Header Ads
Showing 99001 words to 102000 words out of 163596 words

Chapter 34 - YANCNKI Book Complete by Aisha Bagudu.txt

Ads the beginning of article before Image

02 Jun 2024

1318

Ads at the middle of Article

sadashi da parlour'n dady ,Amman a wannan lokacin momy tai masa jagora zuwa bedroom din ,doctor ya fito da kayan aiki yasoma dubashi ,byn ya gama ya kalli mummy yace " "madam ya'akayi hkn ta faru jininsa ya hau dayawa sosai ?
"yakamata ku kiyayye 'bacin ransa domin ya samu cikakkiyar lafiya mai dorewa mumy tace "doctor yanayin rayuwa ne kawai Amman za a kiyaye InshaAllahu. Doctor
Ya bar magunguna da dady zai yi amfani dasu ,allurar bacci akayi masa domin ya samu ishashen bacci sannan yakama gabansa .


Ta bangaren fu'ad shima yana cikin tashin hankali mara misaltuwa, duk inda yasan zai ganta yaje har dama inda bayi tunani ba, hankalinsa yayi maseefar tashi yarasa inda zai sa ransa yaji dadi shi kam a yadda yake ji acikin ransa bazai iya hakura da neman me'ad ba ,kodan tilon diyarsa mara lafiya har hawaye ya zubar aranar ya samu guri gefen titi yayi parking din motarsa ya d'aura kansa a saman sitiyari yana kukan tausayin halin da nasreen dinsa Zata shiga a sanadin wannan tashin hankali, yasan me'ad bawani kulawa zata bata yana jin tsoron ya rasata, ya dade agurin sannan ya tada motarsa yayi hanyar gida ,koda isa gidan kasa zama yayi sai faman zariya yake acikin parlour'n sakamakon sautin bugun zuciyarsa daya addabi kunnensa "wayyohlly Allah nah ya furta yana me rike kugunsa da hannu daya .....


Daren ranar kuwa kwana me'ad tayi nafila Sam takasa runtsawa , saboda tashin hankali datake ciki yafi karfin tunaninta , tunanin mahaifinta yafi komai addabar zuciyarta, tayi shiru agurin tana lazimi tana jin kmr takirasa ta sake bashi hakuri ,daga inda take zaune ta mika hannunta ta d'auki wayarta tasoma neman layinsa ,takira wayarsa yafi sau biyar ba'a d'auka ba kawai ta rushe da kuka tana cigaba da addu'a, sai kusan ukun dare bacci 'barowa yayi awon gaba daita.


Washegari da wuri ta tashi ta shirya nasreen cikin uniform din school itama ta shirya kanta ,ta tasota gaba, tana gaba tana binta abaya har reception,ta bada makulin d'akin domin killaceshi sannan suka fice .


kai tsaye wani had'ad'en restaurant suka nufa tayi musu order abinci, ta turawa nasreen abinci agabanta tare da yin tagumi ta tsura mata ido "ki ci abinci ..... "Momy ke meyasa bazaki ci ba ?Tayi mgnr muryarta na rawa kmr zatayi kuka "kici kawai nasreen bazan iya ci ba .......
take idanun nasreen ya cicciko da kwalla "why momy.....ta fad'a hawaye na gangaro mata"tun jiya banga abinda kikaci ba ,idan bazaki ci ba nima bazanci ba takarasa mgnr hawaye na biyo kuncinta sharrrrrr ..
me'ad tayi saurin kai hannuta saman fuskar nasreen tana goge mata hawaye ", no my bby dont cry I will eat tasoma k'ok'arin dibar abinci ta kai bakinta "gashi ina ci kema ki ci kinji bbynah banason damuwarki ina matukar sonki duk da dadynki nagani kmr banasonki ,adalilin ban ajiye aikina ba Wanda hkn bashi zai nuna bana sonki ba ,nice nayi silar zuwanki duniya idan wuya ake ci naci idan dadi ne naci" ta yaya mutun zai d'auki ciki har na tsawon wata tara yayi na kuda ya haifi d'ansa ace masa bai sonshi .....
"ki daina d'aukar maganganun mahaifinki, abaya nasan nayi sakaci , rashin kulawa dake Wanda bashi yake nufin bana sonki ba ....ina sonki nasreen fiyye da kaina sannan a shirye nake Dana sadaukar da rayuwata akanki, akan mahaifinki nayi komai har sanda na mallakeshi matsayin miji gareni ,ina kuma ga ke dani kad'ai nasan azaba da wuyar Dana sha tun daga haihuwarki har zuwa yanzu.
Ta k'arasa mgnr tana bata abinci abaki suna ci tana kwantar mata da hankali har suka gama tayi dropping dinta a school takama hanyar zuwa office,Akan hanyarta ta zuwa aiki duk inda taga Almajiri sai ta tsaya tabashi sadaka maganin maseefa ..


Ahankali ta Sanyo hancin motarta cikin ma'aikanta tsirarrun mutanen da suka yi sammakon zuwa suka bita da kallo , inda take jikinta ya bata akwai abu dake tafiya a kasa, wata irin damuwa me tattare da tashin hankali ne sukayi mata diran makiya ,amman hk bai hanata sanyawa zuciyar Kwarin gwiwar ba ,ta nufi gurin data saba ajiye motarta tayi parking tana fargaban fitowa ,kusan minti talatin tana zaune works nata faman shigowa ciki har dasu mudansir da ma'aruf suka fito atare suna kyalkyake dry da alamun suna cikin nishadi suka shiga cikin ma'aikatan batare da sun lura daita ba.
tana zaune tahir shima yashigo ya wuceta.
ahankali ta fito da system dinta tasoma operating domin k'arasa tura sakonin da'akayita turo mata daga daren jiya zuwa safiyar yau din nan ,bata fito ba har sai da taga shigowar chairman sannan ta fito adaidai karshen dogon korido ta had'u da mudansir yayi saurin k'arasowa inda take ya amshi jakar hannunta da system, ita kuma tacigaba da tafiya ta nufi hanyar office dinta da niyyar shiga ta gani ko zata daina jin zafin dayake mata.
Mudansir yabiyo bayanta da Dan hanzarinsa "madam yau fa akwai meeting da chairman "nasani ta bashi amsa atakaice tana kusa kanta cikin office dayake tun shigowar mudansir ya bud'e, wanda ya zamemasa kaida .
ai da wani irin sauri me'ad ta fito daga cikin office dinta kmr zata hantsila tana furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun lahaula wala kuwata illa billa....
Shi kuwa mudansir kad'an yarage bai kyalkyale mata da dryr mugunta ba saboda yadda yaga tafito aguje kmr mota ....


numfashi take fitarwa ahankali tana jin zafi ajikinta, tayi saurin barin jikin kofar Dan tiririn dake ta'ba fatar jikinta, ta nufi conference room, koda ta isa ta iske chairman zaune tare da mataimakinsa Wanda yakasance ba indiye ne ,shine na biyu a company sai ita, duk sauran wad'an da ke zaune agurin akarkashin ikonta suke, ahankali ta samu guri ta zauna a natse zuciyarta na bugawa ,wannan shine karo na farko da za'a yi taro ta tsinci kanta cikin matsanancin fad'uwar gaba ,duk taron da za'a yi cike take da natsuwar zuciya da kwarin gwiwar tare da isa da mallaka da nuna ita din wata ce acikin ma'aikatar ,sai gashi yau babu wannan zarra da isa da mallaka sai tsagwaron tsoro dankare da zuciyarta.


Shiru ne yabiyo bayan zamanta , kafin daga bisani chairman yayi gyaran murya yasoma magana cikin kwararren turancinsa wanda bazaka ta'ba cewar ya had'a jinsi da hausa fulani ba"acikin yan kwanakin nan abubuwa dayawa sun faru Wanda yasa dole mu tautauna akai, Abu na farko da campay tasoma fuskanta shine karancin income din da company bai samu ,ta hanyar sakacin manager. Me'ad ta d'ago idanunta da sauri ta d'aura akansa tana kallonsa , chairman ya fuskanceta da kyau kana yacigaba da mgn "sakacin rashin tsayuwarki akan aikinki da rashin bawa aikin mahimmanci yana kokarin janyo mana babbar hasara, a halin yanzu dakatarwa ce tafi dacewa dake ,Amman saboda wannan shine karo na farko da muka ta'ba samunki da wasa da aiki, yasa zamu yi sausaci akai ,Dan hk daga wannan lokacin bama bukatar sakaci ko rashin bawa aikinki mahimmanci, Dan idan muka sake samun rashin ingancin tsayuwarki aiki zamu sallameki......
tunda chairman ya fara magana ta nemi miyo ko daya tarasa abakinta, zuciyarta ke wani irin bugawa da sauri sauri ,duk karfin ac dake aiki acikin conference room din ,hkn bai hana gumi tsatsafo Mata ba..
take furucin mahaifinta yashiga dawowa mata "aikin da kike takama dashi Wanda ni kad'ai nasan irin wahalar Dana sha akansa kafin ki sameshi shima zai bar hannunki ......
"inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kawai take furtawa a zaunen dake agurin gumi na sake tsatsafo mata , iya abinda ta iya fahimta kenan daga bakin chairman duk sauran maganganun da yacigaba dayi babu abinda ta fahimta hatta Wanda sauran ma'aikatan suka taunana bata fahimci komai ba ,sakamakon zuciyarta data tsaya ta daina aiki na wani lokaci ...


Lokacin da zuciyarta tacigaba da aiki ta dawo cikin hanlinta ta nemi kowa tarasa acikin conference room din sai ita kad'ai zaune ,ashe tuni taron ya watse .
runtse idanunta tayi sosai, wasu zafafan hawaye suka shiga kokuwar zubo mata "me ke shirin faruwa da rayuwata ?


"gidana babu dadi ,bani da jituwa da mahaifina , aikina na neman subuci min ,tabbas wata maseefa na kusanto rayuwata "ya Allah ka kawo min sauki cikin lamarina ,ya Allah karka barni haka, na tuba Allah kasanyaya zuciyar mahaifina akaina ya yafe min abinda nayi masa ,domin nasan bakinsa ne ke bibiyar rayuwata,
ta Dade zaune agurin tana kuka ,ganin kuka da tunani bazai bar kanta ba yasa da kyar tasamu ta mike tsaye tare da gyara zaman mayafinta zuciyarta bata shawarar ta nemi mutane suje su bawa mahaifinta hakuri ya yafe mata, mahaifin sajida shine mutun na farko da zuciyarta ta hasasho mata Amman ina bazata taka kafafunta zuwa gidansa ba, 'yarsa tayi mata katangar karfe Dan wannan gidan har abada bazata sake sanya kafafunta cikinsa ba ,ta kofar baya ta biyo Dan batason jama'a su ganta ,Dan zasu fahimci halin da take ciki ..


kmr jira ake duk inda ka yi acikin ma'aikatar maganar me'ad ake da irin matakin da chairman yace zai d'auka akanta, su mudansir kuwa ansamu abinda ake so ,sai murna suke har da rawa kmr wad'anda akayiwa albishiri da gidan aljannah " kai mutumina wallahi ina cikin farinciki mara misaltuwa ka koma gurin malamin nan naka ya sake k'ara wutar aiki, ayi ayi akoreta wallahi ban so uzirin da chairman yayi mata ba ,naso yayi mata me gabadaya ne injin cewar ma'aruf..
wata uwar dariya mudansir ya kwashe dashi "sha kuruminka abokina komai daki daki yafi ka zuba ido kasha kallo muna nan za'a yi mata me gabadaya..
Tahir ya saukar da ajiyar zuciya daman kuma tun da suka soma mgn bai tsoma bakinsa ba sai yanzu yace "gsky na fara jin tausayinta me zai hana abarta hk idan ka lura tayi sanyi ba kmr lukutan baya ba .
"Kunji shirme banza ,kai ta tafi can kabawa mutane guri ,da alamun ka soma sauya ra'ayinka na bukatar matsayinta daka furta tun farko?
"Ko ban sauya ra'ayina ba nima da wasa na fad'a mgnr , ina ni ina matsayinta, ku kanku kunsa wasa nake yi bazan ta'ba samun matsayinta ba sai wani ikon Allah.
Maaruf yace "mudansir rabu da da wannan shirmammen banza da alamun cutar hauka tasoma kama.....
ai bai kai ga karasa mgnr ba tahir ya cakumi wuyan rigarsa da iyakacin karfinsa "ni ne cutar hauka ta kama,?
"ni zaka cewa hk saboda kai Mara imani ne da tausayi " ina zamu da hakinta ?
"Meye ribarmu idan munyi sanadin rabata da aikinta da har zaka dangantani da kalmar hauka?
Mudansir yayi saurin shiga tsakaninsu "haba tahir meye hk ne ?
wasa yake maka fa bai kamata ka d'auki zafi ba ma'aruf ya fizgo mgn da kyar yace "rabu dashi ance masa me cutar hauka yayi duk uwar da zai yi ,mahaukaci dolo sauna dakiki..tahir ya kai masa mari sai ga jini ya balle abakinsa abu kmr wasa suka dinga zagin kansu da son yin dambe, da kyar mudansir yasamu ya rabusu tahir yana huci yace "ni... ni ...na cire hanuna acikin shirinku daman kuma ba dani akaje gidan malam ba ,daga yau babu hannuna cikin shirinku duk abinda zaije yazo karku sani ciki azzalume Kawai ya fita yana banko musu kofar da karfi .
suka tsaya sororo suka bi kofar da kallo kirjinsu na mahaukacin bugu"kaji abinda wannan D'an iskan ya fad'a ko ? Ma'aruf ya fad'a yana naushin iska "rabu dashi shima zan gama dashi wata killa kafin ita tabar aikin shi zai rigata barin aikin.


Kai tsaye tahir harabar ma'aikanta ya nufa inda ya iske me'ad tsayen tana zariya abar tausayi, kunnenta manne da waya "wallahi ta bani tausayi ya fad'a acikin zuciyarsa yana jin kmr yaje ya sameta ya sanar daita abinda aka yi mata,Amman yana jin tsoro saboda yasan halinta, yasan yadda take da saurin d'aukar zafi, karshen abun ya juye ya dawo kanshi ,shi kad'ai .
kad'a kansa yayi kawai ya kama gabansa ya koma bakin aikinsa .


************


Zaune Alhaji ediris takai yake agaban amininsa kuma abokin shawararsa mahaifin sajida suna fuskantar juna kafin daga baya yasoma mgn a natse cikin sanyayyiyar murya "me yasa zaka hanata auren abinda take so, ?
"A ganina daga me'ad har sajida abu daya ne agurimu ta wani fannin ma har gara sajida tunda duk rashin son da batawa emran ta hakura ta auresa daga baya Allah ya kawo rabuwa atsakaninsu, Dan haka banga dalilinka na hana auren fu...ya datse harshensa yakasa karasawa saboda baya tunanin zai iya karasa sunan wannnan D'an matsiyatan, shi kansa bazai so sajida ta auresa ba saboda irin tsanar da yayi masa Amman domin kuntatawa me'ad zaiyi tsayin daka ruwa da tsaki akan yaga yaron ya aureta shi da yasan inda zai ga najma har ita sai yabata makudan kudi ta auresa , kawai dan yaga me'ad cikin bakiciki kmr yadda tayi silar jefa safwan da shi kansa da har yanzu wannan bakinciki yaki barinsa.


"abinda bazai ta'ba yiwuwa bane wannan AI cin amanar kauna da yarda ne Sam sajida baza ta'ba auran mijin me'ad ba har abada ...iniji Cewar mahaifin sajida .
Dady yace "ta ina aurensu yazama cin amana ?
"Gsky ni banga wani cin amana ba acikinsa ba.


Mahaifin sajida yace "Ko babu cin amana ai ana barin halak Dan kunya, "banda wannan halak din mahaifin me'ad ya fad'a yana furzar da iska .
muhawura ce tashiga tsakaninsu kowa na kawo hujjarsa Akan auren daga karshe dcp aliyu ya Mike ransa a matukar 'bace ya bar parlour'n saboda idan yacigaba da zama agurin zasu raba gari ,da shi da amininsa da Allah kad'ai yasan tsakaninsu .


Mahaifin me'ad bai bar gidan ba har sai daya gana da sajida inda yake ce mata "ta gayawa wakilan fu'ad su zo su sameshi idan sun tashi ,ita kanta sai alokacin tasan tayi kuskuren son mijin aminiyarta , Amman yazatayi da tata zuciyar datayi kudin balan kamuwa da matsanancin soyayyarsa?


Bayan kwana biyu sajida tasamu me gidan fu'ad da maganar zance aurenta da fu'ad, Amman ta boye masa gurin Wanda zashi neman aurenta,"yace karta damu InshaAllahu zaije ....fu'ad Wanda ya kasa samun natsuwar zuciya gabadaya ya tattara zance wani auren najma da sajida dayake son yi gefe saboda bulayin neman me'ad da sanyin idaniyansa ya taho guest house din me gidansa inda yafi tunanin zai samesa ya nemi izinin agurin aikinsa domin samun gano inda iyalinsa Suke,yashigo cikin parlour'n dayake zaune yasamu guri ya zauna yana sauke naunayen ajiyar zuciya tare da dafe goshinsa sannan ya gaishe dashi .
Ya amsa yana ajiye magazine din dake rike a hannunsa,yana dubansa "yanzu nake shirin nemanka nan ya karo masa abinda sajida ta bugo ta gaya masa. wata mummunar tashin hankali ya tsinci kansa ciki take gefen kansa ya Sara ya d'ago agigice yana dubansa batare dayace masa komai ba me gidansa yacigaba da mgn yanzu sai ka sanar min da inda gidansu ita dayar yarinyar take sai ayi abun gabadaya a huta ,sosai fu'ad ke kallonsa da idanunsa da suka gama canza kalla har lokacin sunan mutumin dayaji yafito daga cikin bakinsa yake masa yawo acikin kwakwaluwarsa "to me hakan yake nufi da mahaifin me'ad yabada goyon bayan wannan aure?
Zuciyarsa tabashi amsa da ya yana nufin abubuwa dayawa .
a matukar zuciye ya runtse idanunsa yana tsuma bai tsaya gayawa me gidansa matsayin mutumin dazaije gurinsa neman aure ba ....


Mmn sudais ceπŸ’—πŸ’—πŸ’—πŸ’—πŸ’—πŸ’—
'YAN CINKI
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
πŸ’—πŸ’—πŸ’—πŸ’—πŸ’—πŸ’—


~NA~


*AYSHA A BAGUDO*


~DEDICATED TO~
JIDDATULKHAIRI
MARUBUCIYAR
MATAR DATTIJO


Page 79


......Jikinsa ne yacigaba tsuma , kansa gaba Ι—aya ya kulle, yayi mamakin jin abinda mai gidansa ya fad'a mishi, hankakinsa gaba daya yagama tashi ,xuciyar sa ta shiga rud'ani, "wai me surukin nashi yake nufi da shi, ?
"wane irin zato surukin nasa yake masa, ?
"me yasa ya gwammace kar'bar auren sajeeda alhalin lokacin da zai aure me'ad kin amincewa yayi ? Tambayoyin da ya rika yiwa xuciyarsa kenan .
"Yasan zai yi hkn ne Dan kawai ya bak'antawa me'ad rai .. ..


A fusace ya mike zai bar parlour'n, cikin natsuwa mai gidansa ya kira shi "fu'ad ina zaka je haka,? Tsayawa yayi yana haki batare dayace masa komai ba .
" me yasa naga yanayinka gaba daya ya canja? Dawo ka zauna"


A hankali cikin nutsuwa fu'ad ya dawo ya zauna yana fuskantar mai gidansa. "Gaya min menene damuwar ka fu'ad, naga daga yin wannan Maganar gaba daya ka canja daga farin ciki zuwa akasinsa, hankalinka ya tashi damuwa ta bayyana a idanunka, fad'a min idan akwai wata matsala ne musan yadda zamu shawo kanta "


Sunkuyar da kai fu'ad yayi sannan ya fara yin magana cike da ladabi da girmama ga mai gidan sa
"Yalla'bai shi fa wannan mutumin da zai kar'bi auren sajeeda ba kowa bane face mahaifin me'ad"


Wani irin shock mai gidan nasa yayi lokacin da yaji wannan maganar, "mahaifin me'ad fa ?" Ya maimaita yana kallon fu'ad cike da neman K'arin bayani


"Kwarai kuwa yalla'bai mahaifin me'ad ne ,"Abinda yake Ζ™ara d'aure min kai shi ne ta yadda zai yi ya amshi auren sajeeda alhalin a da can baya lokacin da xan auri me'ad 'ke'kashe Ζ™asa yayi yace baxan aureta ba, to yanzu kuma wane dalili ne zai sa ya amince na auri sajeeda tabbas nasan akwai wata manufa a cikin zuciyar shi".


Shiru mai gidansa yayi yana nazarin Wad'annan maganganun da fu'ad ya fad'a masa, bayan sun kammala maganar da zasu yi ne suka yi sallama fu'ad ya tashi ya bar

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads