Header Ads
Showing 75001 words to 78000 words out of 149432 words

Chapter 26 - INTEESAR Book Complete by Zainab Abdullahi.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

1387

Ads at the middle of Article

na k'arasa dake gida."


Kai ta girgiza alamun a'a


"Ka barshi kawai zan shiga adaidata sahu."


Nan dai suka matsa mata akan cewa sai ta shiga,dakyar ta amince ta shiga,tafiyar mintuna biyar ya ajiye Khadija a wani shagon saloon inda ya umarci Inteesar ta dawo gaban motar,dan haka ta dawo gaban motar sannan yaja suka tafi.


"Me yasa kullun na kira wayarki bata shiga,tun ranar da muna cikin magana kika katse kiran ban sake samumki ba."


Tasao ta sanar da shi ita matar aure ne a yanzun amma kuma wannan ai ba aure bane,tunda da zarar matarsa ta dawo zai sake ta,don haka ta yi shiru ta ce


"Bana da waya ne."


"Okay badamuwa mun kusa k'arasawa Ubasanjo complex sai mu shiga ki za'bi kalar wayar da kike so."


Da sauri ta kalle shi


"Dan Allah ka rufa mani asiri,yanzun idan ka siye mani waya me zance idan na koma gida?"


Dariya ya yi


"Kedai akwai matsoraciya to meye a ciki?nifa so nake su san da ni fa,duk da sun sanni amma ina son susan cewa aurenki nake so."


"Naji amma duk da haka ba yanzun ba,kaga yamma ta yi ina sauri na koma gida."


Dariya yayi yare da cewa


"Kinfi son ki zauna kurma ko?"


Da mamaki ta kalle shi


"Kamar ya kurma?"


"Eh mana ai duk mutumin da bashida waya kurma ne."


Dariya ya bata sosai har saida dimful d'inta suka lotsa fararen hak'oranta suka bayyana.


Muhdeen dake tsaye daga tsallakensu gaban access bank yana magana da wani,kamar ance ya juyo kwatsam idanunsa suka sauka kan Inteesar da Usman,tana zaune a gaban motarsa sai dariya take masa harda hak'oranta,want abu ne yaki kamar mashi ya soki zuciyrsa,tunda ya ke bata ta'ba masa dariya ba ko da ita da Gwaggo take dariya da ta ganshi zata had'iye dariyar,amma gata zaune gaban motar wani k'ato tana masa dariya,ransa yakai k'ololuwar 'baci,garan gadan ya nufi tsallakowa titin cikin zafin rai da k'unar zuciya.








Daga alk'amin✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)




Don k'arin bayani


09065327995






Love u oll 😘😍


Comment &,shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89










*INTEESAR*




Story & writing✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)








*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*






*GARGA'DI*


Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.




Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba,arashi ne mai kashe auren wawa.




*JINJINA*


Jinjina ta musamman gare ku masoya na, na yaba kuma nagode da addu'ar da kuke mani Allah yabarmu a tare nayi wannan shafin tukuici ga masoya na na group d'in *INTEESAR HAUSA NOVEL* ina jin dad'in comment da addu'o'i da kuke mani i love you lodi-lodi.




*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*


Page4️⃣6️⃣


Ransa yakai k'ololuwar 'baci gadan gadan ya nufi tsallakowa titin cikin zafin rai da k'unar zuciya,cikin rashin sa'a ga cunkoson ababen hawa sunyi yawa, kasancewar yamma ne kowa na kiciniyar komawa gida.


Kamar ance ta kalli gefenta can ta hangoshi duskarnan tasa a murtuk'e,kuma idonsa na kanta,gaban ta ne ya fad'i dan har sai da hanjin cikinta suka kad'a, cikin tashin hankali ta dubi Usman ta ce,


"Dan Allah mubar wajennan yanzun nan"


Da mamaki ya kalleta


"Lafiya?"


"Ba lafiya kaidai mubar nan yanzun nan"


Cikin sauri ya tara motar suna barin wajen sai ga Muhdeen ya tsallako,kad'an ya rage bai same su ba,cizon yatsarsa yayi cikin takaici da k'unar,don da ya same ta baisan iya abunda zai mata b.


Komawa yayi wajen mutumin da suke magana ya kallesa ya ce,


"Kaga zamu yi magana a waya."


Bai jira cewarsa ba kawai ya shiga motarsa ya tafi,mutumin na masa magana yana tamabayarsa ko lafiya amma ina bai saurare shi ba ya ja motar ya yi tafiyrsa.


Inteesar suna tafiya akan titi sai azalzalar Usman take kan yayi sauri,da taga yabi hanyar gidansu ta ce a'a ba gida zata ba,tayi masa kwatancen inda zai kaita.


"Wai lafiyarki kuwa duk kinbi kin fita hayyacinki wa kika gani ne."


Bata ce komai ba duk da cewar tana dai jinsa ne amma hankalinta baya jikinta.


"To yanzun gidan da zan kaiki gidan waye?"


"Gidan yaya na ne."


Suna isa k'ofar gidan,ko sallama bata tsaya sunyi ba ta fita,da sauri ta tura gate d'in gidan ta shiga, murmushi kawai ya yana kallonta har ta shige sannan ya juya akalar motar yabar k'ofar gidan ba tare da sanin me ya tsoratata ba.


Tana tura gate d'in gidan mai gadin da mai baiwa fulawowi ruwa suna gaishe ta ma bata ji ba,da mamaki suke kallonta ganin yanayin da ta shigo.


Ita kuma idan ta tuna yadda ya murtuk'e fuska ne da wahalarsa da tasha a baya musamman idan ta tuna zafin marukan da ya ta'ba mata kafin suyi aure ne ya ke k'ara saka mata tsoronsa.


Dai-dai kwanar shiga layin gidan Usman na fita yayi gabas,sannan Muhdeen ya fito ta yamma,basu had'u ba.


Da sallama ta shiga cikin falon,ganinta a firgice yasa Gwaggo mi'kewa tare da fad'in


"Lafiya kamar wacce aka jefo?"


"Lafiya lau Gwaggo."


Girgiza kai Gwaggo ta yi tare da cewa


"To me ya firgita ki ne?"


Shiru ta yi tana tunanin ta ina ma zata fara


"Dama dama lokacin da zan tafi gidan rasuwar ne Ishaq Direba naje ya kaini aka ce baya nan 'yarsa ce ko matarsa ce ba lafiya na manta,shine naje na hau ada..."


Bata kai K'arshen zancen ta ba ganin yadda ka turo k'ofa da k'arfi,ganinsa ne kuma ita ya ke kallo tare da nufo inda take yasa ta daka wani tsalle aguje ta shige d'akinta ta murza key,tura k'ofara ya yi yaji ta a ride


"Idan baki bud'e k'ofar nan kin fito kin sanar da ni gidan ubanwa kika je da kuma wanda na ganki gaban motarsa wallahi sai kin tausayawa kanki."


Haka ya dinga dukan k'ofar kamar zai 'balle ta, Gwaggo ce ta k'araso wajen ta ke tamabayarsa.


"Kai Muhammadu lafiyar ka kuwa?kodai ka fara shaye -shaye ne ban sani ba?"


Maganar da tayi masa ne ya basa takaici don haka ya bar wajen ya nufi d'akinsa,don yaga alamar matuk'ar ta tsaya wajen Gwaggo zata iya sawa ya aikata abunda ba shi kenan ba, musamman idan aka ce akan Inteesar ce to fa zata iya 'batawa da koma waye akanta.


Kai tsaye d'akinsa ya nufa,zaciyarsa sai zugi yake masa zama yayi yana tunani,to waye wannan da take zaune a gaban motarsa,sai faman sakin murmushi da dariya take masa da alama taji dad'in kasancewarta da shi,zama ya yi yama nazari ina yasan fuskar wannan Mutumin?don Kan gaskiya ya ta'ba ganinsa a wani wurin,duk da dai yanzun bazai iya tuna inda ya gansa ko ya ta'ba saninsa ba,take sai ya tuno da Usman tabbas shi ya gani a k'ofar gidansu Inteesar suna fira,washe garin da aka sallamota daga Asibiti bayan Mummy da Gwaggo sun saka shi gaba kan tunda baije asibiti dubota ba yaje gidansu,zuwan da yayi ne yaganta tsaye jikin motar Usman shi da ita.


Zuciyarsa ce ta fara tafarfasa wato saurayinta taje wajensa kenan?tayi k'aryar zuwa ta'aziyya yayinda ta tafi wajen saurayinta,bayan ya ce ta nemi Ishaq ya kaita ya dawo da ita amma tak'i amincewa da ya kaita, toilet ya shiga don watsa ruwa.


Inteesar kuwa da taji alamar tafiyar Muhdeen ta kuma ji muryar Gwaggo ne yasa ta bud'e k'ofar,kallonta Gwaggo ta yi tare da cewa


"Me ke faruwa?"


Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta bawa Gwaggo labarin komai,tun zuwanta kiran Ishaq Direba baya nan har yadda ta had'u da Usaman da Khadija suka matsa ta shiga motar har dawowarsu gida bata 'boye mata komai ba.


"To naji me yasa da Direban baya nan baki baki dawo kin sanar da mijinki ba?"


Shiru tayi tare da cewa


"Bakomai Gwaggo naga yana da uzuri kuma ba lallai ya dawo a lokacin ba shiyasa na tafi,kuma wallahi Khadija ta matsa kan na shigo shiyasa na shiga motar."


Zuba Mata ido Gwaggo ta yi tare da tuna yadda Muhdeen ya bi ya damu da bak'in ciki ta shiga motar wani, murmushi ta sake a zuciyarta tana cewa kenan ya fara sonta ne tunda har yake kishinta murmushi ta yi tare da hamdala a zuciyarta.


Daga nan suka nufi kitchen tare dan d'ora abincin dare .


Daga can d'akinsa kuwa bayan ya fito wanka ya shirya ne wayarsa ta fara ruri,d'auka yayi tare da sallama,maimako a amsa sallamar sai jin kukanta yayi a cikin dodon kunnensa.


"Haba my baby me kuma ya faru daga kiran waya sai kuka."


"Haba tambaya ta ma kake?ya zun yaushe rabon da muyi waya?da kullun safiya sai ka kirani idan ka tashi daga barci amma yanzun shiru,kamar ma ka mance da ni ko?"


Ta k'ara sautin kulanta lokacin da takai k'arshen zancen,Wanda har Mum d'inta sai da ta shigo d'akin da sauri Jin kukan Sumayya,bayan shigwarta ne taga waya take da Muhdeen yasa taja tsuki ta fita,don lamarin Sumayya yanzun takaici yake bata.


"Kinga dain kukar nan haka please,ta yaya za'a ce na manta dake?ai idan na manta ki to nima zan iya mance kaina kenan."


Tsagaita kukan tayi ta ce,


"To kwana nawa kenan baka kira ni ba? sai dai ni na Kira ka kuma yadda muke dad'ewa muyi fira yanzun mun daina da mun fara zaka nuna gajiyawarka da ni wallahi hak'uri na ya fara k'arewa,wai yaushe wannan zaman nawa ya k'are?"


"Ya kusa saura sati biyi fah ba nisa mai Happiness."


"Kai a wajenka ne da nisa amma Ni waje na kmar nan da 2 years nake gani,ji nake kamar na janyo ranar tazo yau."


Murmushi yayi tare da cewa


"Ba zaki gane bane wallahi da kinsan halin da nake ciki na rashinki da kin tausaya mani wallahi,hak'urin zaman nake Dan ba yadda zanyi ne amma wallahi I missed you so much."


Sun jima suna fira kafin suka yi sallama


Da misalin k'arfe sha d'aya na dare ne Inteesar tana zaune akan gadonta, Gwaggo na falo tana kallon T.V shi kuma Muhdeen na d'akinsa,tunani take yanzun idan ta kwanta nan Gwaggo na zuwa zata tayar da ita sai taje d'akin Muhdeen dole,ita kuma tsoron zuwa take saboda laifin da tayi masa,tun lokacin da ya dawo ta shige d'akinta ta rufe ya buga bata bud'e ba,tun lokacin bata yarda ta had'u dashi ba sai a dinning table,kuma ta lura da irin kallon da yake mata,alamun yau idan kika shiga hannuna mai k'watarki sai Allah,tasan sarai bazai kyaleta ba yadda yadda taga ransa ya 'baci,bata gama tunaninba sai ga Gwaggo ta shigo da sallama


"Ke 'yar albarka me kike har yanzun baki tafi ba?"


"Wallahi Gwaggo tsoro nake ji."


Bata kI K'arshen maganar ba Gwaggo ta ce


"Sai da fafe Allah tashemu lafiya."


Gabnta na tsananta fad'uwa saboda tsoro,haka ta nufi bakin k'ofar tare da tunani da zullumin abunda zai biyo baya.




*KUYI HAK'URI DA WANNA WAYA TA CE TA SAMU MATSALA*






Daga alk'amin✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
(Manan ihsa)




Don k'arin bayani


09065327995




Love u oll😍😘Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89








*INTEESAR*




Story & writing by ✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)










*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*






*GARGA'DI*


Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.






Wannan kagaggen labari ne banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ki hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba,arashi ne mai kashe auren wawa.






*JINJINA*


Jinjina ta musamman gare ku masoya na,na yaba kuma nagode da addu'ar da kuke mani Allah yabarmu a tare nayi wannan sharin tukuici ga masoyana na group d'in *INTEESAR* *HAUSA* *NOVEL* *GROUP* Ina jin dad'in comment da addu'o'i da kuke mani I love you lodi-lodi.




*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*


Page4️⃣7️⃣


___________Gabanta ne ya tsananta fad'uwa saboda tsoro, haka ta nufi bakin k'ofar tare da tunani da zullumin abunda zai biyo baya.


Tsaye tayi a falon kusan mintuna goma, ta rasa yadda zatayi, zuwa can sai ta tuna da d'aya daga cikin d'akunan dake nan cikin falonta, wato d'akin da aka gyara shima aka zuba mata furnitures komai na d'aki, don haka ciki ta shiga tayi kwanciyarta bisa godon bayan ta karkad'e gadon.


Shi kuma Yana can d'akinsa ya gama shirinsa na kwanciya barci, zama yayi Yana jiran shigowarta don yasan tabbas Gwaggo ba zata barta ta kwana a can ba sai ta turo masa ita, sanin hakan ne yasa ya zauna zaman jiranta.


Ganin har k'arfe goma sha biyun dare shiru ne yasa ya fara tunanin anya lafiya kuwa har yanzun bata shigo ba, mi'kewa yayi ya don shi a tunaninsa kila Gwaggo tana falo barci ya d'auketa ne bata san Inteesar na d'aki ba.


Yana zuwa falo yaga ba kowa don haka ya nufi dakin, ganin alamar cewa hasken d'akin a kashe yake alamun sunyi barci, tambayar kansa yayi mene ne dalilin da yasa Gwaggo zata barta ta kwana da ita?gaskiya bata kyauta masa ba haka nan ransa ba dad'i ya koma d'akinsa ya kwanta, duk da cewar ta 'bata masa rai amma hakan bai hana shi jin kewarta ba, ko ba komai yana jin motsin mutum a cikin d'akin.




Kwance take a d'akinta tana danne-danne a waya, Jabeer ne ya fito daga bedroom da alama wanka yayi, kallonsa tayi tare da cewa


"Ya maganar da mukayi da kai ne na cewa gobe zaka kaini gidan Muhdeen."


Murmushi yayi tare da cewa


"Maryam kenan ki bari sai wani jik'on, don gobe da sassafe zanbar gidan nan."


"Nifa na kula da kai kamar baka son zuwa ka kaini, sau biyu ina maka magana kana kawo mani uzuri."


"Ba haka bane duk lokacin da nake da uzuri shine kike magana."


"Ina son ne na tabbatar da gaskiyar abunda naji."


Kallon mamaki ya mata sannan ya ce,


"Me kike son ki tabbatar a gidan nasa?"


Murmushi tayi


"Naji ance budurwarka ya aura?"


Nuna k'irjinsa yayi da yatsarsa manuniya


"Ni kuma?waye ya ce maki budurwa ta ce Inteesar?"


"Ba wanda ya fad'a mani,amma ni nasan abunda nakeyi."


"To hasashenki ba gaskiya bane ban ta'ba soyayya da Inteesar ba."


Dariya tayi


"Ko da ace baka ta'ba soyayya da ita ba ni nasan kana sonta,na kalli yadda ka dinga rawan jiki da ita likacin auren Muhdeen na farko,sannan lokacin da ka kawota gidan nan kuka siyo mani agwaluma naga tsantsar soyayyarta a cikin idanunka da irin kallon da kake mata,bayan haka nasaha kamaka kana kallon photonta lokuta da dama,sannan ranar da Muhdeen ke sanar da kai cewa Inteesar aka aura masa bayan dawowarka gida naga yanayinka ya canza sosai ka shiga damuwa da yawan tunani."


Shiru yayi yana sauraranta, don yasa duk abinda ta fad'a gaskiya ne, don haka daga nan bai sake cewa komai ba do baida ta cewa yanzun sai ta samu abun fad'a,don haka ya share ta kamar baiji maganar da take fad'a ba.


"Kuma nikam gaskiya naji dad'in auren Inteesar da Muhdeen,domin kuwa ko ba komai hankali na ya kwanta,don gaskiya tunda na fahimci cewa kana sonta hankili na ya tashi miatuk'a ban dai nuna maka bane, amma lokacin da naji labarin abokinka kuma d'an uwa a gare ka ne ya aureta sai hankali na ya kwanta.


Ta k'arasa maganar tana dariya,ido ya zuba mata yana nazari,tabbas abunda ta fad'a gaskiya ne shima ya san da haka.


"Allah ya kaimu goben zan kaiki."


Murmushi tayi tare da cewa


"Ameen ya rabbi"


Da misalin 'karfe biyar na yamma ne ta farka daga barcin da tayi, toilet ta shiga ta d'auro alwala hijabin da ke jikinta ne tasa taji k'arar k'ofar gate alamun an bu'de za'a fita,matsawa tayi kusa da window ta d'an zuge labaulen window ta lek'a,hangosa tayi sanye da farar jallabiya ya fita zuwa masallaci,a zuciyarta ta ce


"Nikan nan na samu wurin kwana har Gwaggo ta wuce sannan na koma d'aki na."


Matsawa tayi ta shinfid'a sallaya ta tayar da sallah.


Gwaggo ma haka ne daga 'bangaren ta sallah take,don ita a zatonta Inteesar na can d'akin Muhdeen kamar yadda ta tura ta.


Da misalin k'arfe shida na safe ne ta fito daga d'akin ta nufi d'akinta,da sallamata a bakinta ta shiga, Gwaggo na kwance akan gado bayan ta amsa sallamar, Inteesar ce ta k'araso cikin d'akin ta durk'usa ta ce,


"Gwaggo ina kwanana?"


"Lafiya lumui 'yar albarka kin tashi lafiya?"


"Lafiya qalau Gwaggo."


"To ya kwanan mijin naki?"


"Yana lafiya lau"


Kai Gwaggo ta jinjina tare da cewa


"Masha Allahu,Allah yayi maku albarka ya azurta ku da samum yara masu albarka."


Tura baki Inteesar tayi tare da cewa a cikin zuciyarta


"Ya dai azurtashi da matarsa Sumayya."mi'kewa tayi don fara aikace -aikacen gidan kamar yadda ta Saba kowace rana


Bayan ta gama komai ne amma bata gyara masa d'aiksa ba,don tasan yana ciki,kuma ba zata iya shiga yana ciki ba don tasan kila har yau bai huce ba.


Kitchen ta nufa don ta girka masu breakfast.
Bayan ta gama had'a breakfast d'in ne inda ta dama kunun gyad'a sannan ta soya k'osai,sai Indomie da ta dafa yare da dafaffen k'wai.


Fitowa yayi daga cikin d'akinsa ya nufi d'akinta don zuwa gaida Gwaggo,da sallama ya tare da tura k'ofar ya shiga, Gwaggo dake kwance ne ta mik'e ta zauna tare da amsa sallama r


"Barka da safiya Gwaggo"


"Yauwa barka dai ya kwanan iyali?"


Shiru yayi yana kallonta don shi dai kam baima sakasa a idonsa ba ballantana yasan ya ta kwana.yana son ya ma Gwaggo tamabaya shin ya akayi ne tabar Inteesar ta kwana tare da ita,bayan yasan cewa bata ta'ba barin ta kwana amma yau ta barta,sai dai yabar zancen kan cewa kila Gwaggo tabarta ne ta kwana tare da ita saboda ganin yadda ransa ya 'baci har yana Shirin dukanta ne yasa ta barta,don bata son abunda zai 'bata mata rai.


Daga nan sai ga Inteesar ta gama ayyukan da zata yi ta shigo,ido ya zuba mata ganin da fara'arta ta shigo amma tana kallonsa sai ta had'e fuska,kamar wacce bata ta'ba dariya ba a rayuwarta,tuna yadda yadda ganta a cikin mota da Usman tana ta masa dariya sosai,amma shi da ta gansa zata had'e fuska kamar taga mala'ikar d'aukar rai, jinjina kai yayi tare da maganar zuci tabbas sai yayi maganin yarinyar nan,badai tana tak'ama da Gwaggo bane nan zata tafi ta barshi da ita sai yayi maganinta.


"Gwaggo ga breakfast can a dinning table na kammala."


Jinjina kai Gwaggo tayi


"To 'yar albarka sannu da aiki."


Murmushi kawai tayi ta ce


"Yauwa Gwaggo"


"To kundai san bana da juriyar yunwa,to don haka ku muje muci da wuri ."


"Ta'be baki Inteesar tayi tare da cewa


"Gwaggo don Allah kuje ku fara ci,ni sai nayi wanka zanci kuma ba na Jin yunwa "


"Ke kenan kowane rana sai anyi

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads