Showing 96001 words to 99000 words out of 163596 words
Chapter 33 - YANCNKI Book Complete by Aisha Bagudu.txt
bayan faruwar hkn ba ,tun yanzu tacire rai da tsammanin da aikinta bisa kaidodinsu ,na ko fashin rana daya mutun yayi zai fuskanci babbar matsala da chairman.
"zuwa yanzu tasan komai ya rigada ya tsaya mata ,shikenan rayuwarta zata zamo abar tausayi mara amfanin ..
Fu'ad yakira wayarta sau babu adadi ,Amman batayi yunkurin d'auka ba sai hawayen datake zubarwa .
jiki a sanyaye nasreen takamo hannunta"momy !!! dady na kira ,should I pick the call?
"No......tace mata atakaice tana me runtse idanunta"why momy ki d'auka mana.......," koni na d'auka plz...?
"Pick....ta fad'a saboda batason k'arin damuwa akan wacce take ciki .
Nasreen ta d'auki wayar tare da cewa "hello dady nah.
" hello my bby How are u doing ?
"Am fine dady .
"Ina momy'nki take ?
"gata a kusa dani tana kuka,Jimmmmm yayi da ransa sannan yace "okay bata wayar.....
nasreen ta miko mata wayar "momy dady yace nabaki..
Me'ad taki kallon inda take ballanatana ta amsa wayar hannunta ,"momy plz now ki amsa wayar dady'na.
Sam me'ad taki, " ta amsa tace masa me byn cutar da yayi mata ?
"Me zatacewa mayaudarin irinsa?
"Mayaudari maci amanar kauna ......"Har abada wata kalma bazata sake shiga tsananinsu ba, kowa yaje yayi rayuwarsa ....
yana jin yadda nasreen ke mata nacin ta amsa wayar Amman taki , tswon minti biyar wayar na tafiya sannan nasreen ta meida wayar zuwa kunnenta tana sauke numfashi "dady........
"taki amsa ko ya fad'i hkn Dan yasan abinda zata ce masa kenan ?
"Don't worry bby, yanzu kuna ina, na dawo hospital doctor yace yayi discharging naki ,na dawo gida bangan bbynah ba,gashi nayi missing dinki ,I want to see ur beautiful face, tayi murmushin jin dadi sannan tace "ai daga hospital gidan grandpa muka wuce nan tashiga koro masa duk abinda ya faru akan idanunta ,fu'ad ya samu guri ya zauna yana mai runtse idanunsa yana jin wani irin zallar 'bacin rai da tunda yazo duniya bai ta'ba jin irinsa ba, wani irin tafarfasa zuciyarsa ke masa "why me'ad ? Ya furta a raunane.
"Me yasa zata masa hk.? Ahankali ya hau sauke numfashi cike da takaicin dabbancin abinda me'ad tayi masa, ya d'auka iya shekarun da sukayi tare shi daita sun zama abu daya, sannan sun wuce wannan nevel din ,tazama shi shima yazama ita, sun chakud'e guri daya ta yadda duk runtsi duk wuya babu wanda zai ji kansu balle mahaifinta, daya fito ya nunawa duniya bayason zamansu tare, Sautin muryar nasreen dayaji cikin dodon kunnenshi ne yasa yayi saurin bud'e idanunsa "dady da gaske ne zaka auri aunty sajida da najma me aiki Dan kayiwa momy'na kishiya dasu?
Yayi shiru kawai ya kasa bata amsar tambayarta, sai ma d'aura hannunsa da yayi ya dafe goshinsa dashi yana shashshafawa ahankali ahankali ,while kirjinsa na bugawa da sauri sauri.
"daddy matukar da gaske zaka auresu ne ,plz change your mind, dan banason kayiwa mamana kishiya saboda banaso ganita cikin damuwa, saboda nima zan shiga cikin damuwa yanzu haka kirjina ciwo yake min dady tak'arasa mgnr kmr zatayi masa kuka .....
Muryarsa a matukar kasalance yace "bby kina bukatar kulawa wanda momynki ta kasa tsayawa ta baki, ni kuma amatsayin na mahaifi ba hurimina bane ,wannan hanyar kad'ai ce zatayi min maganin matsalata saboda nasan idan na auresu zasu kula dake shine dalilin....
" Amman ki za'bawa dady'ki mutun daya acikin auntynki sajida ko najma wanda kike son na aura ta zauna tare dake amatsayin second momy dinki, wace zata cigaba da kulawa dake da dady'nki..
"ni banason dukkansu ,ni banason kowa ni nafi son mummy'na kawai ..........
ya sake runtse idanunsa gam" yanzu kuna ina?
" zanzo na sameku na dawo daku gida, ta d'aga kanta tana duban yanayin gurin ta cikin mota, idanunta ya sauka akan wani green sambod da aka rubuta *main land bridge* Dan hk ta sanar masa a matukar firgice ya bud'e idanunsa ,gabadaya ya gigice ya kid'eme muryarsa na rawa yace "main land bridge?
"Yes dady shine abinda nagani ,yace "ki sa wayar a handafree.
Aiko take nasreen tayi abinda dadynta ya umarceta cikin d'aga murya yace"me'ad kina hauka ne, dazaki kai min yarinya har main land bridge?
"Wai meyasa kike son meida kanki wawiya ne akan yar kankanuwar matsala?
Tayi masa banza taki cewa dashi komai ,shi km ya dinga zuba mata bakaken maganganun ta inda yake fita bata nan yake fita ba still tana jinsa taki cewa komai, Dan idan tace zatayi mgn zagi ne zai fito daga cikin bakinta da hk tacigaba da sauraransa kawai take tana jin zallar 'bacin rai na ratsata, hawaye na bin kuncinta ji take a duniya yagama tozartata, ya gama wulakanta da abinda yake son mata,ganin taki kulasa yasa ya sausauta muryarsa,
"Kiyi kokarin dawo min da yarinyata so that ke ki cigaba da zama agurin tunda abinda kika za'barwa kanki kenan .
yana gama fad'ar hk ya katse kiran,Wanda alokacin ita kuma tayiwa motarta key dan tasan Sarai zai iya zuwa ya samesu agurin tunda yaji inda suke.
me gadin gidansu takira taji ko fu'ad din na gida , ya tabbatar mata da yanzu ya fita, hasashenta ya tabbata kenan, zuwa zai yi ya amshi nasreen din ya barta da tarin bakinciki da damuwa, kai tsaye gidansu ta nufa, bata tsaya bata lokaci ba tashiga ta dibi abubuwanta datasan masu amfani ne gareta, dana yarinyarta ta kulle kofarta ta fito tashiga mota tabar gidan.
Yayinda fu'ad Yayi maya tafi sau hud'u akan main land bridge, ya hau ya sauko Amman bai ga alamun tsayuwar motarta ba ko alamun wata motar daban ba ,gashi yana kiran wayarta taki d'auka haka ya hakura ya koma gida yana jin zallar bacin rai yana shiga gidan jikinsa yabashi tazo gidan . Da sauri ya fito ya isa gurin me gadi yana kwalla masa kira ,me gadi ya k'araso ya tsaya agabansa "maman nasreen tazo ne byn fitata?
"Eh yalla'bai tazo bata ma dade sa fita ba wani irin takaici yaji kmr ya d'aukeshi da mari, a fusace ya juya ya komai cikin gida yana huci gabadaya ya rasa meke masa dadi ,hankalinsa ya sake tashi so yake yasoma neman inda najma take Amman bashi da natsuwar zuciya a kalla ya kusan minti goma tsaye yana tunanin mafuta ya duba agogo karfe karfe biyar ta kusan ciki" ina bai ga ta zama dole duk yadda zaayi sai yaga me'ad da nasreen tare da dawo dasu gida sake bazama yayi ya fito harbar gidan kallo daya zaka masa kasan baya cikin natsuwarsa yashiga motarsa aguje ya bar gidan.
*********
A bangaren mahaifiyar me'ad kuwa kuka take a tun fitar me'ad gidan ,taso kiran fu'ad Amman ta kasa saboda a yadda zuciyarta ke cike da 'bacin rai zata iya gaggaya masa komai yazo bakinta ,abinda bazata so faruwarsa ba kenan atsakaninta da surinkinta ,me mutuntata da ganin kimarta, ita batace kar ya kare aure ba ,"amman meyasa sai sajida da najma?
Tasan zai auresu ne Dan kawai ya kuntatawa zuciyar mead dinta...
gidan yayi shiru kmr anyi mutuwa Dan koda suhailat ta dawo daga makaranta taji labarin abinda ya faru mutuwar tsaye tayi agurin, itama hankalinta yayi mugu mugun tashi..
ta dinga mamakin cin amana irin na sajida a ganinta har gara auren najma akanta.....
Bangaren me'ad kuwa yawo ta dingayi acikin gari, daga wannan titi zuwa wancan titi,tarasa inda zata taji sanyi aranta ,tayi tunanin zuwa dangin momy'nta Amman sai taga kmr zata tonawa kanta asiri ne, a yanzu ta d'auki darasi me girma a zamanta da sajida, bazata sake yarda da kowa ba arayuwarta ,zata koyi rike sirrikanta ,zata bawar cikinta damuwarta bazata sake sharing secret dinta da kowa ba bayan mahaifiyarta, itama Dan tasan bazata gayawa duniya bane ko ha'intarta sai dai ta d'aurata bisa turba .daga karshe zuciyarta ta bata shawarar takama hotel kawai ta cigaba da rayuwarta har zuwa sanda mahaifinta zai sauko ya amsheta ,bazatayi fushi dashi ba ,haka zalika bazata gaji da rokonsa ya yafe mata ba, har sanda zai furta ya yafe mata.
Dan hk Kai tsaye wani had'ad'en hotel ta nufa me suna city hotel, cikin Dan kankanin lokaci ta isa kawataccen hotel din Wanda hotel ne ,na isasu ta d'aki ,daya daga cikin mai'aikatan hotel din yayi gaba rike da key'n d'akin ita kuma tabiyosa abayan rike da hannun nasreen ,byn ya bud'e mata d'akin ta mika masa key'n motarta domin shigo mata da kayanta, ya amsa juya cikin sauri, suka shiga ta meida murfin kofar ta rufe .
Komai na agyare neat a acikin Had'add'en d'aki .
Ko cikakken minti biyar baayi ba maaikacin yashigo da akwati kayansu ya ajiye ya sake fita, ita kuma takarasa tayiwa kofar key tare da barin makuli ajikin kofar ta dawo ta tsaya atsakitar d'akin tana k'arewa falle d'akin daya kallo wanda ya k'awatu sosai , doguwar kujera kwaya daya ajiye , da TV bango sai air condition ,babban wardrobe na zuba kayan sawa daga gefe, mirrow da bedside, daga can bangaren toilet ne me murfin glass .
d'aki ne mai matukar kyau da fad'i ,ta d'auki lokaci tsaye tana k'arewa d'akin kallo sannan ta K'arasa ta kunna ac tare da rage karfinsa saboda nasreen ,
Jikinta a matukar sanyaye ta janyo hannun nasreen jikinta ta rungume yarinyar naji dumin jikinta muryarta a sanyaye tace "muje bbynah kiyi wanka nasan kin gaji dayawa ko?
Murmushi nasreen ta sakar mata sannan ta sake shigewa jikinta, "momy meyasa kika kawomu nan ?
"Mu koma gida nasan dady zai shiga damuwar rashinmu, plz momy mu koma ...
"Shiiiiiii kiyi shiru da zance komawar nan har abada nasreen bazan komawa mahaifinki ba ,idan kuma kinfi sonshi da son zama tare dashi akaina fine I can take you to him right now. "Ki kwantar hankalinki zamuyi rayuwa kmr muna gida kinji bby, zan siya miki duk abinda kike ,zamu dinga kallon TV tare muna enjoy ki manta da wani dady okay"taja hannunta suka shiga bayin tayi mata wanka da ruwan zafi ,tana tsaye akanta tayi alwala suka sake fitowa tare daita daure da towel.
tsab mead ta gyarata ta sauya mata wasu kayan masu kauri, ta Mike mata hijabi, "kiyi sallah kafin na fito, sannan ta juya ta sake komawa cikin bayi.
Mmn sudais ce
[11/3, 8:29 AM] El~hajj: 💗💗💗💗💗💗
'YAN CINKI
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
~NA~
*AYSHA A BAGUDO*
~DEDICATED TO~
FAIZA HAMMADU BARAU
(YAR NUMAN)
Page 78
........tsaye tayi acikin bathtub din ,ruwa na tsiyaya akanta zuwa sansar jikinta,Wanda ke saukar mata da natsuwa kad'an saboda har wannan lokacin bakinciki abinda sajida da fu'ad ke shirin yi mata, yaki barin zuciyarta da gangar jikinta, "ta yaya zata iya sharing din fu'ad dinta da wata macen ,macen ma aminiyarta da suka taso tare... ?
"Suke yin komai nasu tare sannan babu abinda bata sani ba na sirrukan rayuwarta....
"A gurinta Fu'ad ba kmr sauran maza bane ,daban yake acikin mazan datake kallo , sannan natsatse ne kamili Wanda yasan ciwon kansa ,tana son shi fiyye da rayuwarta sai dai bata jin zata iya ganinsa yana rayuwa tare da wasu matan byn ita,tafin son duk runtsi duk wuya su kasance tare suka k'arasa rayuwarsu .
Ahankali take tuna moment dinsu dashi ,duk da ba wani bashi had'in kai takeyi ba ,amman hkn baya hanata jin dadin abinda yake mata. "Anya kuwa zata iya rabuwa dashi kmr yadda ta fad'a tayi rayuwarta ita kad'ai sai yarinyarta?
"Anya kuwa ba wata cutar Kan zata sake yiwa rayuwarta ba ?
Tayiwa kanta tambayar tana jin jikinta yana sauyawa, ahankali take jin feelings dinsa na bijiro mata duk da bata tsamaci zata ji hkn ba akansa, a wannan tsayuwar datake komai na rayuwarsu ke dawo mata daki daki cikin kwakwaluwarta ,yanzu ace agida ne kuma suna zaune lafiya dashi zai shigo bayin ,ya tsura mata kyawawan idanunsa masu maseefar burgeta da tsaya mata arai ,yana kare mata kallo ko kifta idanunsa baya son yi daga karshe kuma ya k'araso gareta ya riko kugunta yana me had'eta da jikinsa tare da shafa kirjinta yana goga mata gashin dake zagaye da fuskarsa zata lafe akirjinsa , koda kuwa bai yi niyyar yin wanka ba ko kwanciyar aure daita ba ,ganinta tsaye babu kaya zai janyoshi yayi koda kuwa acikin bayi ne yayinda ita kuma zata shiga tutturesa tana kukan shagwaba ita tagaji bazata iya da jarabarsa Amman ba zai ta'ba kyaleta ba har sai yacima burinsa akanta duk yadda tayi ta yakice tunaninsa abun yaci tura haka tayi ta tunaninsa ..
ganin tunaninsa daya d'arsu a zuciyarta yaki barin tayi abinda yashigo daita ,yasa ta sauke naunayen ajiye zuciya sannan tasoma sa'bawa jikinta sabulu ,sai dai duk inda ta gogo sabulu ajikinta sai taji kmr tafin hannunsa ne ke yawo ajikinta Dan haka tayi
Shap shap tayi wanka ta d'auro alwala ta fito ,koina a d'akin ya kama kamshi room freshener da'akayi amfani dashi .
jakar kayanta ta bud'e ta ciro doguwar riga ta sanyawa jikinta ta k'arasa inda pray mate yake ta tada sallah byn ta idar da sallah s ta janyo akwatin kayansu ta fiddosu daya bayan daya tasoma jerawa cikin wardrobe nasreen na tayata miko mata, wasu suna hirarsu cikin farinciki duk da ita ba wai nufinta tayi hkn ba ,Amman ya zame mata dole ko dan kwanciyar hankalin diyarta da lafiyarta ,batayi sha'awar kunna makeken TV dake makale da bangon d'akin ba ,Amman saboda ta d'bewa nasreen kewa yasa ta tashi taje ta kuna ta dawo tacigaba da aikin jera kayan.
byn tagama jira kayansu ta tmbyi nasreen ko zata ci abinci Dan ita bata jin cin komai ,yarinyar tace " ba yanzu ba sai zuwa anjima momy , Dan kafin me'ad ta yanke shawarar zuwansu hotel ta sai mata snacks taci a mota .
Kwanciya tayi akan gadon tabar nasreen na kallo ,ahankali ta runtse idanunta domin ta samu hutu da natsuwar zuciya, Kafin lokacin sallar magri tayi ,tunanin mijinta ne ya sake sanyo kai cikin zuciyarta dama gangar jikinta, wani irin sabon yanayi ta tsinci gangar jikinta ciki yayinda wani feelings dinsa yashiga bijiro mata idanunta har sun sauya, da kyar tasamu ta yakice shi ta Mike ta janyo system dinta data jona a caji ta kunna tasoma dudduba sakonin da aka turo mata ,cikin haka kiran chairman din company din datake aiki yashigo wayarta, take gabanta yashiga dukan uku uku ,da kmr karta d'auka Dan bata son K'arin tashin hankali akan Wanda take ciki ,ammam ta sanshi tasan halinsa shima ba kwanwar lasa bane ,Akan company dinsa babu abinda bazai iya yi ba ,Dan HK tayi saurin sanyawa jikinta kuzari ta d'auka ta manna wayar a kunnaneta tana gaisheshi a natse ya amsa tare da cewa "muna bukatar ganinki gobe by 10 :am atakaice tare da katse kiran ,jikinta yayi sanyi kmr wace akayiwa wanka da ruwan sanyi ,gbdy takasa cigaba da operating system din dake gabanta, ta ture system din gefe ta janyo nasreen ta rungume ajikinta hawaye na gangarowa daga cikin kwarnin idanunta ,"jikinta na bata aikinta ya kusan zuwa karshe.....har aka kira sallah magariba tana makale da nasreen tana jin karfin gwiwa a duk sanda ta rungumeta yayinda take cikin damuwa,ahankali ta zameta daga jikinta ta kwantar a saman cinyarta ta tsura mata ido kawai tana kallonta wani irin kaunar yarinyar nabin jikinta bacci take har lokacin tana sauke numfashi ahankali, ta Mike ta tashi taje tayi alwala bayan ta idar da sallah bata tashi ba tacigaba da zama tana lazami tarenda kaiwa Allah kukanta.
*********
Misalin karfe tara na dare mumy ta samu dady ad'akinsa cikin yanayi na rarrashi take ce masa "dady sam abinda kayi bai kamata ba ,yakamata kabi komai ahankali hannunka baya ru'bewa kace zaka yanke ka yar duk abinda me'ad tayi maka duk lalacewarta bazaka ta'ba canzata amatsayin diyarka ba ,kalaman daka furta mata a yau din nan yayi muni dayawa.....
dady yasoma magana cikin 'bacin rai "ina amfaninta arayuwata?
"Meye amfanin D'an da bai jin maganar iyayensa da yi musu biyayya?
"Ni tsine mata ma naso yi tabi uwa duniya kowa ya huta ,dady yana fad'ar hk numfashinsa ya fara sama sama sai faman haki yake ,mummy tana ganin hk ta fara salati game da waige waigen Kafin kace me tuni dady ya fara fita haiyacinsa ,mummy tayi matukar rud'ewa sakamakon numfashinsa daya tsaya a matukar gigice ta kwallawa suhailat kira itama tashigo d'akin a rud'e tayo gurin momy dake jijigasa , tare da taimakon sulahait suka dawo da dady parlour'n, ruwa sanyi mummy ta dinga shafa masa sannan ya dawo haiyacinsa ya jike sharkaf da ruwa kwance ya ganshi ajikin momy wacce idanuwanta tuni sun dade da yin luhu luhu saboda kuka, dady ya d'ago idanunsa ya kalli momy da take faman tofa masa adduoi, da kyar dady ya iya bud'e bakinsa "wai ,abinda nake tunanin ne ya faru..?
Mummy tace " a'a babu abinda ya faru ina dai tunanin BP dinka ne ya tashi bara nai ma doctor waya yazo ya duba ka.
Jikin momy na rawa ta tashi daga gun datake zaune tana rungume da dady tmkr wani karamin yaro ,bedroom dinta ta nufa ta d'auko wayarta dake ajiye akan gado ta fara lalubo lambar cikin kankanin lokacin takira doctor ya d'auka ,ta fad'a masa duk halin da'ake cikin doctor yace "gashin nan zuwa .
Doctor Peter ya faka motarsa ya fito da sauri ya nufi hanyar da zata