Header Ads
Showing 54001 words to 57000 words out of 149432 words

Chapter 19 - INTEESAR Book Complete by Zainab Abdullahi.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

1370

Ads at the middle of Article

waye mijinta hawaye ne kawai ke zuba a kan fuskarta kamar an bud'e famfo.




Bangaren Muhdeen kuwa yana zaune a office d'insa kan sofa yayin da idanunsa a lumshe kamar mai barci amma ba barcin yake ba, Jabeer ne ta turo k'ofar ya shigo har lokacin bai bud'e idanunsa ba, Jabeer sallama yayi masa.


"Assalamu Alaikum"


Can k'asan mak'oshi ya amsa, la'b'bansa ne kad'ai zaka kalla ka gane yayi magana.


"Ya kamata ka tashi ka tafi wajen amaryarka k'arfe goma yanzun, tunda ka ce baka buk'atar rakiyar mu ai sai ka tafi Allah ya bada zaman lafiya."


Banza da shi Muhdeen yayi kamar baiji shi ba, dama baisa ran zai amsa masa ba don yasan halinsa, amma duk da haka bai damu ba sake magana yayi yana cewa


"Kasan wallahi idan har baka tashi ka tafi wajen Amaryarka ba sai na kira Dady yanzun nan a waya na fad'a masa cewar kana nan asibiti zaka kwana ba zaka koma gida ba saboda baka son auren da suka yi maka."


Still shiru yayi kamar baiji me ya ke fad'a ba tsawon mintuna biyar bai ce komaiba ran Jabeer ne ya 'baci yana da niyyar yin magana ne wayarsa ta soma ringing dubawa yayi matarsa Maryam ce, dama tana gidansu Mummy wajen taron bikin ganin karfe 10 bai zo ya d'auketa sun tafi gida ba ne yasa ta kiranshi, ɗaga wayar yayi tare da cewa.


"Hello My dear kinji ni shiru ki?"


Jin muryarta yayi kamar zatayi kuka tana cewa


"Dan Allah ka zo mu tafi gida na gaji ina son na huta pls"


Dariya yayi yana cewa


"Karki damu ganinan zuwa nazo na d'auke ki idan muka tafi gida zan gasa maki jikinki da ruwan d'umi nayi maki tausa zaki ji dad'in barci."


Dariya tayi tare da katse kiran, dubansa ya maida kan Muhdeen ganin baima da niyyar tashi sai ma kishingid'a da yayi ne yasa Jabeer duba wayansa yana lalubar number Dady bugu d'aya a na biyu Dady ya d'aga wayar inda Jabeer yasa speaker na wayar Muhdeen najin Muryar Dady na cewa


"Hello Jabeer ya akayi ne"?


Kafin Jabeer yayi magana cikin zafin nama Muhdeen ya fisge wayar tare da katse kiran, wayoyinsa ya d'auka ya saka a aljihu ya nufi hanyar fita Jabeer yabi bayansa yana k'yalk'yata dariyar mugunta.






Daga alk'amin✍️


Zainab Abdullahi. K.N.T
Maman Ihsan






Don k'arin bayani


09065327995



Love u oll😍😘






Comment & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89








*INTEESAR*




Story & writing by✍️


Zainab Abdullahi (Maman Ihsan)






*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*








Page3️⃣6️⃣


Kafin Jabeer ya yi magana cikin zafin nama Muhdeen ya fisge wayar tare da katse kiran, wayoyinsa ya d'auka ya saka a aljihu ya nufi hanyar fita Jabeer ya bi bayansa yana k'yalk'yata dariyar mugunta.saida suka je inda za su rabu ne Muhdeen ya mik'a masa wayarsa kowanne ya shiga motar sa ya kama hanyar fita asibitin.


Jabir gidansu Mummy ya nufa yayin da shi kuma Muhdeen ya nufi gidansa.


Inteesar kuwa tana can d'akinta, k'udunduna saman gado ta had'a Kai da guiwa sai kuka take yi har da sheshshek'a,tana tuna Ummanta da Abbanta.


Horn yayi mai gadin gidan ya lek'a ta k'aramar k'ofa,ganin Mai gidan ne yasa shi saurin wangale gate d'in gidan,cinno hancin motar yayi cikin gidan a parking space yayi parking,ya fito yakai tsawon mintuna goma yana zaune a cikin motar kafin ya fito ya nufi cikin gidan.


Duk da cewa part biyu ne gidan amma bawai suna rabe da juna bane,kusan a had'e suke kuma k'ofa d'aya suke da ita dole sai mutum ya bi ta falon Inteesar kafin ka shiga falon Sumayya,kuma ko wane bedroom guda hud'u suke da dasu,kuma kowane bedroom da toilet d'insa a ciki akwai kuma kitchen da dinning area kowanen su.


Turo k'ofar yayi k'amshin turare ne suka tarbe sa,wanda bai ta'ba jinsa ba a gidan,kai ya saka da nufin wucewa part d'in Sumayya sai ya jiyo sheshshek'ar kukan Inteesar,kamar ya wuce sai ya nufi d'akin Inteesar d'in,tura k'ofar d'akin yayi ganinta zaune yayi ta k'udundune ta had'a Kai da gwuiwa sai kuka take kamar ranta zai fita.Bata San ya shigo d'akin ba kukanta kawai take yi kamar ranta zai fita.


"Kukan uwar me kikewa mutane?"


Muryar da taji ya dakai dodon kunnenta ne yasa taji gabanta ya fad'i rass don idan har ba mafarki take ba wannan muryarsa ce don ba zata ta'ba mancewa da wannan muryar ba,azuciyarta take magana


"Kenan wannan mugun mutumin shine mijina? Kai ina bazai yiwu ba,bashi bane."


'Dago kumburarrun idanunta da tayi ne yasa ta d'aura su akansa ne yasa gabanta yayi mummunar fad'uwa ,tabbasa shine.


"Kallon me kike mani ne?kin zuba Mani ido kamar mayya,ba ke kika ce kina sona ba?"


Kai ta girgiza alamun a'a idanunta na zubar da hawaye ta fara magana.


"A'a ni wallahi bani bace nace ina sonka."


"To kika yarda kika aure ni?kuma amincewa da aure na da kikayi shine kuskure mafi muni da kika tabka a rayuwarki,dan sai kin gwammace dama baki aure ni ba,tukunna wai me yasa baki bijirewa auren ba kika amince duk da kin San ba k'aunarki nake ba?"


Share hawayen fuskarta tayi tare da cewa


Ban san Kai ne mijin da aka aura mani ba sai yanzun,kuma Koda na sani bazan ta'ba bijirewa zancen iyaye na ba,domin duk wanda yake son rayuwarsa tayi albarka bazai ta'ba bijirewa zancen iyayensa ba,neman albarkar iyaye da biyyaya a gare su yasa ban bijirewa zancen auren ba."


"Ko da hakan yana nufin bak'in cikinki ne?"


"Koda hakan yana nufin mutuwa ta ce,bazan ta'ba bijirewa zancen iyaye na na ba."


"Good"


Daga nan yasa Kai ya fice,ita kuma kukanta ta cigaba da yi don bata ta'ba tinanin cewa Muhdeen aka aura mata ba,haka ta cigaba da kukanta a k'udundune har barcin wahala yayi awon gaba da ita.


Shi kuma yana fita d'akinsa da ke cikin falon Sumayya ya nufa kayan jikinsa ya rage ya fad'a toilet Dan yin wanka,


K'arfe uku na dare Inteesar ta farka daga barcin wahala da tayi, toilet ta fad'a tayi wanka da ruwa mai d'umi sannan ta d'auro alwala ta fito man shafawan Hajiya Bilkisu Mai k'amshi ta shafa doguwar riga ta atamfa ta saka ta sanya hijab don yin sallah,nafila raka'a biyu tayi sannan ta fara karatun alqur'ani mai girma,tana zaune har har lokacin sallah ta tashi tayi sallar asuba,bayan ta idar ne ta dinga yin azkar har sai da gari ya waye tayi addu'a sosai akan zaman auren nan tare da rok'on Allah ya k'ara mara hak'urin zama da Muhdeen.


Tashi tayi ta fito daga d'akinta don tsananin yaunwa ke damunta rabon da ta ci abinci tun karin da tayi jiya da safe,da rana bata ci komai ba haka ma dare yayi ba abunda ta saka a cikinta,ba yadda Mufida bata yi da ita ba amma sam tak'i cin abinci dole ta ha'ura ta kyaleta.


Fitowarta falon yayi dai-dai da isowar mai aikin gidan,wato kande wacce take zuwa ki wace safiya tayi share-share da goge-goge,yau tayi sammakon zuwa ne saboda ranar da aka sanar da ita zancen aikin an fad'a mata cewa matar gidan zata dingayiwa aiki da bata ga matar gidan ba sai ta tambayi Ishaq ya sanar da ita cewa tayi tafiya ne,to sai jiya da taji labarin matar gidan zata dawo yasa ta sammakon zuwa,dattijuwa ce mai kimanin shekaru arba'in.


Ganin Inteesar ya sa ta durk'usa da niyyar gaishe ta,kafin ta kai k'asa Inteesar tayi saurin d'ago da ita tana cewa.


"Haba Baaba ai bai kamata ace kin durk'usa mani ba,ni ce ya dace na durk'usa maki,ina kwana?"


Murmushi matar tayi tare da cewa


"Lafiya lau sannu Hajiya."


Inteesar shiru ta yi tana kallon matar ita dai bata santa ba kuma gashi ta daka sammako wajen zuwa gidan,tana cikin wannan tunanin taga matar ta durkusa tana gaida Muhdeen.


"Ina kwana alhaji"


Alamu yayi mata da hannu alamun ta tashi tsaye,ba tare da ya amsa gaisuwar da tayi masa ba, Mi'kewa ta yi.


"Dama ni ce mai aikin da ke zuwa kullun ina gyara gidan lokacin da baki nan,na ji labarin kin dawo ne yasa nayi sammako ko akwai aikin da zan taya ki da shi."


Kafin Inteesar tayi magana ta ji Muhdeen ya fara magana


"Ai ba ita ce matar gidan ba,matar gidan bata dawo ba tukunna,so it's wannan bata buk'atar'yar aiki don ita ma 'yar aikin ce."


Jinjina kai Baaba kande tayi


"To Alhaji zan cigaba da zuwa ina aikin Koda matar gidan bata dawo ba kamar yadda na saba yi a kwanakin baya?"


"Ba buk'ata Koda ta dawo wannan ce 'yar aikin da zata dinga mata aiki,sabida haka aikinki ya k'are,amma kafin nan ina zuwa."


'Dakinsa ya nufa, sai gashi da kud'i kimanin naira dubu d'ari ya mik'a mata amsa tayi tana godiya duk da ta rasa aikin ta tasa ran dogaro dashi amma kud'in zata ja jari dasu.


"Nagode Alhaji Allah ya saka da alkhairi,ya k'ara arziki da wata wadata."


Ficewa tayi tare da yi masu sallama cikin jin dad'i


Kallonsa ya maida ga Inteesar fuskar nan a tsuke,yayinda ita ma ta kallesa cikin girmamawa ta ce,


"Ina kwana?"


Tsuki ya ja tare da cewa


"Na sallami mai aikin gidan nan daga yau ke zaki maye gurbinta,aikin da takeyi naki sai ya ninka na ta,don ita falo da kitchen kawai take shiga ta gyara ke kuma daga yau na kafa maki doka wajibi ne a gare ki bayan falo da kitchen da Zaki dinga sharewa kina gogewa duka bedrooms d'in gidan nan guda takwas, da toilets nasu guda takwas wajibine ko wace rana sai kinbi su d'aya bayan d'aya kin share kin goge su kin wanke ko wane toilet,sannan ina son na ga ko ina na gida na a tsaftace banason k'azanta,sannan ba sau d'aya ba safe da yamma Zaki dinga aikin, idan kunne ya ji gangar jiki ya tsira."


Shiru tayi tana tunanin uban aikin da wannan bawan Allah ya d'ora Mata,bata gama nazari ba taji muryarsa yana cewa.


"Ki jirani nan Ina zuwa"


"To"


Daga nan ya nufi d'akinsa ba jimawa ya fito hannunsa d'auke da keys ya mik'a mata.


"Kar'bi wad'annan makullayen ki Fara da wancan d'akin"


Ya k'arasa maganar yana nuna mata d'akin Sumayya,daga nan ya koma cikin d'akinsa ya barta nan tsaye,cikin sanyin jiki ta k'arasa cikin falon Sumayya tare da duban saitin da taga ya mata nuna mata, tsayawa tayi tana k'arewa falon kallo a zuciyarayarta ta ce,


"Na fahimci mutumin nan so take kawai ya wahalar dani,ya za'ayi manyan falo guda biyu tare da bedrooms guda takwas ko wanne da toilet da ga kitchen guda biyu kowane falo da dinning romms da table da chairs ko ina sai na shere na goge,kuma safe da yamma harda d'akunan da ba kowa a cikinsu ba datti sukeyi ba tunda ba'a shigarsu amma suma wai safe da yamma."


Goge k'wallan da ya gangaro mata tayi tare da cewa


"Allah ka ka bani hak'urin zama da shi"


Bud'e k'ofar d'akin Sumayya tayi ta shiga bakinta d'auke da sallama,turus tayi tare da dafe k'irji ganin yadda d'akin duk a hargitse komai kaca-kaca ga kgilasai da aka farfasa da kwalaben turarurruka kala-kala ga suturu duk a yayyage,katifa a gefe pillows a watse mirror a tarwatse photon Sumayya da ta gani a manne a bangon d'akin ne ya tabbatar mata da cewa d'akin Sumayya ne a zahiri tayi magana.


"Oh ni Inteesar mai ya faru da d'akin nan ne kamar anyi girgizan d'aki?ta ya ya zan fara wanna aikin ne?kuma da dukkan alamu d'akin Sumayya ce to ina ita Sumayyar take ne?kuma me ya faru da d'akinta haka?"


Sanin ba Wanda Zai amsa mata tambayarta yasa ta fara tunanin ta Ina zata fara,ganin takalmin dake k'afarta irin masu taushin nan ne idan ta taka kwalba zata iya huda takalmin ta shiga k'afarta yasa ta fita dan canza takalmin da ke k'afarta,ba


Ba jimawa sai ga ta ta canza takalmi ta sanya wani flat shoe da da abunda zata zatayi shara ta zuba,katifar ta fara ja ta jingine da gadon ta kwashe pillows d'in abunda ya bata mamaki shine,kayan suturar da ta gani a k'asa ta fara d'agawa abun da ya bata mamaki shine ganin duka suturar a yayyage ba mamora,har cikin closed d'in ta shiga abun mamaki suturan dake cikin wurin duka a yayyage suke haka ta dinga kattara kayan da kwalaben sai dai wad'anda ta ga robace ba kwalba ba da kuma wada'anda suke a gwangwani ba su fashe ba ta kwashe ta jerasu gaban mirror d'in don ba abunda ya same su.


Tsawon lokaci ta d'auka tana gyara d'akin Sumayya kafin ta kammala,ta shirya d'akin tsaf ta gyara shi ta wanke toilet sannan ta janyo k'ofar ta fito.


Haka tabi sauran two rooms d'in duk ta gyara kafin sannan ya rage saura d'akinsa, k'wank'wasawa ta yi yana jinta yayi banza da ita, har sau uku amma ko gezau yana zaune kan sofa sai da ya ga dama ya ce,


"Shigo"


Turo k'ofar tayi tare da sallama


"Assalamu Alaikum"


"Wa'alaiki salam"


Tsayawa tayi kanta a k'asa tsawon mintuna goma tana tsaye amma bai ce mata komai ba,tsuki ya yi.


"Dalla malama idan ba za ki yi magana ba ki fita ki ban waje"


Cikin rawar murya ta ce,


"Na gama da sauran d'akunan ne naka ya rage shine na zo na gyara"


K'arar k'ofar falo sukaji alamun suna da bak'o,hakan yasa ya fita don zuwa dubawa.


Kids ya bud'e k'ofar Mufida ya gani d'auke da basket an jira flasks d'in abinci ciki, murmushi ta sakar masa


"Barka da safiya Yaya


Shima murmushin ya sakar Mata


"Yauwa kin tashi lafiya?"


"Alhamdulillah,dama Mummy ce ta ce na kawo maku breakfast"


Yana k'ok'arin kar'bar basket d'n ta ce,


"Yaya gaskiya sai naga besty na zan tafi"


,hanya ya Bata ta shiga ta ajiye basket akan center table.


Okay tana d'akina zauna na kirata"


Zama tayi akan kujerar dake falon tana jiran inteesar.koda ya shiga tana gyara gadon ya sanar da ita cewa ta zo murmushi ta yi cikin jin dad'i ta fito yana biye da ita a baya,Mufida na ganinta ta mik'e ta nufeta a guje ta fad'a jikinta,muryar Muhdeen suka jiyo yana cewa


"Ke Mufida meye haka ki bi mani amarya a hankali fa ka da ki yi mani illa baki San ba na son abinda zai wahalar mani da ita ba?ki barta ta ji da kanta."


Inteesar ce ta bisa da kallon mamaki,bai gama ba ta mamaki ba sai da taga ya sakar murmushi tare da kashe mata ido d'aya.








Daga alk'amin✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
Maman Ihsan




Don k'arin bayani


09065327995






Love u oll😍😘


Comment and shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89








*INTEESAR*




Story & writing by✍️


Zainab Andullahi K.N.T
(Maman Ihsan)










*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*








*GARGA'DI*


Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce,don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga.






Wannan kagaggen labari ne,banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba, Idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba,arashi ne Mai kashe auren wawa.




*SADAUKARWA*


Wannan shafin naku ne masoyan Inteesar 'yan group d'in INTEESAR HAUSA NOVEL,inajin dad'in comment naku na book d'in nan sunayenku bazai lissafu ba,ina godiya da addu'arku gare ni Allah yabar k'auna.






*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*


Page3️⃣7️⃣


Inteesar ce ta bisa da kallon mamaki,bai gama bata mamaki ba sai da taga ya sakar Mata murmushi tare da kashe mata ido d'aya,mamaki da Al'ajabi suka hana Inteesar motsi kallonsa kawai take kamar gunki,jan hannunta da Mufida tayi ne ya saka ta sakin murmushi tana cewa.


"Ya dai wannan kallon haka kamar yanzun kika fara ganinsa ba tare kuka kwana a gidan ba,koda yake ba zaki gaji da kallonsa ba don yaya na na musamman ne samun kamarsa sai an tona."


Murmushin yak'e Inteesar tayi tare da cewa


"Yauwa Mufida na manta waya ta a gidanku tun kafin a kaini gidan Hajiya Bilkisu,don kwanakin da nayi gidanta ma duka ba waya a hannuna."


"Okay to Ina kika aje wayar ne?"


"A d'akin Yaya"


Murmushi Mufida ta yi tare da cewa


"To shikenan zan d'auko maki anjima idan zan kawo maku lunch,amma ki daina kiransa da Yaya don yanzun kunzama 5&6 kamata yayi ki canza masa suna na masoya mai dad'i kin gane ko?"


Ta'be baki Inteesar tayi,tare da kallon Muhdeen sai gani tayi ya galla Mata harara sunkuyar da Kai k'asa tayi , Mufida ta cigaba da cewa.


"To Ni zan tafi sai na sake dawowa."


Fuskar tausayi cikin marairaicewa ta ce,


"Mufida tun yanzun zaki tafi ki barni ni kad'ai ki bari ki yini dani mana ko zaki d'ebe Mani kewa, pls aminiya ki tsaya kinji."


Kafin Mufida ta yi magana Muhdeen yayi saurin cewa.


"Kinga Mufida aiko ki akayi kije ki isar da sak'o kince mungode,zaki iya tafiya ki gaida mani Gwaggo da Mummy."


Murmushi tayi tare da kallon Inteesar


"Karki damu my besty zanzo zuwa na musamman na wuni dake kinji."


Murmushi Inteesar ma ta maida mata tare da cewa.


"Shikenan ba damuwa"


Zuba mata ido mufda tayi tana nazartar yanayin Inteesar,don tasan Inteesar farin sani yanayin yanda ta ganta da dukkan alamu tana cikin damuwa,amma sai ta share zancen ta barshi kila saboda auren da aka yi mata ne kuma ba lallai tana son wanda aka aura mata ba kuma gashi Bata saba da shi ba kila shiyasa ta damuwa amma a sannu zata saba da shi.


Sallama ta yi masu daga nan ta fice,dubansa ya maida ga Inteesar fuskarsa a tsuke ya fara magana


"Idan ta zauna a nan gidan uwar me zata yi maki?bari kiji na fad'a maki doka ce bana buk'atar bak'i a cikin gidana,kada ki tara mun k'awayenki bana buk'atar kowace mace tazo mani gida babu wacce zata zo gidan nan da sunan zuwa wajenki,ko wace ce a wajenki kuwa Ina fatan kin gane."


Kai ta jinjina


"To amma me yasa zaka Hana kowa zuwa wajena?kuma ko a gidan kurkuku nake ai baza'a hana a ziyarce ni ba ballantana gidan aure na."


Da mamaki yake kallonta


"Ke! Ni kike fad'awa magana lallai kuwa kin samu sake,to bari kiji da kike maganar gidan kurkuku to nan tamkar gidan kurkuku ne a wajenki ki aje wannan a cikin zuciyarki."


Shiru tayi kanta a sunkuye idanunta sun cika tab da k'walla.


"Maza kije ki gama aikin da zakiyi,ba tare da tsayawa ba har sai kin gama,tukunnah ma d'akuna nawa kika gama dasu?"


Yanzun na gama da d'akuna hud'u saura hud'u,sannan na dawo kan falo da kitchens."


'Dan Jim tayi tana son ta yi masa magana tana tsoronsa ganin hakan yasa shi cewa.


"Maye kike yi haka kamar wata munafuka,idan zakiyi magana kiyi idan ba zaki yi na ki 'bace Mani da gani."


Cikin inda

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads