Header Ads
Showing 54001 words to 57000 words out of 171869 words

Chapter 19 - BIBIYATA YAKE YI COMPLT Document by Zainab Bawa.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jun 2024

1075

Ads at the middle of Article

faɗin.


"Meyasa kika saka turare? Daga yau karki sake sakawa idan zaki fita dan Allah baby na roƙeki yafaɗa cikin mawuyacin hali dasauri na jijjiga masa kai a tsorace nace.


"Hamma menene kakeyi hakan? Kabarni natafi Maryam na jirana"


"Okay you can go but after kincemin kina sona" Ganin yanayinda yake ciki yasa na yanke shawarar fa Faɗan dan kawai yabarni natafi. Na buɗe bakina da niyyar faɗa han ankara ba naji ya haɗe bakinmu waje ɗaya yafara tsotsansu a matuƙar tsorace na fara ƙoƙarin tureshi dan son ƙwatar kaina amma nakasa ya ɗauki lokaci narasa ta wace hanya zanbi na ƙwaci kaina saida shida kansa kamar wanda aka zabureshi ya sakeni haɗeda yin baya. Yana sakeni na zube a wajan nasaka kuka sosai. Lips ɗina wani irin raɗaɗi da zafi sukeyi amma zafinda zuciyata takemin yasa banajin zafin lips ɗin. Shikuma yayi baya ya zauna ya dafe kansa baisan dalilin dayasa ya aikata hakan ba. Saida kukan nawa ya tsagaida na tashi dasauri namiƙe nafice a ɗakin. Ko takan maryam banbi ba Allah dai kawai yasa tafito harabar gidan tana waya taga fitowata dasauri hankali tashe ta kashe wayar ta yi kaina ban kulata ba saida nafice daga gidan. Taja trolley tabiyo bayana tana tambayata abunda yafaru ban kulataba nacigaba da tafiya a titin napep na zuwa ta tsara suka yiyo wajena babu yanda batayiba na shiga naƙi har saida ya sauƙo taturani ciki. Juyin duniya tayi dani nafaɗa mata abinda yafaru naƙi Tayitamin tambayoyi amma naƙi bata amsa ita taɗauka faɗa mukayi ma. Ganin mun kusa isowa yasa tace.


"Babe koma menene yafaru ki share hawayenki dan munkusa isowa gida idan baso kike ki tadawa su Mama hankaliba, koma menene yafaru a tsakaninku zakuyi sorting komai tunda bakyaso ki faɗamin nasan bazaki faɗawa kowa ba so ki share hawayenki dan idan anganki haka za'a tuhumeki idan bawai so kike kiyiwa aurenku tun kafin lokacinsa giɓi ba" na share hawayen fuskata amma har lokacin bance komaiba, mai keke napep yakaimu har ƙofar gida ya ajiyemu. Aharabar gidan muka ga motar Yaa Ahmad da alamun yazo kenan. Muka shige ciki su Mama suna zaune cikin gida banyi sallama ba saboda nasan dole muryata ta canja maryam ce tayi sallama suka amsa muka shige ina zuwa na nufi ɗaki. Mama najiyo tana faɗin.


" Marmeeyy zo nan" gabana yahau faɗuwa zuciyata na bugun uku-uku."




ZAYNAB ALABURA


Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.





Dan tun jishowata gidan nake tsarge gani nakeyi kamar kowa ya fahimci abunda yafaru tsakanina da Hamma. Kiranda Mama tayimin ya tsurardani sosai ina tunanin tagama ganewa shikenan nashiga uku nafaɗa acikin zuciyata. Nayi kamar banjiba ba nacigaba da tafiya. Tace.


"Marmeeyy zonan nace. Kamar zan saki fitsari a jikina. Najuyo naƙarasa wajan batareda nayi magana ba naja natsaya jikina sai rawa yake a hankali. Mama tace


"Ɗauki wannan kikai ɗaki ta faɗa haɗeda nunamin wasu turamen zannuwa guda huɗu dasuke gefenta na isa waja har alokacin gabana faɗuwa yakeyi na ɗebesu"


"Wannan turare mai ƙarfinfa marmeeyy?" a'ina kima samoshi?" Mama ta tambaya. Rass rass rass naji narasa abunda zance dannasan turarem Hamma ne daya mannu ajikina yakama jikin. Maryam tayi saurin faɗin.


"A ɗakina ta fesa saida nace mata yayi ƙarfi shiyasa nima na ajiye shi bana amfani dashi" mama tace.


"Yayi ƙarfi kam amma kuma yanada daɗi na maza ne" Nayi saurin na ɗebi kayan nabar wajan. Maryam kuwa ta faɗi hakanne dan ta fahimci turaren Hamma ne tun a napep taji ƙamshinsa amma ganin halinda nake ciki yasa hankalinta bai kawo mata wani abunba sai yanzu dataji Mama tayi tambaya sannan ta fahimci wani abin yasa tayi saurin shiga ta kareta.


A ɗakin Mamana zuba kayan nakoma ɗakinmu na zauna nayi tagumi abun duniya yataru yayimin yawa kawai sai naji hawaye sunabin kumatuna.
Meyasa Hamma zaiyimin haka?" Mai yasa zaiso shiga gonarda bata riga tazama mallakinsa ba? Meyasa zai lulluɓe soyayyarda nakeyi masa da haushinsa? Tabbas yau Hamma ya bani haushi kuma ya ɓata mun rai dan ban taɓa tsammanin haka daga gareshi ba. Toko dama Hamma basona yakeyi bane?" idan yana sonta bazai taɓa aikata mun wannan abunba. Nafaɗa tunani mai zurfi zuciyata ganata kawomin abubuwa kala-kala kawai saina fashe da kuka. Ana haka maryam tashigo ganin ina kuka ta nemi waje ta zauna cikeda tausayina jikinta yamutu takasa rarrashina. Nayi kuka yakai na tsawon 30minute Har yadawo shassheƙa. Sai asannan maryam ta tattaro ƙwarin guiwarta tace.


"Babe please. Dan Allah kiyi haƙuri haba mana. Tundaga kallon yanayinda kika shiga nasan Hamma ya ɓata miki sosai amma yaya zakiyi? Zaki kashe kanki akan namijine? Bayan shi yanacan zaune may be ma harya manta da abunda yafaru. Koma me yafaru nasan Hamma nasonki sosai tnda mece first-love nasa kamar yanda yake a wajanki everything wil be alright okay' just take it easy. Hamma nasonki sosai koma meya faru may be saiya fiki dana sani banajin zai yarda ya saɓa miki dason ransa"


"Na ɗago idanuwana wanda harsun canja kala sunkuma dawowa fararensu nace dagaske kike yana sona?" amma yanzu kika gama cewa may be ma yanacan yama manta da abunda yafaru"


"Uhum yana sonki sosai wancan na faɗane kawai"


"Bakya kallon wani abun bayan soyayya a idonsa" ta jijjiga kai tace.


"absolutely nothing babe" nasauke ajiyar zuciya. Nazuba tagumi ta zauna kawai tana kallona" sai bayan nasamu sauƙin abunda nakeji sannan nashige toilet nayi wanka nafito. Duk yanda naso mu haɗuda Yaya Ahmad bansamu wannan damar ba dan ko palour bansake leƙawa ba har dare yayi. Maimakon nayi karatu dai kuma na lula tunani. Gashi ko message Hamma baiyi minba abunda ya sake ɓatamin rai kenan bare ajega kira ya kirabi yabani haƙuri. Na buɗe littafin amma bana gane komai aciki daga baya kanma zazzaɓine ya rufeni. Haka na ƙwana a daren zazzaɓin bai sakeni ba sai asubahi bayan ya sakeni kuma sai bacci haka na daure nayi sallar asubahi gashi da sassafe mukeda exam bansamu na goma bacci ba haka na tsaya na dudduba littafi ga rashin bacci ga rashin ƙarfin jiki dakuma raunananniyar zuciya"


6 da wasu abubuwan nayi wanka kafin nagama shiri 7 yayi nafito nayi ɗakin Mama maryam itama ta shirya na gaisheda Mama. Ta kalleni jin muryata sai taga fuskata ta kumbura.


"Marmeeyy badai karatun kika kwana kinayi ba idonki yayi haka?" nayi yaƙe kawai tace.


"Aikuwa dai da kinyi baccinki kinga yanda fuskarki ta kumbura? Ana kallonki ansan baki samu bacci ba ana ƙare exam ɗinnan kidawo ki ƙwanfa" toh nace sannan canja zancen da faɗin.


"Babe muje Maryam tataso cikeda tausayinta dan ita tasan abunda yafaru muka yiwa Mama sallama muka fita" kamar yanda nayi tsammani babu motar Hamma a ƙofar gida. Maryam ma tasha mamaki muka wuce muka tafi abunmu"


Kusan nice ƙarshen fita a hall ɗin exam ɗinnan dan abubuwanda nasani basuda yawa bana tunanin sun isheni naci jarabawarnan gashi wani irin bacci nakeji ina zaune har saida lokacin fita yacika likacin 11:00am ina fita nawuce yanda nasan zan samu Maryam. Tana kallona tamiƙe kawai ta isoni muka kama hanyar fita.


"Babe ya exam ɗin dai ta tambaya dan tasan anfafata saboda yanda taganni wujiga-wujiga"


"Hmm kibari kawai sai dai mu nemi taimakon Allah"


"Jiya baki samu bacci ba babe ga dukkann alamu karatunma bakiyishi ba. Babe you have to be strong fa Hmmm tun ba'aje ko'ina ba kina irin haka? Idan iyayenmu suka faɗa miki baƙin cikin maza da suke shanyewa su zauna kamar komai bai faruba zakisha mamaki. Bayin Allahan nan sun shanye abubuwa dayawa sai dai Allah yasaka musu da alkhairi"



Inajinta kawai amma ban tankata ba har muka shiga fita gate muka tsari napep takaimu har gida. Ɗakinmu nawuce ina shiga na canja kayana na ƙwanta sai alokacin nasamu bacci har azahar ban tashiba ina tashi nayi wanka saboda yanyin zafi da ake agarin na shirya nafita palour anan nasamesu duka da zannuwan dana ɗebo jiya nashigo dashi. A gefn Mama. Ina fita palour Mama tace.


"kinga da kika ɗan samu hutun fuskarki harta ɗan saɓe" na zauna muka fara hira sai alokacin nasamu sauƙin abunda nakeji akayita raha sannan Mama ta miƙo mana atamphopin dasuke gefenta kowa ɗaɗɗaya nida Maryam Anty fadeelah da Aysha. Sannan tafara bayani.


"Yayanku yazo dasu Jiya guda shida ankon bikinsane amma bana tunanin zaku samu ɗinki ana yanzu idan kuka bayar sai dai ko can abujan" nace.


"Ni tareda Ya Ahmad zamu tafi dannasan bazai wuce ƙwana biyu ba zai koma"


"Har indai muka kaiwa tailor na zamu samu kafin mutafi cewa maryam" mama tace.


"toh saiku shirya kukai masa" Anty fadeelah da Aysha sy bazasu kaiba dan sunce bazasu jeba. nashiga ɗaki dan ɗaukan mayafina idona yakai kan wayoyina da suke haske suna sanar dani inada missed called ko ajiyayyen saƙo."




ZAYNAB ALABURA




Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.






Na ɗauki wayar gabana yana faɗuwa wayarda Hamma ke kirana da ita nafara ɗauka. saƙonsa ne kamar yanda nayi zato saƙo ne yana mai bani haƙuri haɗeda nuna yayi bai dai-dai ba ya sanar dani cewa kunyar abunda ya aikatamin ya hanashi nemana kuma yahanashi zuwa wajena. Ban amsa saƙon ba na rufeta na ajiye na ɗauki ɗayar wayan saƙon wancan mutumin ne ita Kuma yanamum murna da kammala jarabawata. Na taɓe baki sannan na zuba wayoyin acikin jakata. na ɗauki veil ɗina na fito. Nasamu Maryam harta shirya kai tsaye muka kai ɗinkin muka dawo batareda ɓata lokaci ba dan banason zama ma a wajan. Ya shaida mana nan da 2days zamu samu dan haka mun bashi kuɗin ɗinkin kawai munjuyo. Idan yagama zamuje mu ƙarɓa kokuma yakawo mana har gida.


Mun samu Ya Ahmad a wajan Mama. Mama tana kallonmu tace.


"Har kunkai kenan?" muka amsa mata da.


"eh" tace aikuwa kunyi sauri dama yanzu Yayanku ke tambayar wajanki" saida na zauna sannan nace.


"Ina wuni Yaya" lafiya Marmeeyy yafaɗa alokacinda yake ɗago idanuwansa ya dibeni Maryam ma tace ina wuni ya amsa mata yana kallona sai naga kuma ya haɗe rai yace.


"marmeyy wannan ƙaramin gyalen fa? Ahaka kika fita?" na dubi veil ɗin jikina na turo baki nace Ya Ahmad me yayi?" Mama tayimin danƙwalo tace.



"ƙaniyarki yayi marmeeyy" Maryam tana jin haka tayi wuff tashige ɗaki. Ya Ahmad yacigaba da faɗin.


"Mama kar abatta tasake fita ahaka Baba yasan kinfita? Da izininsa kika fita zan gaya masa ya hanaki bazaki sake fitaba" mama tace.


"Toh shikenan in sha Allahu bazata sake fita ba. Kayi haƙuri" Nace.


"Yaya ni bazanma sake fita ba sai ranar da zamu tafi"

"Thou yayi jibi zamu tafi kushirya dawuri fitar sassafe zamuyi inaso kusamu event da za'ayi" Harna fara murna saina tuno ɗinkinmu nace.


"yaya akwai ɗinkinmu wajan tela fa kuma yace zai kai jibin"


"Kubani lambarsa idanna fita zan kirashi na ƙara masa kuɗi yayi zuwa goben"


"Yaya amma fa da Maryam zamu tafi"


"agidansu za'a barta ne" ya tambaya.


"Ai yanzu anan gidan takeda zama Umminta da abbanta sunyi tafiya kaga idanna tafi nabarta bazataji daɗin zama ba"


"Toh " kawai ya amsa dashi sannan ya miƙe yace.


"Itama sai akarɓa mata ashoben koh?" Mama tace.


"Nabata nawa ma shine yanzu suka kai ɗinkinsa"


"thou Bari naje Baba yana jirana" yafaɗa haɗeda ficewa.
A palour yasamu Baba amma kamar fitowarsa kenan danko zama baiyiba. Yashiga da Sallama Baba ya amsa a lokacinda yake ƙarasa zaunawa. Bayan sun gaisa Baba yace.


"Kunyi magana da Mummynku akan zamanka anan?" saida ya sunkuyarda kai sannan yace.


"Bamuyi magana da itaba amma munyi magana da yarinyar da iyayenta kuma sun amince sun nuna jin daɗinsu akan hakan. Mummy ko bayan biki zan gaya mata tunda dama ba daga biki bane za'a kawota ba sai bayan wani ɗan lokaci"


"okay toh amma kasamu gidan kuwa?"


"Eh shine yanxu nazo na ɗaukeka muje mu gani idan yayi sai ayi maganarsa"


"Toh ma sha Allah hakan yayi sai muje kawai koh?"
Miƙewa Baba yayi yafara tafiya sannan Ya Ahmad ya bishi a baya suna zuwa jikin mota ya buɗewa Baba ƙofar motan yashiga yarufe sannan yaje ya buɗe gate sannan yadawo yazagaya shima yashiga ta mazaunin driver. Saida yafita agidan sannan yafita yarufe gate ɗin yakoma yaja suka tafi saida sukayi nisa sannan yadubi Baba yace.


"Baba mai yasa ake barin Marmeeyy tana fita anyhow? Kasanfa bai kamata kabarta taringa fitaba idan bawai school ba duba da abunda yafaru. yazama dole asanya ido akanta sosai kar azo ana danasane kar a cutarda ita" baba ya yi ƴar gyaran murya sannan yace.


"Hakane yanzu bari suje bikinka su dawo tukunna sai muga abunda za'ayi" Sunje sunga gida yayi kyau sosai dama saida suka biya suka ɗau dillalin gidaje daganan suke wuce wajan mai gidan a lokacin akayi magana aka kafa shaida aka siya tunda dama ba yanzu aka fara maganar ba tun wancan zuwan Hamma aka fara maganar. Bayan sun dawo yanemi mai ɗinkinmu ya ƙara masa kuɗi sanann sukayi yarjejeniya akan gobe zamu samu.




Murna da ɗaukin tafiyarda zanyi ta cikamin cikina ya kawar minda baƙin cikin danake ciki. Aranar kusam saƙo 5 Hamma yayimin ko guda ɗaya banyi masa reply ba banmasan me zance masaba ayayinda zanyi reply ɗin dan haka kawai na sharesu. Amma zuciyata ta rigada ta sauƙo tayi rauni ayanda naga yanata bani haƙuri yana faɗin wallh bada niyya yayi bai baitaɓa tunanin aikata hakan agareni ba. Shi tunda yake a rayuwarsa ma bai taɓa attempting ɗin gwada hakan bama. Ko jiyanma akasi kawai aka samu baiyi niyyar hakanba. Ƙamshin turarenda yake jikina ya tada masa hankali daya kasa jurewa amma dukda hakanma yasan hakan bawai Hujja bace da zaisa ya aikatamin haka ba kuma bawai yana faɗan hakan bane dan kare kansa ba sai dan ya samawa zuciyata nutsuwa. Na tabbata da Yayi nadamar abunda ya aikata domin kuwa kalmansa sun nuna hakan. Ni yanzu har tausayi ma yake bani. Har dare nasamu messages ɗinsa sosai har washe gari na tashi na tarasda message ɗinsa.


Washe gari muka fara shirye-shirye nikam harna haɗe kayana waje ɗaya.


Maryam ma ta haɗe nata su Aysha da anty fadeelah kam dagaske suke bazasu je ɗinba dan babu alamun hakan.


Da Yamma tela yakira Ya Ahmad yace yagama ɗinkin. Ya kawo masa har gida muna zaune ya Ahmad yasghigo dashi yabamu" yadubi anty fadeela yace.


"Ke fadeelah angama muku nakune"


"mu wai? Ai bamu kai ɗinkin ba" tabashi amsa.



"me zakuyi amfani dashi kenan" ya tambaya. Caraf na amshe nace.


"Ai sunce bazasu jeba" da mamaki yace.


"Bikinnawa ne bazaku jeba?" taɓata rai sosai tace.


"Kafa san halin Mummy bazata bari mudawo ba har indai mukaje" tsaki kawai yaja yabar ɗakin yayi wajan Baba. Bayan Baba yafito sallar magrib yatsaya wajan Mama yace takira masa yaran. Muna ciki mama tashigo wai muzo inji Baba. Muka fice dukanmu yacewa su Aysha.


"Yayanku yacemin wai bazaku je bikinsa ba?" Aysha tace.


"Baba gara kar muje kasan halin mmmy bazata bari mudawo ba" Baba yace.


"Kuje babu abunda zai faru zaku dawo rana ɗayama zaku dawo dasu Marmeeyy bazan bari ku ƙara ko ƙwana ɗaya agarinba" da haka suka amince zasuje amma har lokaci zuciyarsu tana musu ɗar-ɗar kafin yafita yace nahaɗa masa shayi kafin yadawo.


ZAYNAB ALABURA


Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.



Kafin yadawo na haɗa masa shayinsa Na rage wuta yana heating a hankali na zauna Ina jiran dawowarsa muna zaune naji shigowarsa na juye a mug nakai masa. Da casbi na sameshi a hannu yana jaa nashiga nayi masa sannu na jawo glass table dake gefen kujera har gabansa na zuba masa shayin a ƴan ƙananun kofi na ajiye gefe yaɗan huce saina zauna akan carfet yana yimin sannu nayi murmushi. Yace.


"Gobe zaku tafi koh?"


"Eh" nabashi amsa.

"akula sosai kinji koh" sannan ga wannan ya ciro bandir ƴan 200 20k kenan ya bani yace.


"Idan zakiyi amfani dashi" dasauri na girgiza kai nace.


"A'a Baba kabarshi kawai babu abunda zamu buƙata koma mun buƙata Yaa Ahmad zai bamu" Ya ajiye Kuɗin agefena yace.


"Wannan kuma ni Babanku nabaku kuyi amfani dashi" nayi ƙasa da kaina nakasa jurewa nace Baba ina kasamu kuɗi?" dannasan Baba baida kuɗi wata rana 2k ma dayaya yake samunta? Haka kawai zaiyimin kyautar 20k bayan nasan ba lallai idan shi yanada hakan a ajiye ba. A kullum shi yanaso ya takura kansa wajan faranta mana. Saida yayi murmushi sannan yace.




"Yakamata Baba yazo yakama sana'a tunda gashi ƴarsama tasan bayayi tana tambayarsa yanda yasamu kuɗi" na girgiza kaina nace.


"bahaka nake nufi ba Baba banaso ka tukura kanka ne kasan komai mukeso za'ayi mana acan"


"Yayanki Ahmad yabani dubu ɗari biyu aciki nabaku ni ban takura kaina ba kuma duk wani abinda zanyi muku ba takura kai bane" na jijjiga kai na amsho kuɗin ina godiya. nace.


"Baba kai sai yaushe zakazo? Yayi shiru Sannan yace.


"Yakamata naje ne?" na jijjiga masa kai sannan nace.


"Sosai ma Baba idan bakajeba Ya Ahmad bazaiji daɗiba koda ba zai iya fitowa ya nuna maka ba. Idan kuma kaje zaiji daɗinda bazai kasa nuna maka ba" Shiru yayi baice komai ba Nakai kusan 9 aɗakinsa har Anty tashigo dake itace a ɗakin ina ganinta namiƙe nayi musu Sallama na fita.


Ɗakin mama nawuce kai tsaye nasake fitowa duk wasu Abubuwanda nasan zan buƙata mama tasake shiryaminsu saida tayimin faɗa itama. sosai akan tafiyarda zamuyi. Nakai wajan 10:00pm wajanta kafin natashi natafi.


dana shiga ɗaki naga missed call na Hamma banbi takaiba dan kona kira bansan abunda zance masa ba. Mun ƙwanta Da wuri saboda tashin wuri.


Washe gari tunda mukayi sallar asubahi bamu koma bacci ba. da sassafe muka shirya tafiya har Baba ya rakomu har mota da Mama anty kam bata fitoba dan ita wajanda Ya

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads