Showing 81001 words to 84000 words out of 171869 words
Chapter 28 - BIBIYATA YAKE YI COMPLT Document by Zainab Bawa.txt
tausayamin take bata taba yarda ta sanar dani halinda Hamma yake ciki dan tasan Babu alfanun hakan zata dada dagamin hankaline kawai. Tunda aka soma maganar har rana mai kamar tayau Hamma bai taba kiran Aysha ba bai nemi yasanta ba sam danko kamanninta bai sanib. Gashi Maryam ta dada hura masa wuta a zuciya data sanar dashi irin Abubuwanda take yiwa Marmeeyy.
Ranar naje makaranta ban dawo ba sai yamma ina shigowa naga manya manyan motoci ima shiga nasamu Su Mummy ne suka iso. A shahshin Baba suka sauka itada wasu yayinda sauran yamn uwan suka sauka a gidn mahaifinsu dake bauchi. Nashiga na gaisheta tanata murnar ganina amma ni sai taga walwalata ba kamar yanda na sababa jikinta yayi sanyi alokacin tasaka Hakuri saida ta tambaya nakasa cewa komai banda murmushi danakeyi na karfin hali. Anty fadeelah ce tafara yimata bayani natashi nafice dasauri. Mummy tamike rai bace tayi dakin Mama tana fadin hakanma bamai faruwa bace."
ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya
Assalamu alaikum yan'uwa da abokan arziki🤝🤝🤝
Ina mata masu fama da wadannan matsalolin
Matsalar haihuwa
rikicewar al'ada
ciwon mara yayi period
Fesowar kuraje ga gaba
Ganin farin ruwa mai wari yana fito maki
Kurajan gaba
Kaikayin gaba
Da dai Sauran wasu alamomi to yar uwa kinsan ko miye to ba wani abu bane face sanyi ne ya taro yayi maki yawa 😔😔😔
Toh masha Allah sha kuruminki Allah ya kawo maki sauki ga wannan addababai ciwo
Maganin da zaki sha kiyi garau da yarda Allah 🙌👍
Toh ga dama ta samu maza ki kira aunty zee mom mujahid Katsina akan wannan lambar wayar ki ce mata MAIJIDDA MUSAWA ce taba ki wannan number
ki na son sanyan magani
08162859027🤝
------
Sallama tayi sannan ta kutsa kanta cikin dakin. Mama wacce ke daki tanajin sallamarta ta nufo palour fuskar Mummy babu annuri hakan yasa Mama taja jinin jikinta batasan abunda Mummy tazo dashi ba ko wani rikicinne kuma? Tanata saƙe-saƙe acikin zuciyarta. Jiki a saɓule tasaka murmushi akan fuskarta haɗeda faɗaɗa fara'arta tace.
"Sannu da zuwa Mummy kece da kanki dakin zauna ai kin huta idan wani abunne saina shigo" Mummy ta girgiza kai.
"A'a mamansu wannan ba maganar jira bace tafaɗa tana zama akan kujera"
"Toh Allah yasa dai lpy"
"Ba lafiya ba gaskiya ashe wannan yaron da Aysha zata aura saurayin Marmeeyy ne? Wane irin abune haka tayaya za'ayi wannan lamari ace saurayin ƙanwarta meya faru da za'a canja mata masoyi zuwa kan ƴar uwarta? Wannan bama mai yiwuwa bace dole azo a canja zuwa kan
Masoyiyarsa ta asali. Ko menene dalilin wannan sauyinma tukunna?"
"Babansu kawai yasan dalili danshi ya canja kuma bai sanarwa kowa komai ba. Amma ita Marmeeyy taceta hakura abar zancen kawai Sam bataso atada lamarin"
"A'a wannan ai bazata yiwu ba kinsan halin Marmeeyy ai saboda ke kika haifeta bazata taɓa damuwa ba har indai akan ƴan uwanta ne yanzu muje wajan Babansu idan bazaki masa magana ba kiyimin iso ni zan masa magana" Mama ta ɗaga da mamaki tana kallonta wai itane Mummy takeso tayi mata iso wajan Baba Mummy mai nuna isa da gadara wajan kowa. wane iso take bukata bayan kai tsaye ma shashinsa suka sauka itada baƙinta. Kodan tundaa ya kasance anan ɗakinta yake tun kafin tabar gidan. Saida tasake maimaitawa sannan Mama ta miƙe tayi gaba Mummy tana binta suka shiga har wajan Baba dake da mutane a ciki yabar musu Babban palournsa dayake zama yakoma palournda yake kusada main ɗakinsa. Da sallama mama ta shiga Mummy na biye da Ita. A palourn ta zauna ta jira Mama tayi masa magana suka fito tare. Mama tayi hanyar fita. Mummy tace.
"Kidawo kizauna a gabanki yakamata ayi zancen ai. Ganin Baba ya tsura mata idanuwa yasa tadawo ta zauna ba'ason ranta ba. Mummy Tajira Baba yazauna sannan tafara karanto masa ƙorafinta. Saida tagama sannan yace.
"Bantari nunfashinki ba Mummy amma akwai babban dalili dayasa akayi hakan wanda yin hakan kawai shine mafita. Banyi hakan dan banason Marmeeyy ko inason fifita Aysha ba.
Aysha da Mummy dukansu Ƴaƴanane kowacce inason farin cikinta babu wacce zan tauye acikinsu dan ƴar uwarta taji daɗi"
"Mummy kibar zancennnan kawai har indai Marmeeyy ce ta fahinci kowa da komai bata ɗauki abun da zafi fa kawai dai ranta baya mata daɗi ne kuma bata fushi da hukuncin" Mama tana gama faɗin haka ta miƙe tana tace"
"Bari naje zamu kasuwa da Aysha akwai kayan kitchen da bamu gama sayayyya ba yanzu zamu shiga mu sayo" har takai bakin ƙofa Baba yakira sunanta. Ta tsaya cakk dan Baba ya kwana biyu bai kirata dasunanta ba bata juyo ba Har saida yacigaba da Magana.
"Ko sau ɗaya bazaki tambayeni dalilin dayasa najuya auren Marmeeyy kan Aysha ba? Da zaki tambayeni da zan zauna nayi miki bayanin komai tun daga farko yanda zaki fahinci lamarin. Baba (Alhaji Habibu) shine ya hanani faɗa miki komai amma har indai zakici gaba da shareni banaji zan iya bin umarninsa zan zauna nayi miki bayani ki fahimta anyi abunne batareda son zuciya ba" sai alokacin ta juyo tayi murmushi.
"Tunda Har Baba ya hana ka gayamin toh sanina baida amfani dan yasan dalilin dayasa yace kada ka gayamin ina bayan hukuncinsa. Sannan niba shareka nakeyi ba kawai yanayin da Marmeeyy ke shiga ke jefani wani yanayi da banajin daɗinsa amma da zarar angama biki nasan komai zai dawo dai-dai" Bata sake magana ba tafice Baba ya sauke ajiyar zuciya yabita da kallo yanajin babu daɗi acikin ransa."
Dake wannan semetern bawani tsayi zatayi ba har munci rabi abubuwa sun fara zafi exam baifi saura 1month ba hakan yasa sam bana zama agidan kuma naji daɗin hakan dan nasamu damar kaucewa abunda banason gani.
ƴan uwan Mummy suka haɗa event Mummy bataso hakaba dan itama auren ya fice mata arai. Mamakin yanda Aysha take rawar kai takeyi tana ganin wautarta zata auri mijinda baya sonta take wannan abun wanda takasa gane dalili yin hakan son saurayin dama takeyi ko tanayine danta ƙuntatawa ƴar uwarta kamar yanda fadeelah tafaɗa mata.
Nadawo daga makaranta nawuce ɗakinmu kai tsaya dukda yanzu bancika zama a ciki sosai ba nafi zama ɗakin Mama dan banason zama waje ɗaya da Aysha. Ɗakin nasamu acike da ƴan mata ƴan uwansu Aysha waɗannan masu masifar jida kansu. Ina ganinsu najuya dasauri zanbar ɗakin dan danasan suna ciki bazan shigaba bansan da isowarsu ba.
"Ina kuma zakije? dawo nan ko kiyi abunda zakiyi ki sake fa Marmeeyy baza'a hanaki sakewa awani gida azo gidan mahaifinki a hanaki ba" Cewar Anty fadeela.
"Bansan da mutane aɗakin bane zanje ɗakin Mama na faɗa ina ƙoƙarin fita" no babu yanda zakije zoki canja kayanki anan. Banason musu da ita dan haka na ƙarasa shigowa. Nafara cire kayan dake da Vest aciki.
"Baku mata jaje ba" cewar Aysha. Dariya su duka suka saka sannan wasu daga ciki suka fara faɗin.
"Allah sarki Allah yamaida alkhairi" ban kulasu ba. Ina jiyo ɗaya acikinsu tana faɗin.
"Aysha bakida Dama haka kikayi wuff da Bawan Allahn nan yanzu wasa gaske saura kwanaki yazama naki ke kaɗai kuma fa yahaɗu wallh ki ganshi fa lallai kinyi gamda katar. Mamaki nakeyi a'ina Aysha tasamu photonsa? Banason jin wani abun dan haka dasauri na ƙarasa cire kayan zan fice.
"Bakiji ba" Aysha tafaɗa ban kulata ba. Kinga please ki sakamin No Hamma anan sorry to ask inba wajanki ba bansan yanda zan samu ba ba cin fuska bane yanayi ne" taƙarasa tana miƙamin wayarta.
"Anya aysha kinada hankali kuwa? Nikam lamarinki na bani mamaki. Wallh Marmeeyy karki kuskura kibata taje yanda zata nema tasamu ƴar iska" ko kallo anty fadeela da tayi magana bata isheta ba.
ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya
Assalamu alaikum yan'uwa da abokan arziki🤝🤝🤝
Ina mata masu fama da wadannan matsalolin
Matsalar haihuwa
rikicewar al'ada
ciwon mara yayi period
Fesowar kuraje ga gaba
Ganin farin ruwa mai wari yana fito maki
Kurajan gaba
Kaikayin gaba
Da dai Sauran wasu alamomi to yar uwa kinsan ko miye to ba wani abu bane face sanyi ne ya taro yayi maki yawa 😔😔😔
Toh masha Allah sha kuruminki Allah ya kawo maki sauki ga wannan addababai ciwo
Maganin da zaki sha kiyi garau da yarda Allah 🙌👍
Toh ga dama ta samu maza ki kira aunty zee mom mujahid Katsina akan wannan lambar wayar ki ce mata MAIJIDDA MUSAWA ce taba ki wannan number
ki na son sanyan magani
08162859027🤝
------
Bansan lokacin da murmushi ya suɓucemin ba wanda ni kaina bansan na menene ba amma tunanina yafi bani na jin daɗine tunda na fahimci ko lambarsa ma bata dashi hakan yana nufin ko kiranta bai taɓa yiba kenan. Sai Alokacin naji inada buƙatar na maida mata amsa tunda nasamu damar yin hakan.
"Anya Aysha kinada hankali kuwa? Zumuɗin auren mutuminda baisan dakeba ko kamanninki bana tunanin ya sani bare ace ya kiraki a waya haka zakiyi zaman aure shine kiketa ɗauki. Wane irin zama kike tunanin zakiyi da namijinda zuciyarsa ta karkata wani waje? Ki zauna kiyi tunani sosai ba Zumuɗi da rawar kai yakamata kiyi ba yakamata ki zauna kiyita addu'a kina roƙon Allah yacire masa son wacce yake fama da ita a zuciyarsa ya sanya masa ƙaunarki. Wannan shawarace a matsayina na ƴar uwarki" Cikin ƙuluwa tace.
"Duk namijinda zai soki Marmeeyy ina tunanin idan ya ganni zai soni fiye da ke dan saiya ninkamin sonda yake miki ai ido ba mudu bane amma yasan kima"
"Okay all the best" shine abubda nafaɗa nabar ɗakin. bayan shigata ɗakin Mama na zauna a gado haɗeda sauƙe ajiyar zuciya Naji sanyi da daɗi sosai a raina banyi tunanin zan samu sauƙi alokaci ɗaya hakaba. Gabana yayi mummunan faɗuwa. Danayi tunanin abunda ya sakani jin daɗin. Anya kuwa nayiwa kaina adalci? Murna nakeyi da rashin kiran da Hamma ke yiwa Aysha? Hakan yana nufin naji daɗin nuna halin kk inkula da yayi da ƴar uwata kenan?" na jijjiga kai da sauri dan banason ya kasance haka. Na tabbata samun damar mayar mata da martanin maganar da take jefamin yasamamin nutsuwa naja dogon numfashi na zube akan gado.
Washe gari zasuyi event ɗinsu dan haka tunda na tafi makaranta ban dawo ba sai har 6:00pm ina cikin makaranta harda maryam itama taƙi komawa gida. Babu yanda banyi da itaba tatafi wajan event ɗin taki. Dana matsa tacemin.
" ke idan naje hakan yana nuni ina farin ciki da bikin kenan? Toh banayi garama ki barni" haka nagaji nabarta ban bar makaranta ba saida na tabbatar kowa yagama tafiya wajan event ina shiga gida ana kiran magrib Kia tsaye ɗakin Mama na wuce ban fito ba sai washe gari ko kalan kayanda Amarya da ƙawayenta suka saka bandaniba. Bansan ango yaje ko baijeba. Mummy ma ban gantaba sai da zan tafi makaranta nabi muka gaisa. Zan fito inaji wasu suna zancen ango baijeba na taɓe baki nawuce abuna. Yau ma irinta jiya nayi sai magrib nadawo. Dake a harabar gida suke event ɗin na taras dasu amma ko kallon yanda suke banyiba nawuce ciki. Anty fadeelah ma ashe bata halarci event ɗin ko guda ɗaya ba bansaniba saida nashiga na tarasda Mama tanayi Mata faɗa nima na saka baki muna tausarta amma cewa take har indai bazan jeba toh itama bazata jeba. Na nuna mata saboda school yasa bansamu event ba takasa fahimta dan haka kawai na yanke shawarar zanje event har indai za'ayi a ƙarshe. Tausayin Aysha ya kamani ganin yanda ake event ba ango bare ƴan uwansa. A paper na rubuta numbern Hamma nakai mata ɗakinda take na ajiye. Tagani batace komai ba nima bance ba dan banama buƙatar tace ɗin bana tunanin yanzu zan iya bari ta faɗamin maganarda ranta yakeso batareda na rama ba.
Ina fita taɗauki numbern dake babu kowa a ɗakin tayi dialing numbern bata daɗe tana ringing ba aka ɗauka ta gaisheeshi ya amsa murya babu yabo ba fallasa. Yayi shiru dan bai gane wacece ba. Tafara in ina.
"Uhmm Uhmm Aysha ce" har cikin ransa tsakani da Allah bai gane wace Aysha dan haka yace.
"Aysha! Aysha! Banganeba. Tarasa me zatace masa yagane sai tace.
"Uhmm dama marmeeyy ce ta bani lambarka shine nace barina kira naji ko zaka halarci diner da za'ayi on Saturday ranar ɗaurin aure. Idan bazaka samu damar zuwa ba sai kawai asoke event ɗin"
"Marmeeyy tabaki Number na? Yayi exclaiming. Da sauri tace.
"eh" a yanda yake zaune yazama statue yakasa koda motsi bayan yayi confirming abunda kunnuwansa sukaji masa. Menene hakan yake nufi kenan? Marmeeyy ce da kanta tabata Numbernsa? Marmeeyy ta yafeshi ta manta dashi ta daina sonsa
kenan? Haka actions nata suka gwada amma baiyi tunanin zata iya daukan numbernsa tabada sisternta ba bayan tasan ita kaɗai yakeso. Yaji ɗaci aransa dakƴar ya iya buɗe bakinsa yace zan kiraki. Yana faɗin haka ya datse kiran."
Lallai marmeeyy tawuce iyakarta kuma tasaka shi yaji zafi yaji babu daɗi. Amma dole zai rama zaije event ɗinda za'ayi kodan shima yasamu ya ƙuntata mata gwargwadon yanda tayi masa. Kai amma anya zuciyarsa zata iya jurar ganin ya ƙuntatawa Marmeeyy kuwa domin yana sonta idanya ƙuntata mata ya tabbata saiya fita shiga damuwa.
Nikuma anawa wajan ba ƙaramin dauriya nayiba dana iya ɗaukan number na bata dan saida nayi hawaye amma yaya zanyi? Tunda inada hanyarda zan taimaka mata kawai gwara na taimaka matan dam bazan barmu dukanmu cikin ƙunci ba."
Har washe gari bai kirata ya sanarda ita akan zai halarci event ɗinba shi asaninsa grooms ke shirya diner idan suna buƙata baisan wane karbani yakaita shirya diner bayan bata shawarceshi ba.
Dakyar wasu daga cikin abokanansa da sukasan yanda lamarin yake suka tausheshi akan yaje. Daya tsaida zuciyarsa akan zuwan kawai saiya tura mata text message akan zai halarta. Amma shi dai har yanzu Marmeeyy yakeso kuma yana addu'a akan Allah yayi ikonsa ya canja lamarin.
Aranar akayi walima itama ban halarta ba ina makaranta har aka tashi.
Washe gari daya kasance ɗaurin aure da zazzaɓi na tashi dan abun ya dokenk sosai gani nakeyi kamar almara wai Hammana zai auri ƴar uwata. Aysha inajin kamar zan iya haƙuri bayan auren amma sakda ranar tazo naji haƙurina gabaki ɗaya ya ƙare. Toilet nashiga nayi kuka na godewa Allah nafito ban fitoba dan nasan idanna fito kowa saiya fahimci halinda nake ciki.
Dagani har Hamma munkasa yarda cewa yau rana tazo da zata saka katanga a tsakaninmu zamu zama ba mallakin juna ba ina tuna hakan sai inji hawaye yana zirara akumatuna.
ƙarfe sha ɗaya da rabi 11:30am aka ɗaura auren Hamma da Aysha Bikin yayi mutane dukda bawani gayyata akayi ba shi Hamma abokanansa idanba na jiki bama bai sanar musu ba. Amma haka abokanan wannan ya sanarwa wannan har suka samu halarta. Hamma kawai yana tafiya ne amma jiri ɗebansa yakeyi ɗakyar yasamu ya sulale yabar cikin mutane dan jiri ɗebansa yakeyi akowani lokaci zai iya faɗuwa."
ZAYNAB BAWA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya
Assalamu alaikum yan'uwa da abokan arziki🤝🤝🤝
Ina mata masu fama da wadannan matsalolin
Matsalar haihuwa
rikicewar al'ada
ciwon mara yayi period
Fesowar kuraje ga gaba
Ganin farin ruwa mai wari yana fito maki
Kurajan gaba
Kaikayin gaba
Da dai Sauran wasu alamomi to yar uwa kinsan ko miye to ba wani abu bane face sanyi ne ya taro yayi maki yawa 😔😔😔
Toh masha Allah sha kuruminki Allah ya kawo maki sauki ga wannan addababai ciwo
Maganin da zaki sha kiyi garau da yarda Allah 🙌👍
Toh ga dama ta samu maza ki kira aunty zee mom mujahid Katsina akan wannan lambar wayar ki ce mata MAIJIDDA MUSAWA ce taba ki wannan number
ki na son sanyan magani
08162859027🤝
------
Tun da aka ɗauki azumi akayi sallah gabaki ɗaya hankalinsa ya karkarata yayi wajanta babu wani abu dayake muradi da burin gani daya wuceta. Yana mararin sanyata a idanuwansa yayi kewarta samada yanda baki zai iya faɗa. Ga abubuwa sunyi masa yawa kuma a wannan lokacin yana tunanin dole ya bayyana mata kansa a yayinda zaije gareta yagaji da ɓoye kansa wannan karon yana buƙatar shima tasanda zamansa matsayinsa na mijintabamma yaya zaiyi da alƙawarin da ya ɗaukawa Baba? Yazama dole yacigaba da ɓoye kansa har lokacin da Baba zai bashi izinin bayyana mata kansa. Wannan dalili ya tsareshi daga zuwa ganinta ya taushi kansa yabawa zuciyarsa haƙuri amma yaga zuciyarsa a wannan karon tana neman fin ƙarfinsa kodan ba wannan karon bane ta saba yimasa haka. Alokacinda ya fara sanin Marmeeeyy yaso ya danneta amma ta gwada masa bazata dannuba saboda taga abunda takeso haka taci galaba akansa ya biye mata wannan karonma hakan takeso tayi masa. Ziciyarsa ta azabtu da son ganinta ko jin muryarta. Ɗaya daga cikin wayarsa ya ɗauko. Yanata tunani yayi ko kar yayi bazai iya hana kansa ba A wannan lokacin abisa tilastawan da ziciyarsa tayi masa yayi dialing numbern marmeeyy.
Ina zaune abun duniya ya taru yayimin zafi narasa yanda zan saka kaina tunda naji labarin an ɗaura auren nakejin jiri-jiri harda zazzaɓi dan zuciyata sai tashi takeyi nakasa cin komai. Tun banaso kowa yagane har Mama tazo ga sameni a cikin wannan yanayin tashiga tashin hankali matuƙa zama tayi tanamin nasiha da kalamai masu ƙwantarda hankali da sanyaya zuciya.
"Marmeeyy kina jina? Ki ƙwantarda hankalinki kisan cewa kowani irin lamari rubutacce ne wajan ubangiji dama can Allah ya rubuta Hamman ba mijinki bane. Kuma bamu isa muja da hukuncin Allah ba. Alkhairi kawai muka roƙa a wajansa kuma inada yaƙinin alkhairin zai bamu. Karkiji komai karki riƙe komai a zuciyarki ki tashi ki fita cikin ƴan uwanki ko zakiji sanyi. Idanma bazaki iya hakanba ki zauna anan ki ɗauki ƙur'ani ki kiranta zakiji sanyi. Tayi tamun nasiha sosai ina jinta har tagama kuma Alhamdulillhi nasamu sauƙi. Na lumshe idona kamar mai bacci ganin haka yasa tafita. Ina zaune ƙwance wayata tafara ruri a hankali na jawota. Ina ganin lambar saida gabana yafaɗi amma na dake. Baitaɓa kirana ba tsawon