa yana barin su tsaye a wajen, dukan su binshi sukayi da wani irin kallo lokaci ɗaya Hajiya Batula ta lailayo wani irin ashar ta figi mayafinta tana faɗin. Bazata zauna tana kallon bakin ciki ba haka kawai zuciyarta ta buga kan wani ƙaramin yaro, wannan auren sai kace jaraba, Humaidah ta riga ta ɗebowa kanta ruwan dafa kanta...




(Complete documents)
*WAMINAL HUB* #500
*ZO GARENI* #300
*NIDA RAHEEMA* #300
*RAYUWAR AURENAH* #300






#Asmy b Aliyu
#Hajja ce
#Imran Matawalle
#Rahama Galadanci
#Humaida
#Haske Writers Association..
[11/28, 11:07 PM] Asmy B Aliyu😘: *Kawayena nace Kunyi using ko Kuna using Kayan ROYAL EXQUISITE KM.*


*Tou albishirinku, ku bude kunnenku sannan Ku Matso kusa kuji. Kayan ROYAL EXQUISITE KM akwai kyau da inganci Tested and Trusted 💯.*


*Gaskia duk wadda batayi using Ba Tou An barta A Tashar dakata Kuma tasani Tabbas ta Dade tana cutar kanta Kuma tana cutar mijinta. Eh Tabbas nasan kunji Mai nake cewa,Nace kin Dade kina cutar Mijinki Hajiyata.*


*Maza ki garzayo Fadar *ROYAL EXQUISITE KM* *domun Mallakar naki kayan Kawata akan Farashi me Rahusa kar ayita abun arziqi babu ke aciki.*


*Yawwa kafin in cikaku da zance nace ba, munada Kaya kamar haka.*


*_Exclusive Tsumi_ .*
*_Virgin Again_ .*
*_Tightening pills (ciccibi Huta)_ .*
*_VIP tsumi._*
*_Milkilicious_ .*
*_Sweetener powder_ .*
*_Zinariya._*
*_GT Honey_ .*
*_Libido Booster_ .*
*_Gumbar Dadi_ .*
*_Dahuwar kaza_ .*
*_Infection set_* .
*_Amare set_ .*
*_Jego set. Da sauransu_ .*


*Akan Farashi me Rahusa, Nace Eh @very Affordable price.*


*Karki bari ayita abun arziqi babu ke ciki Hajiyata. Damun Mallakar naki kayan a tuntubi ummu Ammar a number kamar haka 08030644073.*


*Muna muku maraba da zuwa in advance. Mungode, Jazakumullah Khairan, Thank You 👏👏*


*ALBI...*
(my heart❤️)


*ASMY B ALIYU*
DA
*HAJJA CE*👈


PAID BOOK..#(500)


*Account Details*
0004157137
*Jaiz Bank*
*Asma'u Buhari Aliyu*
Shaidar biya ta
08086207764


*Katin waya ta MTN.ta 07043079282 shaidar biya ta 07065283730 view WhatsApp*


34......


"Bakiga mugun wulakanci da yayi mana bafa." Hajiya Batula ta faɗa sounding so very harsh. "Wallahi da Humaidah na jin maganata da kuma inada iko akanta da yau na raba aurenta da wannan shegen yaron wanda yake kallon kowa a ɗan iska." Mommy ta shiga girgiza kai tana faɗin. "Batula har yau baki san wacece Humaidah ba, kin zata Imran Matawalle yafi karfin ta juyasa ne? Toh shi wanene da mace bazata juyashi ba? Tab aka juya uban da ya kawoshi duniya ma ballantana shi ɗin banza. Ke dai kawai kallo ne naki, aure an riga da an ɗaura shi dan haka shigar bazai yi mata wuya ba dan na ɗauki wannan alkawarin Imran Matawalle sai ya zama bawan Humaidah Makarfi, sai ta juyashi, sai ta takasa da kafafunta, sai ya raina kansa, dan duk wata izza da girman kai sai ya sauke su na rantse." Batula Makarfi ta shiga girgiza kai tana faɗin. "Ina jin ta kan asiri zaku bi ku sami duka Imran Matawalle, an faɗa maku kullum ake kwana akan gado? Karki manta fa tun farko baya son Humaidah nasan kuma har abada bazai sota ba tunda ya riga ya furta da bakin sa, sai ta hanyar asiri right? Kuma asiri bazai daɗe akan saba, na tabbatar maki da hakan sister dan irin ƴan iskan nan da wuya asiri ya juya masu zuciya." Mommy tayi shewa tana faɗin. "shi wanene da asiri bazaiyi tasiri akan saba? Mutumin da bai tsare kansa ba ai asiri zaifi tasiri akan sa farat ɗaya ma kuwa. Ni zan faɗa maki waye Imran Matawalle yaron da zai iya yin sati bai kalli gabas yayi sallah ba."

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads