Showing 27001 words to 30000 words out of 163596 words
Chapter 10 - YANCNKI Book Complete by Aisha Bagudu.txt
dadi ta shiga d'akinta tana shiga ta fad'a saman gadonta ta kwanta flat tare da runtse idanunta
*******
Misalin karfe tara na dare ranar a kwance da fu'ad yake ya ciro D'an karamin diary dinta brown me d'igon ruwan zinari, daya tsinta bayan rabuwarsu da me'ad ,yana kallonsa dagani kasan me tsada ne ,ahankali ya kai diary din daidai saitin hancinsa yana shinshina, ni'imtaccen kamshin, Dior addict daya kama jikin diary sosai ,sai kawai yasamu kanshi da lumshe idanunsa tare da bud'esu duka atare cikin wani sabon alamari da ba zai iya kwatantawa ba, a lokacin fu'ad matashi ne Dan kimanin shekaru talati cif da haihuwa ,duk inda ake neman kyau ga d'a nmj fu'ad ya mallakeshi ,fari ne tass me dagon hanci da yawon suma me kyawawan idanu farare kal kuma manya masu cike da nagarta .
Cikin sand'a malik ya iso inda yake kwance ya fixge diary din yana dubawa yaga wasu mahimman file da ATM atsakiyarsa, fu'ad ya d'ago idanunsa ya kalleshi a matukar tsorace.
" uhmmmmm daman nasan ka fad'a tarkon son yarinyar nan ,amman kake wani son waskewa, shiyasa fa nace idan kana sonta ni na hakura nabar maka , kaje ka nemi soyayyarta, amman ka tsaya wani jin kai ..."kana sonta ko ba hk ba abokina?
"Tsaki fuad yaja a d'an hassale sannan ya juya masa baya "kai dai ayi D'an matsala wallahi, kaje man kayi introducing kanka agurinta Dan ni bata gabana .....
" shiyasa naga ka tsurawa diary dinta ido ba ,tare shakar kamshin turarenta? inji cewar malik yana me tuntsurewa da wata uwar dry.
Wani tsakin fu'ad yaja "kanka ake ji, ga diary din nan a hannunka kayi duk abinda zakayi dashi ,sannan kayi kok'arin ya isa gareta a duk sanda kaje gabatar mata da kanka ,ina maka fatan alkhairi tare da samun soyayyarta ...
"Dan Allah abokina, da gaske ,da gaske addu'ar samun nasara kamin? yakarasa mgnr yana me karasowa zuwa inda fu'ad ke kwance ya rike hannuwansa duka cikin nasa "na...gode abokina amman tare zamuje gidansu tunda ga addresse dinta acikin diary..?
"a'a kaje kai kad'ai ,hallo dai ina maka fatan samun nasara akanta sannan ya meida idanunsa ya runtse ya cire hannunwasa cikin na malik yana dafe goshinsa da hannunsa daya.
malik yayi saurin boye dryrsa sannan ya mike tamkar wanda akayiwa wanka da ruwan tsanyi ya isa makwancinsa "wannan shine karo na farko daya ganshi cikin damuwa hk, yammata dayawa suna kawo masa farmaki amman babu wace yaga tsan tsan damuwarsa akanta kmr me'ad, ayau suka soma ganinta amman da dukkanin alamu ta tafi da zuciyar abokinsa, ya kwanta yana dryr mugunta, domin a zahirin gsky shi ba son me'ad yake ba, amman ganin fu'ad yana neman waskewa akan sonta, yasa shi son shiga rayuwarsa tunda daman sukanyiwa junansu hk shi dasu kabeer , daga baya komai ya daidaita, Amman banda fu'ad da duk macen data kawo masa hari baya yarda ya amincewa soyayyarta ,acewarsa ba soyayya ce agabansa ba, yadda zai samu aikin da zai kula da kakarsa yake .
"itama bangaren me'ad kasa runtsawa tayi duk ta inda ta juya fu'ad take gani acikin kwayar idanunta,wani irin canji take ji a gabadaya ilahirin jikinta, ahankali take jin feeling's na bijirowa gangar jikinta wanda wannan shine lokacin na farko dataji hk ajikinta, domin duk yadda sajida ke bata labari akan yanayi makamancin hk, bata ta'ba yarda ba, ta d'auki lamarin amatsayin shirme, ashe ba shirme bane da gaske ne?" mutun kanji wannan yanayi ajikinsa idan ya had'u da abinda yake so...
kudundune jikinta guri daya tayi acikin bargonta, tana kok'arin basar da abinda take ji yana tafiya da bugun zuciyarta ,wanda a zahirin gasky mamaki faruwar hkn ya soma kamata, a kallo daya komai ba neman birkice mata....... da kyar da taimakon bacci barawo tasamu tayi bacci.
Abu fa kmr wasa kullun me'ad sai fita zaga gari ko Allah zai sa ta had'u da fu'ad amman shiru ka keji ,har kusan sati daya , tana garari agari. yadda take zariyar neman fu'ad, haka malik ke zariyar nemanta domin bata diary dinta dake d'auke dakatin ATM dinta ,da kyar ya samu shigowa cikin estate dinsu ya isa bakin tafkeken get din gidansu da'aka nuna masa, yasamu daya daga cikin masu gadi gidan bayan ya gaishesa ,me gadi ya amsa yana masa wani irin kallo sannan yace" wa kake nema?
"dan Allah ina neman me'ad.
Me gadin yayi shiru kawai yana duban malik daga samansa har kasa, ba dan yana da wata makusa ba ajikinsa, sai na talauci da babu daya nuna ajikinsa, me gadi ya sake maimaita tmbyr da malik yayi "kace kana neman me'ad ko me?
malik ya d'aga masa kai ala'mun eh.
"Ita me'ad din tasan da zuwanka ?
"Aa amman idan kashiga kace mata wanda suka had'u agurin injin din ci...
"Dakata anan da shirmenka, sannan ka juya ka 'bace daga gurin nan , daganika irin yan yunwan nan ne, jobless marasa aikin yi," kaga yarinya yar babban gida shine ka lallabo ko? "oya maza ka 'bace tun kafin ita kanta tasan da zuwanka kasha dukan banza.
Batare da mutsu ba jiki a sabule malik ya bar unguwar tamkar wanda kwai ya fashewa acikin yana mamakin girman al'amarin, sai dai kullun zai zo amman baya samun ganinta hk zai juya ya koma da diary dinta , inda fu'ad ya d'auki zafi sosai dashi "kana wahalar da kanka abanza daga karshe ka had'u da wulakaci .
"ka fahimceni fu'ad Allah ba wai .."dakata malam kaje kacigaba da bibiyarta rayuwarka ce, abinda zai min ciwo bai wuce naga ko naji kace an wulak'anta ka ba, yana karasa mgnr ya fice daga d'akin yana huci. Malik ya girgiza kansa ,tabbas ya fahimci irin son da abokinsa kewa me'ad amman ya dakewa zuciyarsa, shi zai yi iya kokarinsa yaga ya had'a ruhinsu guri daya....
*******
Yau takama litinin wanda kowa yake sauri ya shirya ya samu halatar makaranta da wuri ,ko neman aiki da sauransu , ita kuwa me'ad tana gado tana juyin da tunanin fu'ad dinta ,har kafe tara sannan ta tashi tasa aka had'a mata ruwan,tayi wanka ,nan ma sai da ta'ba lokacin gurin tunaninsa ganin take kmr yana tare daita, duk inda ta juya shi take gani har mafarkinsa take, suna rayuwar aure tare.
ahankali ta fito daga bathoorom gurin shiryawa ma sai data bata tsawon lokaci ta fito ta karya sannan takama hanya dan zuwa bank domin amsar sabon ATM.
tun da ta cusa hancin motarta cikin harabar zenieth bank ta sauya yanayin tukinta tayi parking sai dai tajima acikin motar saboda ganin kmr mutane sun yi yawa kafin daga baya ta fito, tana taku ahankali da rangwad'a tashiga .
kai tsaye gurin costume's care ta nufa , somi itace wace jinisu ya had'u daita sosai, somi na ganin me'ad ta sakar mata murmushi tare da cewa"me'ad you are welcome hade da tmbayarta abinda ke tafe daita, cikin harshen tsadadden turancinta tasoma mata bayanin abinda tazo yi, hannunta ta zura karkashin table ta zaro wani file ta mika mata tare da nuna mata wani madaidaicin office da hannunta "ki shiga can ki cike sai kawo min.
"okay me'ad ta furta sannan ta amshi file din ,cikin mintuna kad'an ta cike ta fito "ta mika mata batare da 'bata lokaci ba akayi mata komai akace taje ATM ta canza pin dinta tare da mika mata envelop ,cike da rausaya ta nufi injin cire kudi bata wani canza pin dinta ba, ainhin pin dinta na da 5996 ta sake sakawa sannan ta kama gabanta wanda dayawa mutanen dake tsaye agurin hankalisu na kanta.
Yau ma kmr kullun tana fita malik yazo gidan sai dai me gadin bai bi ta kansa ba ,saboda kallon wani mahaukaci dayake masa har sanda ta sanyo hancin motarta, ana kok'arin bud'e mata get shi kuma yana kok'arin isa inda motarta take, sauran security suka dakatar dashi, dan wani har ya kai masa mari ya goce da sauri.
Me'ad ta bishi da wani irin kallon sani ,sannan ta kusa hancin motarta cikin gida tayi parking , ta fito tana gyara zaman glass din dake manne da idanunta ,ta kira daya daga cikin masu kula da bakin get "waye wancan mutumin da kuke dambe dashi kan sai ya iso gareni?
sai da obi yayi jim..
sannan yace "wai gurinki yazo yau akalla ya kai sati kenan yana zuwa " what? ta furta arazane sannan tace.
"how dare him yazo gurina akan wani dalili ?
"hk dai yace ranki ya dade.
"Karku sake ku bashi damar sake shigowa estate din nan ballanata har ya iso bakin get din gidan"yes ma .
ta juya zuwa cikin gida tana tunanin inda tasan fuska amman sam ta kasa tunawa.
obi ya juya cikin sauri ya isa ga malik yasoma tura keyarsa "dan Allah ka saura ni abunta nazo kawo mata data yar bawani abu nazo nemana gurinta ba, amman ina sam obi yaki sauraransa har sai da kai ga fitar dashi gbdy daga estate din.
*******
tafe suke ita da sajida a Shopprit domin siyaya wa mahafinta dake jinyar hannunsa agida,kuma a yau din nan suke expecting dawowar abbansu me'ad daga kasar America wanda yaje cheek up , ahankali suke takawa kmr basu san taka k'asa me'ad na sake bawa sajida labarin fu'ad sannan suna daukar duk wani abun amfanin daya kai su bayan sun gama sukaje inda ake biyan kudi me'ad ta bada ATM dinta, suna daf da fitowa suka had'u da Malik cikin saurin yake binsu yana kiran sunanta" me'ad me'ad!! me'ad ta juyo tana ganinsa tayi saurin kawar da fuskarta tacigaba da tafiya "kai kawata wannan mutumin fa ke yake kira.. ki tsaya mana da ala'mun yasanki "baki da hankali aganni na tsaya da wannan ai sai mutane su raina da ajina .
biyota malik yayi" dan Allah ki tsaya abunki zan baki. da sauri taja hannun sajida ,haba me'ad ki tsaya mana wulakanci bashi da amfani balle d'an adam daraja garesa "bawani abun fad'a anan kawata , wancan banza nema yake na kulashi ,ni km ina i can't suka shiga motarsu cikin sauri suka bar gurin kafin malik yakaraso.
"okay mubar zancesa cigaba da gaya min labarin kyawawa nan , ko shima kmr sauran samari gari yake ?
birki taja sakamakon gitawar da wani me okada yayi ta gabanta.
ta Leko da kanta cikin bacin "kai ina zakaje kake sauri hk?
" jiki da wata banzar mgn kisawa motarki alamar koya tuki Dan da alamun baki kware ba .
" kai koya min tuki zakayi ko me ?
"Kina bukatar hkn ai.
"kutumar uban can... "kinga malama duk abinda za'a yi ayi ammam ban da zagin iyaye yar rainin hankali kawai, ko dan kinganki cikin wannan kememiyar motar kike tunanin zaki zageni na kyaleki?
sajida ce tayi masa alamun ya wuce kawai tare da cewa "kinga manta da wannan " kibani labarin kyakyawan saurayin nan da kuka had'u last week wallahi ina jin dadin yadda kike fassalta shi, me'ad tayi shiru ta kasa cewa komai ,kafin daga baya ta furta sunansa "fu'ad kenan ....
"suna me dadi tunda kike furta min sunasa naji sunan har cikin raina inji cewar sajida "Allah ko ai sai ma kinganshi kawata hadadden gaye aji farko zance fu'ad suke har suka shigo harabar gidansu sajida inda suka iske motar gidansu me'ad"kai kinga da ala'mun dady Dina ya sauka? Cikin sauri suka fito hannunwasu rike da farar laylon.
Da dariya suka shigo parlour ,n inda suka iske mahaifin sajida da nata zaune suna tautaunawa akan abinda ya faru " ai ina gaya maka Aliyu tabbas zakasamu k'arin girma nan ba da jimawa ba akan wannan kokarin naka,mead takarasa kusa da mahaifinta ta rungumeshi "dady sannu da zuwa.
"yauwa yar baba fatan kina lfy?
"ina lfy amman ba lau ba takarasa mgnr tana nufar mahaifin sajida "gashi uncle "ka gwada wannan kaji yana da dadi sosai .
" yar baba aliyu ya gaya min cewa tsalake rijiya kikeyi a wajen harbe harben da'akayi? batare data juyo ba tace "eh baba amman babu abinda yasameni ,uncle ka fa zama jarumi a gari "kalli can kagani ta nuna masa tv da yatsan hannuta, kowani gidan talbijan kai suke nunawa tun daga last Week har yau din nan sajida ta zauna kusa da mahaifinta tana gyara masa zaman bandage dake d'aure da hannunsa.
Mahaifin me'ad ya gyara zamansa tare da cewa " yar baba kawo min coffee mara madara "okay dad.
"uhm yar baba nima ki kawo min, me'ad ta nufi hanyar kitchen tana karasa shiga ta ja ta tsaya tana kiran "sajida ........
"na'am.
"a ina kika ajiye sugar?
takarasa mgnr tana kallon wasu jerin robobi dake ajiye a kitchen cabinet ,acp ya bata amsa daga zaune dayake " ai in dai wannan yar zaki tambaya ,to kuwa kin saba lamba.
sajida ta kaiwa babanta naushi a dayan hannunsa mara ciwo tana dry "kai baba "kai baba ko gsky na fada? " ko sau daya bata ta'ba shiga kitchen din nan da sunan d'aura wani abu ba, bari nazo na d'auko miki yakarasa mgnr yana me mikewa tsaye "me'ad..... sajida takirata tana murmushi nima kizo min da coffee da k'arin sugar kinji kawata.
" hmmm yarinyar idan zaki koyi had'a shayi Da kanki , ki tsaya ki koya ko Dan aure da zakiyi watan gobe "ni imran din ma nake tausayi inji cewar acp "in tambayeki yar baba, waye wancen yaron dana samun labarin yana xuwa gurinki kullun bayan ga maganar safwan da'aka ajiye "uhmmmm wannan Shashan , ai kwana hudu data wuce na fara ganinsa ban san inda yasan ni ba amman har sunana ya sani abun tsoro .
"uhmmm?
" uhmmm uncle nifa abun ya fara damuna yau ma sai da muka had'u dashi a shopping, acp ya juya zai bar kitchen din fuskarsa da ala'mun rashin yarda "uncle kar ka fahimceni ba daidai ba "ai shikenan yar baba na fahimceki ....
********
tsaye suke su duka acikin had'ad'd'en boutique dake depomu wanda yakasance mallakin mahaifin kabeer ne .wasu yammata ne su biyu suka shigo cikin harabar gurin, kowace sanye da riga iya cinyarta wanda ke nuni da yare ne, makale da yar karamar jaka suna tautaunawa, kabeer dake tsaye kusa da malik yana dan kurban fiver alive "yace kumeless tare da binsu da wani shu'umin kallo malik yayi saurin juyawa shima ya bisu da kallo ,sannan ya juyo ya kalli fu'ad yana dage masa gira kana ya sake juyowa ga kabeer "idan kabiyi wad'an yammanta kai ka zasuyi su baro ,duk bugi ne wallahi ina gaya maka. "kai dan Allah banason shirme ka juya ka kalleshi da kyau gsky sun hadu inji cewar kabeer.
Malik ya sake juyowa ahankali yana kare musu kallon tsab sannan yace "uhmmmmm wad'an yammanta lagos din suna da tsabagen wayo tsiya ,su sha kwaliya su dinga maganganu irin na birgewa, amman duk fanko suke,ya dan sake kallon inda fu'ad yake sannan yacigaba "daya nagani acikinsu me nagarta da kamalar madarar kyau ...... sudais yayi saurin cewa "da gaske ?
"yace uhm.
"kallesu da kyau kagani duk kwaliya ce kawai "yanzu kayi kok'arin kallonsu batare da kwaliya ba kagani .
"kamar yaya kenan? inji cewar kabeer .
"ka aiyana da tunaninka mana ..
"kai dan Allah banason shashanci da ala'mun fa kwal'kwaluwarka tasoma samun matsala inji cewer kabee .
"kai ne dai mahaukaci amman ni nasan abinda nake duk da cewar akwai yammata dayawa amman me'ad dina ta zarce kowa yakarasa maganar yana ware hannunwansa duka..
"kaji mahaukaci suka kwashe da dry "matar da jiya jiyan nan tagama shuka maka rashin mutunci, wai har da wani cewa me'ad dinsa suka sake kwashe da dry suna nunashi .
fu'ad dake tsaye rungume da hannuwansa duka a kirji bai kulasu ba illa fuskantar kofar shigowar dayayi tare da takaicin malik, aiko tamkar a mafarki yaga shigowarta sanyi cikin doguwar rigar abaya har kasa ta nad'e kanta da mayafin abayar hannunta rike da karamar jaka saurin runtse idanunsa yayi yana cigaba da kallonta ahankali ya mutsutsuka idanunsa" itace ko kuwa wata ce me kama daita ,tabbatar da itace yasashi saurin waskewa alokacin da suka had'a ido daita itama kallonsa ta tsaya yi cike da matsanancin mamaki ta mutsumutsuke idanunta tagani ko shaukin sonshi ne yasata ganin hk oho.
muryarta a sanyaye tace "sajida ga fu'ad dina tare da nuna mashi, tsura masa ido sajida tayi, lokaci daya numfashinta ya nemi d'aukewa ganin halitar da bata ta'ba ganin irinta ba, tana ganin kyawun imran wanda zata aura amman na fu'ad ya zarta nashi,kad'an kad'an taoma jin tsigar jikinta na tashi abinda ta kasa fassalta ma'anarsa, wani irin sanyi soyayyarsa ne ya tsarga mata ya fara bin ilahirin jikinta, take ta lumshe idanunta zuciyarta na wani irin harbawa da sauri sauri, gbdy ta kasa d'auke idanunta akanshi har sanda ya juya musu baya.
shi kuwa malik na ganinta yasoma murmushin tamkar wanda akayiwa bushara da gidan aljanna sannan yace "kai kabeer sudais itace fa gata can yarinyar nan wallahi itace ..me'ad najin hk tayi saurin riko hannun sajida "kinga wanda na nuna miki?
"uhmm sajida ta iya cewa still idanunta na kan fu'ad "wance dake sanye da kaya shine fu'ad dina amman zo mubar nan yanzu yanzu saboda banason wancan mahaukacin ya dagula min lisafi ,sai yanzu na tina shi, ranar da muka hadu da fu'ad suna tare sai dai bansani ba taren suke ko kuwa anan suka had'u, wanda nake so daban shi kuma yana kokarin hanani rawar gaban hantsi .
"haba me'ad dan Allah ki tsaya naga fu'ad din da kyau shine dai sanye da riga pinky?
"eh shine amman mu wuce kawai...
da sauri malik ya biyo bayansu yana kiran sunanta "me'ad...jimana me'ad!! dan Allah ki tsaya ya kwaso aguje su kabeer suka biyosa" kai majinun