Showing 81001 words to 84000 words out of 149432 words
Chapter 28 - INTEESAR Book Complete by Zainab Abdullahi.txt
k'aton banza dakai k'aramar yarinya ka kasa yadda zaka shawo kanta,kalli yadda ka koma a dare d'aya lusari kawai, sai Kai ta zama a haka tunda ba zaka fad'a mani damuwarba ballantana na shawo maka kanta, idan kaga dama ka tashi kayi kalaci."
Daga nan ta fice daga dak'in, binta kawai yayi da kallo har ta fice bai tanka mata ba.
A falo ta samu Inteesar zaune akan kujera, ta tsaya tsaye a kanta ta fara magana.
"Ke kuma na dawo kanki, me aka kawo ki kiyi a gidannan?
Cikin rashin fahimtar inda zancenta ya dosa ta ce,
"Kiyi hak'uri Gwaggo ban gane inda zancenki ya dosa ba."
"Zaki ce haka mana, to bari kiji ba'a kawo ki nan gidan da kici kisha ki kwanta ba, don idan dan abinci ne gidan iyayenki kina ci, idan sha ne a gidan iyayenki kina sha haka sutura ma, ko ba haka ba?"
"Hakane"
"To wani abu ne wanda ya zama bak'o a wajenki dole sai a gidan miji ake yinsa?"
Shiru tayi tana nazari kafin ta ce,
"Wallahi ni Gwaggo bansan inda zancenki ya dosa ba, ban gane me kike nufi ba."
"Dan k'aniyarka baki san hakkin miji akan matarsa ba? Ko baki san ki biyawa mijinki buk'atarsa ba ne? kin fi son ki kwana cikin tsinuwar mala'ikun Allah? to bari kiji duk ranar da na sake ganin makamancin hakan ya faru dake da mijinki wallahi ranar zaki ga 'bacin raina, daga nan bata sake magana ba ta nufi dinning area, Inteesar mi'kewa tayi cikin sanyin jiki ta bi bayanta, zuba mata nata tayi dai-dai lokacin Muhdeen ya k'araso, k'amshin turarensa ne ya sanar da ita k'arasowarsa, zama yayi d'aya daga cikin kujerun dinning d'in yayin da ita kuma ta zuba masa nasa, k'ok'arin barin wajen tayi sai taji muryar Gwaggo tana cewa
"Ina zaki je baki ci komai ba?"
Tsayawa tayi ba tare da ta juyo ba ta ce,
"Bana jin yunwa"
"Shikenen ke kika sani, idan ma fad'a da na maki ne kike fushi dani, ban damu ba kuma matuk'ar baki sauya ba to ba ruwa na dake."
Daga nan Inteesar d'akunsa ta nufa dan gyara masa,dama irin wannan lokacin take jira, idan baya ciki ta shiga ta gyara har ta fito ma bai sani ba.
A daren ranar ma haka Gwaggo ta sanya Inteesar ta shirya cikin wasu kayan barci masu kyau, har da k'ara ja mata kunne akan kar ta sake gudun mijinta, ita dai Inteesar bata ce komai ba sai da safe tayiwa Gwaggon ta fita.
Tsayawa tayi a falo tana ta sak'e-sak'e matuk'ar ta ce zata tafi d'akinsa ba makawa sai yayi abunda ya ce zaiyi da ita, ita kuma bata k'aunar haka ta faru da ita,don haka ta ce ba zata tafi d'akin ba ballantana ace ya cutar da ita, d'akin da ta kwana shekaranjiya nan ta tafi ta kwanta.
Shima a 'bangarensa bayan ya gama shirinsa na kwanciya barci zama yayi a bakin gadon ba abunda yake sai tunanin yarinyar nan, ya kasa gane gaskiya shin son ta yake ko me? shidai a iya saninsa ya tsani yarinyar ada ko son ganinta baya yi, amma a yanzun baya jin tsanarta a cikin zuciyarsa kamar yadda yake ji ada, kuma shi haryanzun baya jin yana sonta, sai dai abu d'aya ne yake basa mamaki wanda kuma ya kasa gane dalili, shine a duk lokacin da ya kad'aice shi da ita a cikin d'aki d'aya sai yaji gaba d'aya sha'awar kasancewarsa da yarinyar yake ji,ko kallonta yayi sai yaji wani yanayi na buk'atuwa musamman idan ya kalli wani sashe na jikinta sai yaji feelings ya taso masa, ga Sumayya matarsa da sukayi auren soyayya da ita Sumayya idan zata kwanta tsirara a gabansa zai iya tsallake ta ya wuce ba tare da yaji wani abu dangane da haka ba, amma idan Inteesar ce ko yaya ya kalli wani sashe na jikinta sai ya rasa nutsuwarsa,koda Gwaggo ke turo ta d'akinsa baida niyyar ta'ba koda yatsarta, amma da zaran ya ganta sai ta nemi wargaza masa lissafi, shiyasa ba ya iya hak'uri sai ya ta'ba ta, idan kuma ba haka ba shine yake shan wahala don sai ya kwana yana ciwon mara, shiyasa ya fad'a mata duk ranar da ta shigo masa d'aki sai ya biya buk'ararsa.
Kwanciya yayi yana ta juyi shi kad'ai, zuciyarsa sai tunaninta yake,a wannan lokacin ita Kam ta dad'e da barci.
*LONDON*
Dad da Mum d'inta suna zaune a falo, ta fito daga bedroom d'inta ta tsaya k'erere akansu.
"Dad Mum gobe zan koma gidan miji na"
Da mamaki Dad ya kalle ta
"Akan me zaki koma gidansa? mutumin da tunda kika taho bai saka k'afa yazo ba shine zaki koma gidansa? bayan kinsan cewa danginsa da kakarsa ba k'aunarki suke ba kiyi zamanki anan, bana son kije inda za'a wulak'anta mani ke alhalin kinfi k'arfin wulak'anci."
Murmushi tayi tare da cewa
"Kada ka damu Dad mijina yana sona, shi kad'ai ma ya ishe ni ban damu da kowa yak'ini ba, sannan wannan kakar tasa ba zamu zauna inuwa d'aya da ita ba, tun farko bata sona, sannan muna tsaka da cin amarcinmu ta sa akayi mani kishiya, hmm bashi ta d'auka tasa nayi nesa da miji na tsawon wata d'aya, yanzun haka tana cikin gidan ita da 'yar lelenta wacce ta aura masa Inteesar take ko wace ce? oho masu amma bazan sauka a gidan ba sai nan da 1 week da zaran ta bar gidan ni kuma zan koma gida na yayin da zan k'untatawa rayuwar Inteesar, wallahi sai tayi nadamar auren miji na."
Sai a lokacin Mum tayi magana ta ce,
"Aure dai sun riga sun masa,kuma suna k'aunarta fiye da ke, saboda haka kada kije ki aikata abunda zaisa kiyi dana sani bada yawu na ba."
"Hmm ita ce da dana sani bani ba sannan kuma kada ma kiyi yawu Mum, don na lura yanzun baki k'aunata kamar kin janza hali ba Mum d'in da na Sani da ba, kuma wallahi da bakinsa ya fad'a mani cewar ba son yarinyar yake ba, ya tsane ta kada na d'auke ta kishiya na d'auka cewa 'yar aiki aka kawo mani,ita zata dinga mani aiki, shine dalilin da yasa na hak'ura na janye k'udiri na akanta, da badon haka ba da sai na illata ta."
Dad ne yayi ajiyar zuciya ya ce
"Yanzun ke kad'ai zaki koma daughter?"
"Lokacin da nazo ni kad'ai nazo ba tare da kowa ba kuma ra'ayin kaina ne, to yanzun ma ni kad'ai zan koma dan ra'ayin kaina."
Tana gama fad'ar haka ta juya ta koma, da ido kawai suka bita don idan ta fad'i magana ba ta sauraron kowa.
Washe gari da safe dukkansu suna Kan dinning table suna breakfast, Muhdeen ne ya kalli Gwaggo tare da cewa
"Gwaggo zan d'anyi wata tafiya ta kwana biyu, so zaku ji shiru baku ganni ba."
Gwaggo ne ta ajiye kofin tea da take sha yayin da Inteesar kuma tayi shiru kamar bata ji ba,inda Gwaggo ta ce,
"Wani gari zaka?"
"Birnin tarayya zanje?"
"To Allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya, wani lokaci zaka tafi?"
"Yanzun idan na fita zuwa asibiti daga can bazan dawo nan ba,sai bayan kwana biyu na dawo."
"To Allah ya tsare ka ya kaika lafiya ya dawo muna da kai lafiya."
Ameen ta rabbi kaka ta, Gwaggo ce ta kalli Inteesar ta ce,
"Baki ce komai ba kodai kunyi sallama jiya dadare ne."
Cikin sanyin murya ta ce,
"Allah ya kiyaye hanya"
Ta'be baki yayi don har yau yana jin zafin maganar da tayi masa inda yake ce mata zai mutu ta ce masa idan ya mutu kwanansa ne suka k'are,wato k'iyayyar da take masa har ya kai haka?idan ya tuna zancenta kawai sai yaji ransa ya 'baci.
Gwaggo ce ta katse masa tunani ta hanyar cewa
"Lafiya kuwa ko akwai abunda yake damunka ne?"
"Kai ya girgiza tare da murmushin yak'e yace,
"Bakomai Gwaggo, bari na tafi"
Daga nan ya nufi falo Kan kujera ya d'auki k'aramar jakarsa ya rataya a kafad'arsa,daga nan ya juyo ya kalli Gwaggo da take d'aga masa hannu.
"Ke 'yar albarka ba zaki zi ki raka mijinki ba?"
Bai kula su ba ya nufi hanyar fita, Inteesar tabi bayansa saboda maganar da Gwaggo tayi mata,yayin da Gwaggo ta zauna a kujeran falo.
Yana gaba tana biye dashi a bayansa, yana jin k'arar takun takalminta,bai juyo ba kuma bai tsaya ba, har suka k'arasa wajen motorsa ,yana shiga yayiwa motar key yabarta nan tsaye a wajen ko kallonta bai yi ba.
Ita kuma taji zafin share ta da yayi don haka ta juya ta koma ciki.
A asibiti ma ya sanar da cewa zaiyi tafiya zuwa Abuja,duk da cewar Jabeer d'an uwansa ne kuma amininsa bazai iya fad'a masa gaskiyar inda zai je ba, shiyasa Koda Jabeer ya tambaye shi ya ce Dady ne ya aike sa.
Bayan yabar asibiti hotel ya je ya kama masu d'aki na tsawon kwanaki bakwai, shida Sumayyarsa,isowarta kawai yake jira yaje Airport ya d'auko ta.
Da misalin k'arfe d'aya na rana bayan ya idar da salla ne ya nufi Airport d'auko ta.
Akan hanyarsu ta zuwa Hotel ne yana Driving ya d'an juyo ya kalleta
"Ya su Dad da Mum duk suna lafiya?"
Murmushi tayi tare da cewa
"Lafiya lau suke suna gaishe ka"
"Shine kika tafi kika nisanta kanki da ni ba tare da kinyi tunanin halin da zan shiga ba ko"
Yamutse fuska tayi
"Baby mubar maganar nan kawai, dan wallahi zaka sa na tuno da abunda nake k'ok'arin cire shi a Raina."
"To shikenan tunda bakiso na bari"
Hirarsu suke har suka k'arasa Hotel d'in, inda sukayi order na abincin da suke so, ta shiga wanka,bayan ta fito ta shirya ta zauna gefensa, kallonta yayi tare da cewa
"Banga kinyi sallah ba? Kada dai kice mani fashin sallah kike ki sakani cikin wani hali."
Dariya tayi sannan ta ce
"Ba fashin sallah da nake."
Murmushi yayi tare da cewa
"Alhamdulillah, to banga kin tashi kinyi sallah ba."
Yamutse fuska tayi
"Sai anjima zan had'a da la'asar nayi gaba d'aya."
Dafe goshinsa yayi
"Sumayya wai har yanzun baki daina jinkirta sallah ba?"
"Shikenan bari na tashi nayi"
Mi'kewa tayi ta nufi toilet don d'auro alwala,binta da ido kawai yayi ya ce,
Allah ya shirya
Tsawon kwanaki biyu yana tare da Sumayya,idan ba lokacin sallah ba ba abunda ke fitar dashi daga Hotel d'in, kullun sai yayi waya da Gwaggo da su Mummy ba Wanda yasan ba Abuja yake ba,kowa ya d'auka yana Abuja, a ranar ne kuma Sumayya ta ce ta gaji da zaman Hotel d'in,tana son su d'an fita, haka kuwa akayi suka fita suka d'an shak'ata, a kan hanyarsu ta komawa Hotel d'inne dai-dai kwanar da zasu shiga Jabeer yazo wucewa ya hanto Muhdeen da mace a gaban Motarsa,da mamaki ya tsaya yana kallonsa har suka shige,sannan yaja motarsa ya wuce cike da mamaki.
Bayan ya koma gida yana zaune a falo ya ciro wayarsa layin Muhdeen ya kira, Muhdeen da yake zaune a kujera Sumayya tayi folo da cinyarsa wayarsa ta soma ruri dubawa yayi tare da d'aga wayar.
"Hello Jabeer ya akayi ne?"
Ajiyar zuciya Jabeer ya sauke tare da cewa
"Kana ina ne?"
"Ya kake tambaya ta bayan kasan na tafi Abuja"
"Me kaje yi a Abuja?"
"Saunawa zan sanar dakai Dady ya saka ni wani aiki"
"Shi aikin baida suna ne ko kuma na kira Dady na tambaye shi wani aiki kake masa, nasan dai bazai 'boye mani ba."
Cikin d'aga murya Muhdeen ya ce,
"Bai shafeka ba, kada ka shiga hurumin da ba naka ba"
"Bansan yaushe ka zama haka ba, amma bari yanzun nan naje gidanka na d'auko Gwaggo sannan na biya na d'auko Mummy sai na kawo su ka fad'a masu aikin da kakeyiwa Dady wanda su bazasu iya sani ba."
"Ka kawo su Ina?"
"Safara Hotel, inda ka ajiye mace da sunan kana Abuja."
A zabure mi'ke tsaye Sumayya dake kwance saman cinyarsa har ta fad'i.
Daga alk'amin✍️
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09055327995
Loveu oll😍😘
Comment & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by✍️
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_
*Alk’alaminmu ‘yancinmu*
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.
Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubutashi dan cinzarafi ga kowa ba,idan suna ki hali yazo d'aya to a gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba,arashi ne mai kashe auren wawa.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page5️⃣0️⃣
A zabure ya mi'ke tsaye, Sumayya dake kwance saman cinyarsa har ta fad'i.
"Look Jabeer ba yadda kake tunani bane, kasan waye ni bazan ta'ba aikata abunda ya kaucewa shari'a ba, duk abunda kaga nayi to bai kauce, hanya ba."
"To wace ce ka ajiye a Hotel tsawon kwanaki biyu?"
"Mata ta ce"
"Wace matarka.?"
"Sumayya ce,kasan akwai takun sak'a tsakaninta da Gwaggo kuma zamansu waje d'aya akwai matsala, hakan yasa na ajiye ta anan har zuwa ranar da Gwaggo zata bar gidan."
Ajiyar zuciya Jabeer ya sauke tare da cewa
"Idan 'bera nada sata daddawa nada wari, haka zalika idan anbi ta 'barawo abi ta mabi sawu."
"Kaga ba wani zancen Hausa zaka tsaya kana mani ba, maganar gaskiya Gwaggo ta tsanar mani mata ne kawai,ba gaire ba dalili."
"Itama matar taka harda halinta yasa aka tsane ta, kaima kasan matarka nada matsala."
"Ni banga matsalarta ba, kaga sai anjima."
Daga nan ya katse kiran, don baya son Sumayya taji maganar da sukeyi.
Washe garin ranar ne ya sanar da Sumayya cewa zai koma gidansa, don dama kwana biyu ya ce zai yi, kullun da safe kafin ya tafi Asibiti zai je, ya duba ta, kafin ya tafi Asibiti, kuma idan ya tashi kafin yaje gida zai biyo wajenta.
Haka dai ta hak'ura badon ranta yaso ba, shi kuma ya nufi gidansa akan hanya ya tsaya harda 'yar tsaraba ya siye ya tafi dasu gidan, a harabar gidan yaga motar Jabeer yayi parking a gefe, sai da gabanasa ya fad'i don kada Jabeer dai abunda ya ce zaiyi shi yake k'ok'arin yi, don ga motarsa nan a gidan hakan na nufin yazo d'aukar Gwaggo ne ya kaita Hotel inda yake tare da Sumayya? tambayar mai gadin gidan yayi yaushe Jabeer yazo gidan? ya sanar da shi cewa yanzun.
'Daya daga cikin ma'aikatan gidan ya kira, yasa shi ya d'auki ledojin tsarabar da ya dawo dasu,fruit ne da kayan ciye-ciye danginsu chocolate cake da snacks.
Tsawon mintuna biyu yana tsaye yana tunani idan Jabeer ya sanar da Gwaggo gaskiyar lamarin ya zaiyi, shidai yasan tijarar Gwaggo, duk da cewar matarsa ya ajiye a Hotel ba karuwa ba.
Da haka ya nufi hanyar shiga ta cikin falon,da Sallama ya d'auke a bakinsa ya tura k'ofar, Gwaggo da Jabeer ne suka amsa masa yayin da Inteesar ke kwance a k'afar Gwaggo,tana barci, Duk gashin kanta mai tsayi da bak'i ya bazu ya rufe mata rabin fuskarta, sanye take wata k'aramar riga mara hannu mai kama da singileti pinck colour sai siketa bak'i har k'asa,rigar ya kwanta a jikinta kuma ya kama jikinta,hakan yasa ya bayyana surar k'irjinta,ta kwanta rigingine kanta na saman cinyarsa Gwaggo, ta d'ora hannunta na dama a saman cikinta,barcinta kawai take yi, bayan sun amsa masa sallamar ne ya gaida Gwaggo.
"Barka da yammaci Gwaggo."
Shiru tayi masa kamar bata ji abunda ya ce ba,kauda kanta tayi tana Mai cigaba da kallon T.V da take, gabansa ne ya fad'i kar dai a ce Jabeer ne yayi masa tonon silili, aiko indai haka ne Jabeer bai kyauta masa ba, kuma sai ya ci mutuncinsa, dubansa ya maida ga Jabeer dake zaune shima ya zuba masa ido tare da d'aga
Masa gira d'aya ya dai? kauda kansa yayi daga kallon Jabeer d'in, ya maida zuwa ga Gwaggo ya k'ara cewa
"Ina wuni Gwaggo?"
"Da ban wuni ba zaka ganni?"
Shiru yayi yana kallon Jabeer, yayinda shi kuma Jabeer ke masa murmushi ya ce,
"Da alama kayi mata lafi ne"
"Nayi mata laifi ko kuma kayi mani munafurci ko?"
Sanin inda zancensa ya dosa ne yasa Jabeer shek'ewa da dariya ya ce,
"Kasan baka da gaskiya ne shiyasa ka tsargu kanka, ni ba abunda na sanar da Gwaggo, amma wata k'ila dai zan sanar da ita, ka Fara bincikar laifin da kayi mata tukunna."
Gwaggo ce ta kalli Jabeer ta ce,
"Ka rabu dashi Jabeeru, ba wani bincikar da zaiyi ya sani ai,tunda yasa k'afarsa ya tafi Abuja sau d'aya ya kira mu bayan saukarsa, ga matarsa nan koda sau d'aya bai tambayi halin da take ciki ba."
Sai a lokacin Muhdeen ya kula da irin kayan dake jikin Inteesar, bayan ga Jabeer a wajen zaune sun facing da juna, ransa ne ya 'baci ya fara magana
"Wannan wane irin isakanci ne kuma?"
Da mamaki Gwaggo ta kalle shi tare da nuna shi da yatsa ta ce,
"Kai Muhammadu ka kiyaye ni ka fita a ido na,gidan uwar wa ake isakancin?"
"Haba Gwaggo kema kinsan ko a addinin musulunci wannan ba dai-dai bane, ta yaya matar aure zata tsaya ta kwanta gaban wani namiji da ba muharraminta ba haka,kalli fa ko suturar arziki bata saka ba,ga gashin kanta a waje ki hula bata m saka ba, ga wata 'yar isakar rigar da ko hannu babu."
K'arasawa yayi gabansu ya d'an ja gashin kanta da d'an k'arfi, k'ara ta saki tare da tashi zaune tana mutstsika idanu alamun barcin bai ishera ba,ido ta zubawa Gwaggo don Bata lura da shi ba,tura baki tayi tare da ri'ke kanta ta ce
"Gwaggo akwai zafi."
"Daina Kallo na ga shugaban mugayen nan da yaja maki gashi, saboda mugunta irin taka, dama ina jiran dawowarka ne idan baka sani ba ka sani, tunda ka saka k'afa ka tafi Abuja ka kirani sau d'aya baka sake kira ba, sannan wayar Inteesar da ka amshe ka maida mata da wayarta kaji na fad'a maka."
Dariya Jabeer yayi tare da cewa
"Au dama Abuja ya tafi Gwaggo?"
Kallonsa Gwaggo tayi tare da cewa,
"Ya kake tambaya ta bayan ya ce, daga wajen aiki ne tafiyar ta tashi kuma naga wajen aikinku d'aya, shine baka san ya je Abuja ba?"
Dariya Jabeer yayi
"Wato mutumi na Abuja kaje ko? to me kaje yi ne dan bansan aikin da kaje yi ba,sannan kaga kamar ba Wanda yayi dogon tafiya ba, Abujan ce kuwa ko dai fad'a ne kawai."
Banza da shi yayi dama yasan halin Jabeer da tsokana, kuma yana da tabbacin cewa Jabeer bazai ta'ba tona masa asiri ba, don haka ya maida idonsa ga Inteesar ya ce,
"Saboda tsabar wulak'anci shine kika Sanya wannan banzayen kayan a jikinki ko? sannan kika zo kika tsaya gashin kanki a bud'e kika tsaya