Header Ads
Showing 1 words to 3000 words out of 171869 words

Chapter 1 - BIBIYATA YAKE YI COMPLT Document by Zainab Bawa.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jun 2024

1057

Ads at the middle of Article


BIBIYATA YAKEYI
(WAYE SHI?)
ZAYNAB BAWA


Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
*Y'AR FARI*
*YARIMA FAYAD* paid 200
*ƘADDARAR RAYUWA*


*Assalamu alaikum barkanmu da warhaka*


INA MASOYANA WANDA SUKA KARANTA LITTAFIN BIBIYATA AKEYI 🤝 WANNAN SALON SHEKARAR 2017 NE, YA KUKAJIN LABARIN? NASAN DA YAWANKU BAKU MANTASHI BA!


TO MASOYA GANI NAN NA KAWO MUKU WANI ZAZZAFAN LABARI MAI CIKE DA SALO KALA KALA!!! WANNAN SABON LABARI SHINE BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI).


WANNAN SALON 2023 NE! SABON LABARI SABON SALON LITTAFI DABAN YAKE DANA BAYA BIBIYATA AKEYI!


BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI) PAID BOOK NE BA FREE BA.🤝








*Allah yabani ikon rubuta muku abu mai amfani kamar yanda nafarashi Lafiya Allah yasa nagamashi lafiya.*




Page 1


Jin alamun za'a shigo ɗakin ya sanya nayi saurin ɗauke idanuwana daga kan madaidaiciyar tv ɗin dake manne ajikin bango nayi saurin maida hankalina ga littafin dake gabana. Da sallama ta buɗe labulan ɗakin ta shigo ta zauna a ɗaya daga cikin kujerun da suke cikin falon. Matashiyar matace wacce bazata wuce shekara talatin da takwas ba. Kallona tai ta taɓe baki ta zare remote tana faɗin.


"Nida ɗakina amma ban isa abarmin tashar dana keson kalla ba kulllum sai dai wannan tashar kwallon ta jaraba, ke kina mace ni bansan mai ya hadaki da wannan kallan kwallon azabar ba."


Nidai bance komai ba harta canja tashar ta maida zuwa tashar shirye-shiryen Hausa sannan ta ajiye remote din. Mikewa nayi ina zumburo baki nafice daga ɗakin ina jiyota tana faɗin.


"Dama nasani wannan karatun na munafunci ne kallon ball kawai kike yi."


Nidai bance komai ba na wuce zuwa ɗakin matar mahaifina wacce muke kira da Aunty na zauna na cigaba da kallon ball ɗina acan. Sai da aka gama sannan raina yayi sanyi domin tawagar da nake so itace ta lashe wasan kwallon. Raina fess na fito na nufi ɗakin mahaifiyata. A uwar daki na sameta na shiga na zauna tana faɗin.


"Angama kallon ball din kenan?" Batareda ta jira amsata ba ta cigaba da fadin. "To sai amaida hankali maza ayi karatu tunda angama ibadar." Zumburo bakina nayi nace.


"Nifa dama Mama na rigada nagama karatu, kawai bita nake yi."


"Gara dai ki maida hankali kiyiwa kanki faɗa Mamee kitsaya kiyi wannan karatu dakyau ke kanki shaida ce kinga yanda aka samu kika fara wannan karatu, har indai kikaki nutsuwa kici wannan jarabawar kika fadi kinsan yanda mahaifinku zai ji. Idan kuma so kike ki karasashi toh, kina gani dai da ya ya aka yi aka hado har dubu casa'in aka biya miki rijista dan kawai kin nuna kina so, idan kika zuba masa kasa a ido baki yiwa kanki adalci ba. Ki daure kiyi karatu kici weeding ɗin nan in sha Allahu har indai kin wuce zamu san yanda zamuyi mu hada karfi da karfe wajan ganin mun taimaka kinci gaba. Idan kuma kika tsaya wasa kika fadi ko shakka babu nasan cewa aure babanku zai yi miki da karancin shekarunki dan ya samawa kansa saukin rayuwa. Amma idan kinci wannan jarabawar koda ace auren ya yi miki sai mijinki ya karasa daukan nauyin karatun naki ki karasa agidansa." Saurin girgiza kai nayi nace.


"Dan Allah Mama ki daina fadin haka, zanyi karatu kuma in sha Allahu zanci." Sai da ta kalleni na wani lokaci sannan tace.


"Shikenan Allah yasa." Nace,


"Amin." Saboda yanda nakeso naci jarabawar nan haka na hana idanuwana runtsawa sai da na raba dare sannan na kwanta.


Washe gari kuwa kafin kowa ya tashi na tashi kusan kaff gidan na rigasu tashi ina jiyo mahaifinmu zai fita sallar asubahi yana bubbuga kowa ne ɗaki domin atashi ayi sallah. Ina idar da sallah na shiga wanka na shirya ban tsaya karyawa ba dan karfe bakwai zan shiga jarabawa mama tabani kudin abun hawa nafito harabar gidan babu kowa haka naabude karamar kofar dake jikin gate dinmu na sanya kaina nafice yar, dakyar nasamu abun hawa nashiga yawuce dani makarata zuwa 12:00pm nagama duk wani abunda zanyi a makaaranta na nufo gida dan ban fita ta ishesshen kudin da zai isheni nayi karin kumallo ba kuma yunwa nakeji shiyasa ina gama abunda zanyi na nemo hanyar gida dukda kasancewar bawai dama ina tsayawar bane,


Da sallama na shiga gidan a tsakar gida na samu Mamana da Anty suna gyaran shinkafa sannu nayi musu sannan nawuce ciki na cire kayan jikina na sanya kayan gida sannan na nemi abunda zanci, sai da na tabbatar cikina ya ɗauka sannann na fito izuwa cikin gida na zauna na sanya hannuna a cikin gyaran shinkafar ina yi ina kallon agogon wayar Mama domin kar lokacin da za'a fara wasan kwallon ya yi bana kusa. Da sauri na mike ganin baifi saura minti 2 biyu afara wasan ba Mama tana magana ko jiyota banayi har nakai daki na canja tasha na zauna kallon kwallon.


Ko kawarda idanuwa na bana yi dan bana so wani abun ya wuce ni ba tare da na gani ba duk da kasancewar yau ba team din da nake supporting bane suke buga wasan, Daya daga cikin dan wasan kwallon ya zura kwallo araga wani irin ihu nasaki daya sanya mama ta mike ta shigo ɗakin ina kallonta na bata fuska dan nasan saita hanani kallon kwallon nan. Aikuwa hakan aka yi domin masifa ta fara yi min tana faɗin.


"Sai yaushe zakiyi hankali Mami? Kin gwammaci kibar iyayenki suna aiki kizo ki zauna kallon banza? Kina ihu kamar tababbiya? Toh wallahi gara ki mike tun kafin mahaifinki ya leko yaga muna zaune muna aiki ke kuma kinanan kina kallo kin san ranki da namu gabaki daya baci zai yi." Na karairaye murya nace.


"Wallahi Mama nagaji kinga yanzu na dawo daga makarantar nan kuma zuwa jimawa karatu zan shiga dan Allah kiyi hakuri na zauna na ɗan huta." Mama tace.


"Har mai kikayi da zaki gaji? Ki tashi tun kafin ran mu duka ya ɓaci."


Mikewa nayi raina bai so ba na koma cikin gida mukaci gaba da gyaran shinkafar, muna gamawa na karɓa na shige kitchen na zuba ta a cikin tukunyar dake kam murhu wacce tun ɗazu take tafasa. Haka a tsaitsaye na taya su muka karasa aikin hankalina yana wani waje daban. Muna zaune mu dukkan mu a cikin gidan mahaifina ya shigo cikin girmamawa dukansu matan suka yi masa sannu da zuwa, ni kuma na gaisheshi dake yau fitar sassafe nayi bamu gaisa ba. Ya amsa cike da kulawa yana faɗin.


"Ya ya jarabawar?" Nace.


"Alhamdulillah da zarar munyi gobe mun gama." Yace.


"Toh Allah ya bada sa'a, amma da zarar kin gama taya su aikin saiki tashi kije kici gaba da karatun koh kar ayi wasa."


"Insha Allahu bazan yi ba Baba."


"Toh shikenan Allah yayi miki albarka." Mu dukkan mu muka amsa, yana gama magana yayi sashinsa Aunty dake itace da girki ta tashi ta bishi,


Muna zaune ƙananun ƙannena suka dawo daga makaranta. Mama tace na tashi na taimaka musu su canja uniform izuwa kayan gida. Nan na samu hanyar barin wajan da sauri na mike na shige ɗakin Aunty na fara taimakawa yaranta suka shirya. Gabaki daya yaranta guda uku ne babbar ba tafi shekaru takwas ba Meema sai twins Hassan da Hussain. Ni kuma a wajan mahaifiyata ina da ƙannena guda biyu dukkan su maza ne, Sadeeq sai Amir. Sai da na fara shirya su Meema sannan na fito daga ɗakin Aunty na shirya su Amir. Ban yarda na koma cikin gidan ba dan na san wani aikin zan riske dan haka na zauna karatuna. Koda akayi la'asar ban damu da saina tashi ba tunda nasan cewa ba sallah zanyi ba.


Washe gari kamar jiya da sassafe na fice daga gida dan zuwa zana jarabawata ta karshe. Alhamdulillah babu laifi jarabawar tayi daɗi sosai ina gamata na sanya kai na dawo gida ba tare da na tsaya wani abun ba.


Yau kam na tsaya na taya su aiki sosai dake na san ba jarabawa gareni washe gari ba kuma aranar babu wata kwallon da za'a buga. Yau kam na huta da fadan Mama dan sam ba tayi min shi ba, koda yake dama takance duk ranar da babu wasan kwallon kafa nafi kowa hazaka wajan aiki a gabaki ɗaya kaff gidan mu.


Yau ta kasance ranar Asabar tun safe na shirya kannena na sakasu a gaba muka tafi islamiyya, da safe ake zuwa duk ranar sati ba zamu dawo ba sai yamma. A kafa muke tafiya dake bawani nisa ne tsakanin haddar tamu da gidan mu ba, sai da na tabbatar kowannen su ya shiga aji kamar yanda na saba sannan nima na wuce nawa ajin.


Karfe sha biyu Aunty da kanta ta kawo mana abinci kamar yanda ta saba, bayan an fito sallah na haɗe kannena dukkan su muka zauna mukaci abincin sannan na ɗauki ƴan canjin dake jikina na saya mana ruwa dashi.
Wannan al'adar makarantar mu kenan karfe ɗaya muke fitowa kowa yaci abinci sannan ayi sallah mu koma aji ba zamu sake fitowa ba sai sallar la'asar karfe biyar kuma a tashe mu mu koma gidajen mu. Bayan an tashi sai da nabi ajin kowanne na dauke su sannan na sanyasu agaba muka wuce gida.


Washe gari lahadi ma hakan take kasancewa acan makaranta muka wuni, sai dai yau Hussaini ya tashi da zazzabi sosai amma haka Anty tace dole sai yaje makaranta acan zai warware. Misalin karfe sha biyu muna zaune a aji malamin su Hussaini ya aiko a kirani, ina zuwa na samu jikin Hussain ya yashi zazzabi ya rufeshi sosai, sai malamin yayi min umarni dana kaishi gida na dawo. A bayana na goyashi na nufi gida, ban samu Anty ba ta fita dan haka ɗakin Mama na wuce dashi.


Bandaɗe da shigowaba Anty ta shigo ta samu halin da ake ciki, pracetamol Mama ta bashi muna nan a kansa har zazzabin ya fara sauka, Anty ta dubeni tace.


"Mamee ki koma makaranta sannan kibi kitchen ki ɗauki kular abincinku ki tafi muku dashi. "


Da toh na amsa ina shirin fita sai ga sallamar Baban Yayan mu Ahmad Mama tace.


"A'a wanakeji kamar Ahmadu? ashe kana hanya?" Karasa shigowa yayi yana faɗin.


"wallahi ina hanya." Sannan ya gaida ita ta amsa tana tambayar.


"Yaya Maman taku acan?"


"Lafiyanta qalau." Ya bata amsa. Nima na gaishe shi ya amsa sannan ya dube ni yace.


"Me kuma kike yi agida bayan yanzu lokacin makaranta ne? Mama ta karbe zancen da faɗin.


"Kaga Hussaini ne babu lafiya shine ta dawo dashi yanzu." Uhm kawai yace Anty ganin bayi da niyyar gaidata ya sanya tace.


"Ina wuni?" Ba tare da ya kalleta ba ya dubi Mama ya canja zancen da fadin.


"Bari naje wajan Baba dan yanzu ma daga wajan nasan nake nace barina shigo mu gaisa." Mama tace.


"Toh shikenan nima zan shigo yanzu dan bai san da rashin lafiyar Hussainin ba."


Mikewa yayi ya fice jikina duk ya yi sanyi da naga yanda ya yiwa Aunty, ko dan izuwa yanzu ya kamata ace wannan lamarin yabi mana jiki amma gabaki ɗaya ya kasa bin jikin mu. Jiki a sanyaye na fito na nufi kitchen na daukar mana abincin mu na fito wajan Baba na hanga da takalman mata guda biyu sai na Ya Ahmad daya shigo yanzu.


Toh su waye waɗannan matan? Dan nasan cewa idan banda Mama da Anty babu wata mace mai shiga dakin2 Baba sai mu Yayansa, kuma nasan su Mama ma basu san da zuwansu ba. Ganin banida amsar tambayata kuma banida lokacin tsayawa ganin ko su waye dan yanzu kannena na can suna jirana. Fita nayi na wuce zuwa makaranta koma su waye idan na dawo nasan tabbas zanji.








PAID BOOK
Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab m Bawa JAIZ BANK shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya zan sanyaki a group Hankli kwance zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike."




✔️ote
Comment
Like
Share please


To be continued


Zaynab Alabura."






*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡


*BIBIYATA YAKEYI*
_(WAYE SHI?)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*








BY
ZAYNAB BAWA


Assalamu alaikum
Ina kuke manyan mata?


Matanda suka san kansu, Suka amsa sunansu Mata, Amarya, Uwar gida shin kin taba using kayan *ROYAL EXQUISITE* kuwa??? Idan kin taba to barkanki danna tabbata kin fita daban da sauran mata, idan Baki taba ba kuwa lallai an barki a baya kuma kin dade kina cutar kanki da mijinki, Domin samun kayanmu masu kyau da inganci zaku iya tuntubarmu domin munada Kayan mata masu kyau da inganchi Kamar su
Virgin again
Tightening pills
Turaren ban mamaki
Sweetness agents
Wetness agents
Infection set da sauransu
Domin ƙarin bayani ku tuntubemu ta wannan numbern
08030644073




Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
*Y'AR FARI*
*YARIMA FAYAD* paid 200
*ƘADDARAR RAYUWA*




*Assalamu alaikum barkanmu da warhaka*


INA MASOYANA WANDA SUKA KARANTA LITTAFIN BIBIYATA AKEYI 🤝 WANNAN SALON SHEKARAR 2017 NE, YA KUKAJIN LABARIN? NASAN DA YAWANKU BAKU MANTASHI BA!


TO MASOYA GANI NAN NA KAWO MUKU WANI ZAZZAFAN LABARI MAI CIKE DA SALO KALA KALA!!! WANNAN SABON LABARI SHINE BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI).


WANNAN SALON 2023 NE! SABON LABARI SABON SALON LITTAFI DABAN YAKE DANA BAYA BIBIYATA AKEYI!


BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI) PAID BOOK NE BA FREE BA.🤝










PAGE 2




Bayan fitarmu daga ɗakin gabaki ɗaya, Mama ta dubi Anty ganin yanda jikinta yayi sanyi duk sai taji babu dadi, cikin karfafa guiwa Mama tace.


"Kiyi hakuri idan wannan abun ne yaci ace yanzu ya zame miki jiki ya daina damunki gabaki ɗaya. Kuma ina da tabbacin wata rana zai shude ya zama labari kamar hakanma bai taba faruwa ba."


Saida Anty tayi murmushi mai ciwo sannan tace.


"Mama dole na damu domin ba yanzu bane lokacin damuwar, lokacin da abun zai zama wani iri nakeji, ina matukar tausayawa yarana dan sune kananu acikin gidan nan. Kuma sune wanda basu da farin jini, inaji ajikina ba zasu taba son yaran da na haifa ba. Yau idan akace babu ni yarana basu da makama tunda sune manya sune danginsu kadai kuma basa son su, gara ke koda yaranki basu tasa sosai ba amma kina da dangi wanda zasu iya rike miki yaranki kuma basajin haushin naki kamar yanda suke jin haushin nawa yaran, ni ba uwa ko uba gareni ba bare nayi tunanin ko babu ni nabar wanda zasu kulamin dasu." Mama ta katseta da fadin.


"Haba Habiba wai me yasa kike haka ne? Duk me ya kawo wannan zancen? In Allah yayarda Allah zai barmu akan yaran mu har zuwa girman su." Anty ta share kwallar data zubo mata tace,


"Shikenan na daina yanzu kishiga ki fadawa babansu jikin Hussainin danni idan na shiga sai ya zama wani abun daban."


Mama ta mike ta fice daga dakin. Ganin takalma a kofar dakin Baba ya sanya ta tsagaita kamar bazata shigaba sai kuma tayi sallama ta shiga. Dukkan su wanda suke palourn suka amsa mata sallamar,


Kujerar dake kusa da ta Baba ta karasa ta zauna tana karewa yan mata guda biyu dake zaune kasa kan carfet kallo fuskarta dauke da fara'a tace.


"Ikon Allah wa nake gani kamar Fadeelah da Ayusha? Lallai sun girama masha Allah shekaru da yawa ba'a hadu ba." Baba yace.


"Sune kuwa, shekaru dayawa kam, yanzu nake niyyar na aika a kirawoku gabaki daya domin yayansu yazo min da wani zance." Mama tace.


"Toh ai gamu bari nakira Habiban tana tare da Hussaini yanzu Mamee ta dawo dashi daga makaranta zazzabi ya rufe shi."


"Allah ya sauwake." Shine abunda Baba ya fada sannan ya dubi Fadeela da Aysha yace.


"bakuga Mamanku bane ba? Ba zaku gaidata ba?" Fadeela ce tafara faɗin.


"Ina wuni?" Mama ta amsa fuska a sake sai Aysha ma tabi bayanta suka gaisheta. Mikewa tayi ta fita ta kirawo Aunty, Minti biyu gabaki dayansu suka shigo tare,


Itama sai da Baba yayi magana kafin suka gaida ta hakanma murya adakile kamar wanda bakin su ke ciwo. Bata batawa kanta lokaci wajan amsawa ba dan yanayin yanda sukayi mata gaisuwa gabaki daya babu da'a a ciki. Baba ya jijjiga kai kawai yanajin babu dadi bai san yaushe al'amarin gidansa zai gyaru ba, yana fata Allah ya kawo masa mafita a wannan lamari kafin mutuwarsa idan ba haka ba zai mutu da bakin ciki da fargabar tarwatsewar ahalinsa.


Ya ɗauki lokaci a haka saida gabaki daya wajan suka fahimci abunda ya faru bai yi masa dadi ba. Anty sai taji babu dadi data san halin da zai shiga kenan data amsa gaisuwar ko a yaya suka yi ta,


Yadauki lokaci ahaka sannan yayi gyaran murya gabaki ɗayan su suka fuskance shi sai da yai nisa sannan yace,


"Hajiya Indo (Mama) Habiba (Aunty) ga Fadeela da Aysha daga yau in sha Allahu sun dawo gidannan da zama gabaki ɗaya, anan zasu ci gaba da karatunsu har Allah ya fito musu da miji suyi aure. Na baku amanar su ina so kuji ajikinku kamar ƴaƴan da kuka haifa ne duk da cewa banda shakku akanku zaku kula dasu yanda ya dace kawai tunasarwa ce nayi. Idan laifi suka yi kamar yanda kuke yiwa kanwarsu Mamee hukunci haka suma zaku yi musu." Mama tace,


"Insha Allahu ai abunda yayi Mamee shi yayi su Fadeela Allah ya bamu ikon rike amana."


"Amin" Baba ya amsa bai jira yaji maganar Aunty ba dan yasan idan Mama ta amince itama ta amince. Anty cikin ranta ji takeyi kamar tafito ta gaya masa bazata iya rike wannan amanar ba dan ga dukkan alamu yaran dan ita sukazo aransu, amma bazata iya ba saboda bata san halin da zai shiga ba har indai ta fadi hakan. Ita ta fara mikewa tace,


"Zan koma wajan Hussaini na barshi shi daya." Baba yace.


"Toh nima yanzu zan shigo na duba jikin nasa." Ya dubi Mama yace,


"Kuje ki nuna musu yanda zasu zauna idan kin nuna musu ki dawo." Amsawa tayi ta tashi tayi waje, bayan tafita Baba ya dube su yace,


"Ku dauki kayanku kuje wajan Hajiya Indo zata nuna muku daki sannan dan Allah bana

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads