Showing 123001 words to 126000 words out of 171869 words
Chapter 42 - BIBIYATA YAKE YI COMPLT Document by Zainab Bawa.txt
bazai iya badani ni kaɗai mutafi ba. Dama kafin lokacin already angama min duk wani abunda za'a buƙata na tafiya Yaya Ahmad ya tsaya akan komai akayi cikin lokacin daya dace. Sai Anty fadeelah tare aka haɗa akayi mana yaya Habibu kam dayake shi dama bai daɗe da dawowa ƙasar ba yanada duk wani abun buƙata sai Mummy itama haka.
Bayan na idarda sallah Ina zaune nayi tagumi Mama tashigo ta sameni ina Jin shigowarta na sauƙe tagumin da sauri tun kafin na sauƙe ta kalla dan haka takeni waje tazauna.
"Marmeeyy akwai wata matsala ce?" Dasauri na jijjiga kai. Murmushi tayi.
"Idan kinada wata matsala gara ki faɗamin tunda kinga nisa zamuyi nanda wani lokaci zaki ƙwana biyu baki ganni ba zakiso ace ina kusa ki faɗamin abunda kikeson faɗamin amma bazaki samu daman hakanba yanzune damarki da zaki samu zantawa dani fuska da fuska" hawaye yafara gangara a fuskata inajin gabaki ɗaya kamar rayuwata ne take shirin zuwa ƙarshe.
"Mama tayaya za'ayi na iya rayuwa ni kaɗai acan wata ƙasa wajanda babu ke babu Baba babu wasu ƴan uwana? Tayaya za'ayi rayuwa tayimin daɗi har yanzu nakasa tunanin yanda rayuwa zata kasancemin shin rayuwa zata tafi ko kuma tsayawa zatayi?"
"Tabbas rayuwa zata tafi Marmeeyy babu abunda zai tsaya kuma zaki rayu kamar yanda kowace mace take rayuwa agidan mijinta sai dai zaki rayu da kaɗaici zuwa na wani lokaci da zarar kin fara tara yara zasu ɗebe miki kaɗaicinki. Kisani bakece mace tafarko data fara barin garinsu ko ƙasarsu zuwa wata ƙasa da sunan aure ba dubu sunyi kuma sun zauna lafiya cikin farin ciki sun bawa abokan zamansuma farin ciki yanda zaki tafi yanzu sune zasu kasance danginki na har abada kamar yanda muke fata" Hawaye yakasa barin tsiyaya a fuskata ina shirin fashewa da kuka nake magana"
"Mama bakijin zafin tafiyar da zanyi ne? Inaga kaman baki fahimci yanda nakeji ba kowa nawa fa zan bari natafi can wani waje danyin rayuwa" saida tayi murmushi mai cike da ciwo sannan tace.
"Nasan yanda kikeji mana Marmeeyy tunda ina tunanin inajin fiye da hakan ko kwtaankwacin hakan nifa uwace tunda na haifeki baki taɓa tafiya mai nisa kinbarni ba sai yanzu zakiyi kuma tafiya wanda muke saka ran idan anyita anyine ta har abada sai dai kizo mana ziyara, ke kaɗai Allah yabani ƴa mace duka sauran mazane tayaya zakice bazanji ciwo ba? Ko naji ciwo yaya zanyi tunda ai ba'a kanki aka fara barin iyaye da gida ko gari ko ƙasa da sunan aure ba ba'a kanki aka fara irin wannan aurenba to yazama dole gabaki ɗaya mu sakawa ranmu haƙuri dan kisanu kije kiyi zaman aure kiyi ibada yanda ya kamata" Mama tayi tamin nasiha.
"Duk wnai abunda ya kamata na koya miki wanda idan kinyi aure zaki rayu a gidan mijinki na koya miki tub daga tasowarki ban bari sajda kika girma ko sai kinyi aure kinzo barin gida kafin nafara miki nasiha ba inada tabbacin duk suna ƙwaƙwalwrki abubuwanda zan ƙara miki bazasuyi yawa ba" tayi tamin nasiha da saida nayi kuka mai isata" dakyar na haɗiye kukana kawai Mama tamiƙe tanajin zafi aranta amma yaya zatayi? Dole ta ƙwantarwa Marmeeyy hankali ta nuna mata komai ba komai ba har ta ƙwantarda hankalinta.
"Mama fita zakiyi? Har yaufa baki taɓa tambayata ina sonsa ko bana sonsa ba" Tajuyo tayi murmushi.
"Kina sonsa mana Marmeeyy"
"Meyasa kikace haka bayan baki taɓa tambayata ba"
"Marmeeyy nifa mahaifiyarki ce lokuta dadama bakya buƙatar saikin furta kafin na gane abunda kike nufi"
"Mama zata iya yiwuwa biyyay kawai nake yiwa Baba ga zaɓinsa gareni shiyasa kike ganin kamar ina sonsa" na faɗawa Mama hakane saboda inaso ta bani wani dalili guda ɗaya wanda ni kaina zai gamsar dani cewa inason Hammood dan ina kokonton son danake masa. Alokacin ina tare da Hamma idan bai kirani na nakan damu na kirashi Amma hammood bakan iya cireshi araina daya kira badai kiraba ban damu ba"
"Banace A'a ba marmeeyy ta iya yiwuwa biyayyar ce tasanya soyayyar tashiga ranki abu guda dana sani shine kina sonsa, bari naje na dafawa babanku ruwan shayi dasauri na miƙe.
"Mama bari zan haɗa masa" toh kawai tace nafice zuwa kitchen na haɗa kayan shayin na ɗaura a wuta inajin shigowarsa na juye nakai masa. A palour na sameshi yana zaune nashiga da sallama bayan nayi masa sannu na zuba masa ruwan shyin na miƙa masa. Shi kansa ya lurada yanda jikina yadawo sanyi-sanyi. Daurewa yayi yayimun nasiha sannan yacemin Zanje gidan Hajiyarsa na ƙwana biyu."
"Washe gari Sassafe Natafi gidanta naji daɗin zaman danayi a gidanta danna koyi wasu abubuwa da bansamu na koya a shekarata sha tara ina neman ta ashirin a duniya ba. Kuma hajiya batajin kunya duk wani abunda yakamata ta koyamin tana koyamun shi har wasu daga cikin al'adu na zamantakewa da larabawa wanda bansan a yanda ta koyi hakanba.
Mummy kuwa anata wajen sayyaya kawai takemin tana kashe kuɗi wanda ita kanta batasan yawansu data kashe ba duk wani abunda tasan idan naje can zan buƙata ta siyamin maimakon ƙwana biyu saida nayi 5days a wajan Hajiya sannan nadawo.
Nasamu Baba da maganar Exam ɗita guda ɗaya wacve take kaina tubda dama ya riga yamin register bandai taɓa zuwa ko lactures bane nasiya material da zummar zanyi karatu kawai idan takama za'ayi practical ko wani abun sai naje. baba yace shi yanzu baisan yanda za'ayi ba tunda yasan tafiyarmu wannan satin ce gashi kuma exam ɗin gabaki ɗaya bazata wuce 7 weeks ba kuma baza'a fasa tafiya saboda exam ba abunda za'ayi shine udan naje nayiwa Hammood maganar jarabawar duk da yasan bazai rasa masaniya akanta ba.
A daren ranar jirginsu Hammood ya sauƙa a abuja ƙwana ɗaya yayi a abuja ya iso bauchi. Adaren ranar kuma Yazo gida saida suka gaisa dasu Mama sannan nashiga wajansa. Kallo ɗaya yayimin yasan ina cikin damuwa nikam nakasa kallonsa gabaki ɗaya ma. Hira sai jifa-jifa mukeyi san dama kwana biyu gabaki ɗaya banida walwala tunda nasan ya iso Abuja sai rashin walwalar ta ƙaru bare yanzu danake ganin baifi ƙwana biyi nabar gida ba. Hammood cikin kulawa yakira sunana.
"Zaynab" na ɗago na kalleshi tunda bashiga sai alokacin na kalleshi idanuwanmu suka haɗe waje ɗaya gabana yahau faɗuwa dasauri na kawarda idona. Ajiyar zuciya ya sauƙe sannan ya jefomin tambaya.
"لا تريد الذهاب معي"
(Bakison tafiya ne dani)?" Dasauri na gyɗa kaina alamun eh. Yayi murmushi yasan za'a rina."
PAID BOOK
Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab m Bawa JAIZ BANK Ko katin MTN ta wannna lambar 08161146563 shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya Hankli kwance zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike."
ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun banking Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya
Shiru nayi ina sauraron abunda zaice dan ganin yayi murmushi ya ƙaramin ƙarfin guiwa.
"I know bakizo tafiya ba amma yaya za'ayi? You have to kamar yanda na faɗa miki abaya cewa duk ranarda nasaka ƙafata a ƙasarnan bazan tafi batare da keba and yanzu gashi nazo nasan za'ayi haka yasa na ƙara miki morerthan 1month akan lokacin gama school ɗinki yanzu tunda na saka idanuwana akanki bazan iya tafiya ni kaɗai ba, wannan dalilin yasa tunda natafi ban kiraki a waya ba dan ina tunanin da Zarar naji muryarki bazan iya yimiki adadcin ƙarin lokacin dana sanyawa raina zanyi ba, I'm sorry amma wannan karon yazama dole nutafi tare" kukan taɓara na fashe dashi dan dajin kalamansa suna fitowane daga zuciyarsa bazai iya barina na ƙara lokaci tare da ƴan uwana ba. Ya dawo wajanda nake a zaune cikin sanyayyar muryarsa yafara rarrashina yana mamakin yanda kuka bayamin wuya danasaan yanda kukana yake cutar dashi da bazan sake yarda ko drop na hawaye ya ɗiga a idona ba.
"Shhhh is okay Zaynab please لا تبكي (Dont cry) yanzu toh we're not leaving tomorrow sai Jibi" na maƙe kafaɗa nacigaba da kukana. Hannuwansa ya sanya ya kamoni gabaki ɗaya ya shigar dani jikinsa ya rumgume lokaci guda kukan ya tsaya batareda ya furta wata kalma ta rarrashi ba na rumtse idanuwana ina shaƙar ƙamshin jikinsa. Shima ya ɗaura kansa akan gashina yana shaƙar ƙamshin dayake fitowa daga ciki. Dama Mummy ta bada an haɗamin Humra masu masifar ƙamshi kusan kullum saina turara jikina dasu da turaren jiki dana gashi da kulaccam na jiki dana gashi. Mamakin irin ƙamshin dayaji a jikina yakeyi yaji ƙamshi kala-kala a duniya na turaruka brand masu masifar ƙamshi da tsada amma bai taɓa cin karo da makamancin ƙamshin dayakeji a jikina ba bakowani irin ƙamshi bane yake masa daɗi he's picky about turaruka shiyasa turarensa yake na daban amma yayi admitting wannan ƙamshin mai daɗine gashi yana sauƙarda nutsuwa shiru mukayi gabaki ɗayanmu kowanne da abunda yake saƙawa a cikin ransa. A hankali na raba jikina da nasa na sunkuyarda kaina dan banaso mu haɗa idanuwa murmushi yayi ganin kukan ya tsaya. Sai alokacin yasamu ƙarfin lallashi amma lokacin ina kukan rasa abunda zai faɗa wanda zai ƙwantarmin da hankali yayi dan gabaki ɗaya rikicewa yake idan yaga hawayen fuskata sai dai shi rikicewarsa ba'a iya ganeta dan sai dai kawai ya tsaya ya tsura ido batareda yasan abunyi ba.
"I'll إن شا اللله be good to you ki kwantar da hankalinki Ina Sonki sosai bazan cutar dake ba in sha Allah bazaki samu wani tashin hankali a gidana ba zan tsaya miki a komai a matsayina na mijinki and your protcetor bazan yimiki alƙawarin cewa bazakiyi kewar gida ba amma I'll be there na ɗebe miki kewar da kike tare da ita. kuma bazance zan kasance tare dake a kullum ba sai dai ke zaki iya kasancewa tare dani a kullum Idan kinso zaki bini duk yanda zan saka ƙafata muje tare dan banaso ki kasance cikin kaɗaici" nayi shiru ina sauraronsa wato dai barina a gidane bazaiyiba ya rantse sai mun tafi a wannan tafiyar. Baiyi dare sosai kamar yanda ya sababa baifi 1hour ba yatafi saboda akwai abubuwanda yake buƙatar yi kafin yabar ƙasar kai tsaye cikin gida na nufa dukaninsu suna harabar cikin gidan Har mummy dake shashinsu ɗaya da Baba kuma a palourn Baban muke zama shiyasa tafita tabamu waje. Na ƙarasa wajan da suke zaune ana kallona ansan naci kuka.
"Kuka kikaje kikayi masa kenan Marmeeyy? Kina tunanin kukanda zakiyi shi zaisa a fasa tafiyar?" mama ta faɗa cikin ɓacin rai.
"Toh dan tayi kuka shine tayi laifi? Waye baiyi kuka ba lokacin da zai bar gidansu? Kefa a gari ɗaya anguwa babu nisa haka kikayita zabga ihu har aka shigo dake cikin gidannan kina ihu amma bakiyi laifi ba sai ita wacce bama gari ba ƙasar za'a bari ta ita gabaki ɗaya idan tayi kuka tayi laifi?" Mama taja baki tayi shiru jin Mummy na shirin yimata tonon silili a cikin yara. Naje na zauna wajan Mummy na ƙwantar da kaina a kafaɗarta. Cikin muryar kuka nace.
"Mummy kijifa wai jibi zamu tafi dan Allah kiyiwa Baba magana yace masa yabari sai wani sati"
"Au jibi? Kinji tafiyar yanzu tadawo jibi ai Marmeeyy da gobe ne ma tafiyar ta iya yiwuwa yaji tausayinki ne ya ƙara kwana ɗaya akai kuma yanada abunyi ai a cikin satinnan naji Ahamd yana faɗa"
"Mummy toh yatafi mana sai mutafi abayansa ai ba sai lallai muntafi tare ba idan muka isa sai yasaka aje a ɗaukomu"
"Kinga Marmeeyy ni ban is ada wannan zance ba bawan Allahn nan dai yayi ƙoƙari wallh aure yana neman shekara anata jaa masa lokaci saifa da akayi aurenku sannan akayi na Ahamd gashi matar Ahmad yanzu inaga cikinta yakai wata 6 shiyasama bazamuje tare dashi ba ko bikin Aysha yanzu wata 4 yake ciki ina muka isa muce masa yatafi wai sai bayan sati ɗaya? Sati ɗya da jibi ai duk ɗayane wajan ubangiji idan darai da lafiya" na fashe da kuka.
"Wallh Mummy nikam a wajena ba ɗaya bane ko ƙwana ɗayane idan zan ƙara cikin ƴan uwana zanji daɗi"
"Nidai wallh Marmeeyy bansan yaushe kika dawo haka ba gabaki ɗaya kin dawo sakaliya wai akanki aka fara aure da zakiyita fitowa mutane da sababi kala-kala? Ba gashi zaku tafi da Fadeelah da Mummy ba harda Yayanki mafa waya samu irin gatan da kika samu? Kowa shi kaɗai aka kaishi gidan miji amma banda ke wacce gata yayiwa yawa" mummy tayi dariya.
"Toh idan Mummy da fadeelah da Habibu sunanan Mama tana nanne? Ko akwai Baba? Babu anty babu ƙannenta Dan Allah ki saurarawa yarinyar nan taji da abu guda ɗaya." Mama taja baki tayi shiru sukaci gaba da rarrashina harda Anty.
Washe gari sassafe nida Anty fadeela mukaje gidan Aysha har azahar mukakai acan daga nan nawuce gidansu Maryam. Itama tun safe tamin waya akan zatazo nace mata gani gidan Aysha idan nagama zan biyo ta gidan. Kuka sosai mukayi nida Maryam Ummi tana aikin lallashi dama yanda muka shaƙu tasan dole idan akazo rabuwa da aiki. Daga ƙarshe tare muka tafi da ita agidanmu muka ƙwana. Da safe Haka mama tatashi ido jajazir da alamu taci kuka cikin dare amma sai fisfisgewa takeyi dan kar agane. Nima tunda natashi dasafe nake kuka maryam tana tayani mama ganin bazata iya rarrashi ba tabar mana ɗakin gabaki ɗaya. Tun safe nake zuwa ɗakin Baba a kulle gashi wayarsa bata shiga. Dana matsa da zuwa Mummy tacemin ai Baba tunda yafita sallar asubahi bai dawo ba dan dama haka yaƙwana baiyi bacci ba. mummy tace ko runtsawa baiyiba. 12am zamu tafi gashi har 10 Baba bai dawoba nazauna ina kuka ni bazan tafi ba sai naga Baba duk ƙarfin halin Mama saida ta zauna ta rarrasheni. Yaya habibu yafita neman Baba yaduba duk yanda ya kamata amma bai sameshi ba. Hamma ya kawo Aysha muyi sallama saiga Aysha tana kuka riras ganin yanda nake kuka kuma tasan tafiya zamuyi" tsabar kuka jikina har yayi laushi kukan yadaina fita da sauti sai zafin zuciya da nakeji 12 kuwa muka tashi tafiya alokacin danaga tafiya za'ayi nafara tijara babu wanda baiyi kuka ba kaff gidanmu. saida Mukabi gidan Hajiya da Gidan Baba (Alhaji habibu) mukayi masa sallama sukayitamin nasiha sannan muka kama hanyar airport. jirginmu ya sauƙa a abuja amma gidansu Mummy muka wuce sai nazamo kamar wata celebarity kowa son kallona yake ni ɗaki ma nawuce dan haushin mutane nakeji daƙayr mummy tasaka naci abinci ahakanma babu yawa ban fitoba sai bayan la'asar liss nasmau Mummy jibge da kayyayaki agaba da turaruka da abubuwa wanda bansan menene su ba jibgi guda ashe ananma tasa a haɗa mata wasu kayan wancan an rigada an gama dasu dan har sun hau jirgi waɗannan ne zamu tafi dasu. Har kayan sawa da Mummy ta ɗinkamin bansan adadinsu ba gasunan akwati set guda mai 4pcs. Munyi waya da Maryam daga zuwanmu kusan sau 5 kenan a lokacin na faɗa mata saƙonta dana bari awajen Mama. Har wayar Hannunama yanzu ƙarama ce nabar wancan a bata Baba har lokacin wayarsa a kashe take. Kuɗin wancan account ɗin kuwa tunda aka saka ranar tafiya kullum sai nayi tranfer wa Mama iya gejin Tranfer na account ɗin per day.
Bayan magrib jirginmu zai tashi kafin magrib zazzaɓi ya rufeni saboda kukan danasha. Mummy ta haɗamin ruwa nayi wanka tazo tabani magani nasha sai bacci ana kiran sallah naji a kunnena natashi nayi sallah ina zaune har akayi isha'i natashi na gabatar da sallah ban ida ba saiga Mummy tashigo akan nafito. Har lokacin jikina da ɗumi Mummy ta ƙaramin maganin dan bataso jikin yayi tsanani muka tafi airport kai tsaye. Ayanda naga alamun jirgin babu wasu mutane a cikinsa muka shiga aka kaimu wajan zamanmu muka zauna. Bamufi 30minute da zama ba jirgin ya ɗaga dake nasha magani lokaci guda bacci ya ɗaukeni ga zazzaɓi Sa'i-sa'i kawai nake farkawa ina komawa bansan awa nawa muka ɗauka muna tafiya ba dan inajin zazzaɓi sosai hakan yasa baccin yayi nauyi. A hankali nake buɗe idanuwa na Nayi miƙa haɗe dayin addu'a idona har sun kumbura saboda kuka har alokacin hucin zazzaɓi fita yake a jikina.
Idanuwana suka sauƙa akan Hammood wanda yake zauune cike da damuwa da alamu jira yake natashi dasauri na miƙe ina kallon gefe babu mummy da Anty fadeelah ko Yaya habi namiƙe a hankali zan zauna dan jiki a babu ƙwari ya taimakamin na tashi zaune ina kallon gefe yagane wanda nake nema.
"Sun tafi already mun iso you were sleeping akwai zazzaɓi a jikinki naga kaman kinajin daɗin baccin shiyasa nasa suka fara gaba idan kintashi saimu tafi tare" Na kalleshi da mamaki kawai dan ina bacci shine bazai tayar dani ba? ni banmasan cewa tare muke tafe dashi ba dan 2days kenan banji daga fareshi ba ashe shi tun asuba ya wuce abuja yasauƙa a masauƙinsa sannan bayan isha'i yatafi filim jirgi shahsin daya zauna da muƙarrabansa sabanne yasa bamusan yana ciki ba. Ina ƙoƙarin miƙewa yace.
"Idan baki warware ba zaki iya baccin kawai ko kaɗanne ki ƙara na girgiza kai danni yanzu zanfi ganewa na ganni wajan Mummy. Tallafeni yayi a jikinsa muka sauƙo motoci suna jiranmu ya buɗe mota ya shigar dani a hankali sannan shima ya shiga ta wani gate daban mukabi na filin jirgin batraeda mun fito cikin mutane ba da dukkan alamu cincirindom mutane suna jiran sauƙowarsa shikuma bayason hakan hankalinsa gabaki ɗaya yana gareni gani yake duk ƙarancin hayaniya zata takuramin ne. Tafiya mai tsayi ce takaimu gidan da jami'an tsaro a zagaye da ko'ina. Ni dake a kwance nake idona suna lunshe ban lura da mutanen da suke jiran isowarsa ba ciki harda ƴan jaridu muna shiga aka rufe gate babu wanda zai iya hango cikin gidan. Nanma taimakamin yayi muka shiga har ciki yanayin