Showing 102001 words to 105000 words out of 163596 words
Chapter 35 - YANCNKI Book Complete by Aisha Bagudu.txt
me gidansa zaune yana mamakin abinda ke shirin faruwa.
Yana fitowa harabar gidan Motar shi ya bud'e ya shiga sai yaji kamar baxai iya yin driving din ba saboda wannan Maganar da aka yi masa ,tambayar kansa ya shiga yi me Mahaifin me'ad yake nufi da wannan batun da da'akazo masa da shi da rana tsaka, ?
tunani ya rika yi gami da nazari, ba ƙaramin caji ƙwaƙwalwarsa ta rika yi ba a haka har ya isa gida wanka yayi ya sake fita neman me'ad sai bai samu ganinta bai yi tunanin zuwa gurin aikinta ba ,saboda yasan halinta ,kad'an daga cikin halinta su siyar da hali agurin shi kuma abinda bazai so faruwarsa kenan ba .
A ɓangaren me'ad kuma, har yanzu tana fama da matsalar da ita kanta bata san asalinta ba, ba kuma ta san dalilin da yasa ta tsinci kanta a wannan halin ba,sannan har wannan lokacin bata daina tunanin hakunci da chairman din office din su ya fara tunanin yanke mata ba ,ta hanyar dakatar da ita amma sbd kwarewar ta ga iya aikin da jajircewa wajen tsayawa tayi aikin yadda ya kamata yasa ya d'aga mata kafa gabadaya ta fige ta rame tafita haiyacinta ban da kuka babu abinda take ..
Hankalinta kullun sake tashi yake ganin yadda kullum matsalarta gaba take yi bata baya ,hkn yasa ta sake dagewa da addu'a da sadaka da kiyamullaili a kan Allah ya kawo mata karshen wannan matsalar da take ciki, duk da wannan jajircewar da take wajen addu'a da sadaka still dai har yanzu bata iya xama a office dinta domin gudanar da aikinta kamar yadda yakamata ,yayinda tsakanin su mudansir da tahir amintarsu ta dawo sama sama ko nace ta kusan Yankewa, saboda kusan kowa yanzu harkar gabansa yake sai dai a kasan zuciyar mudansir yana jin cewar bazai iya barin tahir hk ba sai ya bisa da bita da kulle.
sajida zaune a d'akinta tana tunanin yadda aurensu zai kasance da fu'ad , ita tana jin idan duk duniya zasu had'u akanta matsawar fu'ad ya amince da aureta zata aureshi ko da kuwa mutuwa me'ad zatayi ,ita Sam bataji kunyar ko tsoro acikin dady'n me'ad zai kar'bi aurenta ,a ganinta ma meye aciki Dan ta auri fu'ad?
"Tana son shi bugu da kari kuma ita me'ad tayi wasa da damarta ta hanyar rashin kulawa da gidanta, yanxu hk tana da labarin duk abinda ya faru daga korar da mahaifinta yayi mata har zuwa neman da fu'ad ya haukace agari yana yi akanta, gashi ita tasan hotel din da me'ad take gaya masa ne kawai ba zatayi ba ,tana nan tana jiran yagaji da nemanta ya hakura ya dawo haiyacinsa suyi aurensu a wuce gurin Dan ta najma me sauki ne ita me tasan yadda zatayi daita a karshe matukar ya aureta bazai ta'ba tunanin wani aurenta ba hatta me'ad din karon kanta zatasa ya manta daita arayuwarsa ,tana cikin wannan tunanin kiran khalid yashigo wayarta,taja dogon tsaki tare da furta another problem sannan ta d'auki wayar "meye ne zaka dameni bafa nason takura
"Ki fito ina jiranki a harabar gidanku ya fad'a atakaice tare da katse kiran .
khalid matashin saurayi ne D'an kimanin shekaru a shirin da shida zuwa da bakwai ,abokin aikinta ne dake bibiyarta da sunan friendship har ta kai daya fito fili ya bayyana mata sirrin dake ransa , Amman fur taki amince masa asalima sai yanke halaka tayi dashi saboda bataga wani abin so ajikinsa ba ,kuma tun daga ranar bata sake barin sun had'u da junansu ba balle ya karanto shirme ,shi kuma babu abinda yake kwadayi da son gani kmrta .duk da bata sanar masa ba yasan komai akan yadda take mugu mugun son fu'ad .
Ta fito sanye cikin wando da rigar body hook Wanda ya matse jikinta sosai ,A tsaye ta sameshi jikin motarsa dake kusa da nata motar ,ya hard'e hannuwansa duka akirji, tun sanda ta fito ya tsurawa surar jikinta idanunsa,yana kallonta daga sama har kasa yake kare mata kallo tsab irin macen da yake burin so da mallaka kenan arayuwarsa ,ji yake duk duniya babu mace me kyawunta sannan yana ji tmkr ya isa gareta ya rungumeta akirjinsa , yanayin yadda yake kallonta kwata kwata baiyi mata ba ,Dan har ya sata jin wani iri ajikinta saboda gabadaya ya tsurawa nonuwanta idanunta kmr zai cinyesu , kallo daya tayi masa ta d'auke idanunta akansa ta haye saman motarta ta zauna tana kallon wayar hannuta batare da tace masa komai ba
Khalid kyakkyawa ne shima sai dai bai kai fu'ad a komai ba , gyara tsayuwarsa yayi tare da matsowa gabanta still rungume yake hannunwansa a kirjinsa ahankali yasoma mgn cikin sanyayyiyar muryarsa "plz sajida kinsa na dad'e ina binki ta hanyoyi daban daban , ina sonki kuma tsakanina da Allah ,ki manta kowa ki bani damar na shigo cikin rayuwarki dan Allah....
Ta busar da iskar bakinta idanunta har lokacin yana kan wayarta, kanta tashiga girgizawa sannan d'ago ahankali tana dubansa a yatsine kana tace " Khalid Kake ko wa ?
"Wai me kake tunani Akaina ne?
"meyasa ba zaka fahimceni ba sannan ka fahimci ina na dosa ,?" Try to understand me Khalid ....."bana son ka bana kaunar wata halaka da kai kuma halakar da mukayi abaya ta mutunci Allah yasanya mata albarka Amman dan Allah ka fita cikin rayuwata , saboda kai ba irin namijin danake so bane ,you not can of man I like"
" am not can of man ?ya tambayeta yana tsareta da manya idanunsa "yes of course ta bashi amsa tare da shayi ko wata fargaba ba sannan ta maida idanunta kan wayarta tacigaba da abinda take.
muryarsa cike da rauni da in ina yace "meye bambamci tsakanina da kalar namijin da kike so?
"khalid.....bana tunanin yau ne zan fara gaya maka wannan mgnr ,I have my type, ina da type din namijin da nake so , wanda zuciyata take so da muradi ba kai ba ,kuma zan tabbatar da na bawa xuciyata abinda take so tak'arasa mgnr tana hura masa iskar bakinta me zafi sannan ta tsaresa da idanunta "just forget about any love you have for me coz I can't love you kaje gaba da rayuwarka watakila zakayi cath up wata tasoka but not me ....
"but ai ni ke zuciyata ta za'ba kuma take muradin rayuwa daita ina sonki saji...."enough khalid don't ever say that rubbish again..bazan ta'ba sonka ba koda kuwa zaka mutu ka dawo sajida nada ra'ayin mijin datake so okay ,"ina son namiji kamili natsatse wanda yasan darajar da ciwon kansa, dogo baki me faffad'an kirji me sex eyes me haiba da Kammala, ma'aboci kyau wanda a duk sanda na kallesa zanji Feelings dinsa na ratsani ...
" idan na kallesa zan ji dadi acikin zuciyata sannan zai sani na jini a new level ba kai ba me zaka min ?
"me zanji a tattare da..... ...?
"common short up there my friend karki tozartani akan wannan sifoffin da kika lisafa ... ni meye na rasa ajikina ?
" meye banda shi acikin abubuwan da kika lisafa?
ta kai hannunta ta gyara gashin kanta daya zubo gefen fuskarta sannan tace "karka fad'i abinda kasan ba haka bane, da kace duk abubuwan dana lisafa kana dashi khalid ta ina ?
"Ina suke ?
"ina abinda na lisafa?
"Sam ni banga komai ba danake so na namiji ajikinka , da kana da abinda na lisafa da yanzu mun wuce gurin ,abu na karshe da zan gaya Maka ka bar rayuwata ..
Muryasa a matukar sanyaye yace plz sajida wallahi ina .."
"Ka daina ronkona plz Dan ba zaka ta'ba samun abinda kake so ba kalleka fa D'an Allah wani gaja gaja da kai .
kai yanzu bakiji kunyar cewa Kana sona ba a girme na girmeka nesa ba kusa ba Khalid me zan ji aurenka ...? zai yi mgn ta katseshi ta hanyar cewa "stop beging me khalid kaje kaso wata plz..
ya sauke naunauyen ajiyar zuciya tare da zura hannunwansa duka cikin aljihun wandonsa yana fitar da wani hucin Numfashi me gyaraye da tsagwaron 'bacin rai"ammm.. amm naji baki sona sai mijin aminiyarki kike so, saboda shi ne wanda ke da dukkanin tsifofin da kika lisafa ,tell me i want know?
Ta d'ago fuskarta a d'aure tana dubansa shima kallon cikin idanunta yake cike da isgilanci rainasa din datayi "khalid am not long interested on you just live my life plz ...
ya juyar da fuskarsa kad'an yayinda dryrta ta subuce masa yayi murmushin mugunta sannan ya juyo ya fuskanceta "dole ki waskewa mgnta saboda kinsa nasan komai , auren cin amana kike kokarin yi amman bari nagaya miki wani good news, ki hakura ki aureni saboda nasan duk abinda kike bukata daga cikakken nmj wallahi zan miki ,Zan iya cika wannan bombom din naki tsab da zan mararki Dan hk ki daina rainani yaro ne ni a zahirance Amman baki San badini na ba ..kuma ki rubuta ki ajiye a inda bazai goge ba ni ne zan aureki as ending .......
A matukar tsawace tace "plz just go tana nurfafashi tmkr me cutar asma " i don't want see you near me ta fad'i hk cikin murya mai rawa ala'mun tana son yi masa rashin mutunci "
"sajida ...yakira sunanta muryarsa a kasalance "khalid can you live plz ? "dole ne nace bana yi bana sonka bana kaunarka bazan iya soyayya da kai ba ka bar rayuwata mana "naji amman yakamata ki duba girman son danake miki ki bari muyi ...."no no we are not talk to anything just go ...get out ..live ..bye... ta fad'a a matukar harzuke tana me dafe gefen kanta data ji yasoma Sara mata "plz i beg you sajida tayi saurin d'aga masa hannu out bey tana nuna masa kofar get da hannunta.
jimmmmmm yayi yana kallonta sannan ya meida hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa yasoma d'aga kafafunsa kmr kazar da kwai ya fashewa aciki tsaki taja ta gyara zamanta tayi consentret akan wayarta datake aikin turawa fu'ad text message tana jin lokacin da me gadi ya bud'e masa get ta juya a matukar fusace "you stupid man if you ever open get to that stupid boy you wil see what wil happen to you," a'a kunji min jaraba da maseefa irinta primature... karami yaro dashi sai jarabar naci ko ya zaiyi dani oho?
"nace banayi banayi !! ana so do.... shiru tayi ta kasa karasa mgnrta taja tsaki kawai ....
cikin sauri fu'ad ya fito daga cikin d'akinsa yana waya sanye da farar singlet da wando sai dai ya d'aura rigar t shirt a saman singlet din bai sanya botira ba "okay ina jinka tana wajen har yanzu ?
Can bangaren kabeer yace "tana wajen Amman kayi sauri da alamun ta kusan gama abinda tazo yi .."dan Allah ka tsayar min daita . Kabir yace "kaima kasan halin wannan rikitacciyar matar taka ba tsayawa zatayi ba ,yanzu ma data ganin bazata tsaya ba .", okay ganin nan zuwa suna tare da nasreen ne ?
"A'a injin cewar kabir cikin sauri fu'ad ya isa ya bud'e motarsa yashiga ya kunna tare da danna hon.....da karfi me gadi ya bud'e masa ya fita aguje.
sai dai yana zuwa yashiga bud'e idanun yaga ta inda zai ganta ,kai tsaye inda kabir ya gaya masa ya nufa da sauri Amman bai ganta ba Dan hk yak'araso gurin kabeer yana riko hannunsa "ina take kabeer ...?
Cire hannunsa kabir yayi cikin nasa yace "wallahil yanzu nan ta wuce naso na bita sai dai banzo da mota ba ,goshinsa ya dafe yashiga zagaye gurin tare da ya furta Allah yana me runtse idanunsa "why me'ad me yasa kike son ruguza mana rayuwarmu alhalin kinsa muna bukatar juna ..?
Da sauri ya sake dawowa inda kabir yake tsaye yana dubansa cike da matsanancin tausayawa "wani hanya tabi kabir ...?
Kabir ya nuna masa hanyar da tabi ..yabi hanyar da kallo yana tunanin yabita ne ko ya fita harkarta ya hutawa rayuwarsa, shi daman ba saboda ita bane yake wannan wahalar...
Jiki a sanyaye ya k'arasa jikin motarsa yana kokarin bud'ewa kiran sajida yashigo wayarsa ya ciro wayar daga aljihun gaban rigarsa yana duba screen din wayar,number da ya gani ne yasashi Jan tsaki , kmr bazai d'auka ba sai kuma ya d'auka "uhmmm meye kuma?
"I lost a lot of things arayuwata amman banaso kaima na rasaka fu'ad hope sir malik ya isa maka da sakona?
"Wani banzar sako kenan "sajeeda ya kirata ransa a matukar 'bace"karki k'ara min matsala da damuwa akan wanda nake ciki ,wai ma Sajid me kike nufi dani ne ?
"Babu komai sai alkairi kuma InshaAllahu zai tabbata ,tun da har ka furta tare da amincewa aurena wannan kawai ya isheni nacigaba da rayuwa har zuwa sanda zamu mallaki juna sannan kuma karshen matsalata tazo ,ka daina zurfafa tunaninka ,ka daina damuwa I promise zan baka dukkanin kulawar dakake bukata ,zan baka kulawar daka rasa saboda irin son Da nake ma ...
"common that was not on fear, sajida bakya sona ki duba kiga yadda nake cikin tashin hankali akan matsalar gidana nasan kinsa komai amman ke k'ok'ari kike kawai a d'aura mana
aure.
"Tabbas aurenmu shine agabana kuma shine abinda nake buri a halin yanzu sannan zanyi Iya kokarina naga na mallakeka , yanzu dai kana ina ,Dan ina son mu had'u da kai akwai maganar da zamuyi very important"
"bani da lokacinki a halin yanzu neman inda matata da yarinyata nake "ta kwashe da wata uwar dry sannan tace "ka sani ko nasan inda matarka take da yarinyarka just try and come...jikinsa yayi sanyi yasoma ya rage murya "Dan Allah ko kinsa inda take ne ki gaya min ...?
"Uhmm a'a ban sani ba ,Amman ka dai kazo akwai Wanda yasani "rubbish ya furta a harzuke ganin raina masa wayo take son yi akwai siyar data sake shirya masa ,shi kuma ya ranse ba zai sake barin su had' u ba either ko tazama matarsa ko km sun rabu ..."ba zaka zo ba kenan ?"yes of course banzo wawiya kawai maciya amana ke auren ma na fasa inga uban da zai sani aurenki ...ta saki wata razannaniyar k' ara tare da durowa daga saman gadonta tana furta "what?
"Abinda kunnenki yaji shi na fad'a na fasa aurenki kibar rayuwata simple as that "
Muryarta na rawa tace" Dan girman Allah Allah fu'ad kar ka fasa au..sai kuma kiyi ya katse kiransa tare da shigewa motarsa ya bar gurin aguje..
**********
Yau takama Monday Wanda ko bature na tsoron ranar da girmamata rana ce da duk wani ma'aikaci ke jin tsorota da taka tsantsar daita ,me'ad tana zaune acikin motarta kmr koda yaushe tana tunanin yadda xata bullowa wannan matsalar da ta addabe ta , taji an kwankwasa glas din motarta da sauri ta d'ago kanta, tare da bud'e murfin mota ,daya daga cikin staff din company ne ya bayyana agabanta bayan sun gaisa yake fad'a mata cewa chairman yana son ganinta a office din sa.
A sanyaye ta fito daga cikin motar tare yiwa motar key , da sallama ta shiga office din tare da neman kujerar da ke ajiye a gefe ta xauna gabanta na wani irin fad'uwa , bayan sun kammala gaisawa da chairman ya shiga jefa mata wasu tambayoyi.
"Har yanzu na kasa ganin wani canji daga gare ki me'ad ,dan Allah ki fad'a min abinda yake damunki bana so ki boye min komai, Ni dai nasan da ba haka kike ba sam ban sanki da sakaci ko wasa da aiki ba, me yasa Yanzu abubuwa suke neman tabar'barewa Company? Ina jiran amsa daga gare ki kuma bana so ki boye min gaskiyar abinda ke faruwa da ke.
Kuka mai tsanani me'ad ta shiga yi, sai da tayi kukan da ya ishe ta sannan ta zayyana mishi dukkan halin da take ciki.
Ya tausaya mata sosai kuma yayi alƙawarin insha Allah matsalar da take ciki da mahaifinta yazo ƙarshe godiya tayi masa, yacigaba da mgn yana duba file din su ma'aruf "kinsa cewa wannan rashin zamamki cikin office dinki , sammu akayi miki ?
mead ta d'ago kanta a matukar firgice tana dubansa cike da mamaki da matsanancin tsoro, "kina mamaki ko ,?tayi saurin d'aga masa kai alamun Eh "karkiyi mamaki mead akan samu irin haka .
bakinta na rawa tace " ni kuwa wa nayi laifi da har zai min samu akan aikina ?
Chairman yace "kina son sani ko su waye ?
Jikinta na rawa tashiga girgiza masa alamun eh"
"okay ina zuwa "ya d'auki wayarsa ya kira messenger cikin minti biyu yashigo jeka ka cewa acp ya shigo min da yaran nan kafi ya wuce dasu "okay sir ya fita da sauri ..
Ahankali taji an bud'e kofar gabadaya ta kasa juya saboda jikinta daya d'auki rawa har sai da charman yace "ki juya mana kiga yan iskan da suka miki aika aika da kokarin rabaki da hanyar abincinki "
jikinta na cigaba da kyarma ta soma juyawa ahankali har ta juyo gbdy idanunta ya sauka akan tahir da mudansir da ma'aruf dukanindu hannunwansu da handcuff, take gabanta yayi wani irin dukan uku uku yashiga fad'uwa tashiga nunasu da hannunta bakinta na rawa "ku..ku ne kuka min sai kuma ta rushe da kuka "laifin me na muku da kuka shirya min wannan munakisar?
"A halin yanzu ba sai kayiwa mutun komai ba zai nufeka da sharri inji cewar chairman "wasu mutane suna nan su kawai basa son ganin cigabanka ,sun fi so kullun suganka kana bara akan titi 'acp a wuce