Header Ads
Showing 3001 words to 6000 words out of 149432 words

Chapter 2 - INTEESAR Book Complete by Zainab Abdullahi.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

1393

Ads at the middle of Article

huta"


"To son a huta gajiya sai ka fito."


Mufida ce ta ce


"Yaya tsaraba ta fa?"


Murmushi yayi tare da cewa


"anjima idan na huta sai na fito maku da tsarabar ku"


Kai tsaye ya nufi hanyar part din sa da sauri Inteesar ta sunkuyar da Kai k'asa Don bata San sake kallon sa,sai da ya wuce sannan ta daga Kai.


Bayan mummy sun kammala cin Abincin ne Mufida ta kwashe abubuwan da suka Bata ta nufi kichen, Inteesar ta goge wajen ta nufi kitchen dan wanke kwanika da sukayi amfani dashi, Mufida dama dakinta ta wuce, Mummy ce ke zaune a falo tana kallon news,
bayan Inteesar ta gama ta fito dai-dai lokacin wayar dake kan dinning ya fara ruri, Mummy ta juya ta kalli wayar tare da cewa


"Inteesar Dan Allah d'auki wayar nan na Son kikai masa Ina ganin ya mance da ita ne"


Rass gaban ta ya fad'i Jin abunda Mummy tace,ba yadda ta iya haka dole ta karasa ta dauki wayar da haryanzun take ruri sunan da ta gani a wayar shine my happiness,
Azuciyar ta ta ce budurwar sa ce ke kiransa cikin fad'uwar gaba ta nufi part d'insa tayi knocking sau uku taji shiru sai tayi tunanin ko barci yakeyi,don haka da sallama ta murda handle din k'ofar ta shiga,ba kowa sai kamshin turare dake tashi ta nufi bedside drawer ta Duk'a ta ajiye wayar dai-dai ya fito daga toilet kenan yana daure da towel a k'ugunshi sai karamin towel dayake tsane ruwan kansa juyowar da zatayi taji taci karo da mutum wani razanannen ihu ta saki cikin tsoro...


Daga alk'amin✍️


Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)




Don k'arin bayani


09065327995


Love u oll😍😘Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89




*INTEESAR*


Story & writing by✍️


Zainab Abdullahi
(Maman Ihsan)








*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*








*GARGA'DI*


Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izini na ba.






Wannan kagaggen labari ne,banyi tunanin Rubuta ta Shi Dan cinzarafi ga kowa ba.idan suna ko hali yazo daya,to KU gafarceni bada niyyar yin hakan nayi ba.Arashi Mai kashe Auren Wawa.


*BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM*


Page0️⃣4️⃣




Wani razanannen ihu ta saki tsoro ne ya sa ta fad'a jikin sa ba tare da ta sani ba,cikin hanzari ta kalleshi shi,idon ta ne yayi tozali da kwantaccen gashin kirjin sa da suka kwanta luf a faffad'en kirjin sa da sauri ta runtse ido tare da ja baya cikin tsoron sa, mugun kallo ya watsa mata tare da daka mata tsawa cikin d'aga murya yace,


"Uban waye ya baki izinin shigowa nan har cikin bedroom d'ina?"


Cikin tsananin tsoron sa da takeyi kanta a kasa, ta fara magana cikin in'ina ta ce,


"A'a Dddmma in in mu mm mm mummy ce ta ta tace na kawo maka wayar ka."


Ta karasa maganar tana nuna masa wayar da hannun ta
juyawa yayi ya kalli wayar da ta nuna masa,
Tsawa ta daka Mata tare da numa Mata hanyar kofar fita.
Cikin daga murya yace,


"Get out"


Cikin sauri-sauri gudu-gudu tabar dakin,ya bita da harara tare da karasawa ya rufe kofar da key yace,


"Mayya"


Ya koma cikin d'akin ya karasa gaban dressing mirror ya d'auka lotsion d'in shi ya fara shafawa.


Bangaren Inteesar kuwa yadda ta Fado falon Mummy ne yasa ta daga Kai ta kalle ta sauri.


"Ke lafiyarki kuwa ya haka kamar an koraki"


Girgiza Kai Inteesar tayi ba tare da tace komai ba,sake jin muryar Mummy tayi tana cewa,


"Ko Muhdeen d'in ne ya maki wani abun?"


Kai ta girgiza tare dacewa,


"Babu komai mummy ba korata yayi ba."


Shine kika shigo kamar wacce aka koro?"


Kanta ta sunkuyar cikin sanyin murya ta ce,


"Mummy zan tafi gida"


Mummy ce ta kalle ta tace,
lapiya yau zaki tafi yau da wuri haka?"


Kai ta gyad'a tace


"Eh Mummy bari na tafi dan nasan Umma na jira na."

Murmushi mummy tayi tare da cewa,


"Shikenan ki gaida Mani da umman taki"


Kai tsaye ta nufi hanyar fita Mummy tabita da kallo tana murmushi cike da son yarinyar.


Da sallama ta shiga cikin gidan, Umma da fitowarta kenan daga band'aki rike da bokiti alamun wanka tayi.


"Wa'alaiki Salam Inteesar har kin dawo?"
Murmushi ta k'ak'alo akan fuskar ta ta ce,

"Eh umma nagaji ne shine nace bari na dawo nayi sallah na d'an kwanta


"To shikenan "
Cewar ummin yayinda ta d'auki buta ta zauna a kujerar tsakar gida ta Soma alwala .
Inteesar ma dakin ta ta shiga ta ajiye hijabin ta,ta fito ta dauki buta ta shiga ban daki ta fito yazauna inda umma ta tashi,ta soma yin alwala cikin nutsuwa.


'Bangaren Muhdeen ma fitowa yayi daga part d'in a inda yasamu Mummy zaune ya kalleta yana murmushi.


"Mummy bari naje masallaci ana shirin tada sallah"


Mikewa tayi ta ce,


"Nima bari na tashi adawo lapiya."


Bayan ya dawo daga masallacin ba kowa a Babban falon Kai tsaye part d'insa ya koma don yana son yayi waya da Sumynsa.kwanciya yayi akan gadon tare da daukar wayar say yayi dialing din number ta inda yayi sevin number ta da my happiness.


*LONDON*


kwance take akan lapiyayyen Royal chair,tana sanye cikin wando 3 quarter yallow da farin singilet kanta tayi Karin gashin attached ya zubo har gadon bayan ta,ga faratan ta zaro-zaro anyi masu fixing tare da ahafa masu shinning sai d'aukar ido suke.wayar ta dake hannun ta ta kalla ganin Kira ya shigo cikin tsananin Jin dad'i tayi picking din wayar tare da kaiwa kunne.cikin shagwaba tace,


"Haba my happiness meyasa tun since Ina Kiran ka baka dagawa why"?


Ta kara narkar da murya tare da cewa,
"Kuma Kai baka damu da ka kirani ba,sannan idan ni na kiraka baka picking sai kaga dama"


Murmushi yayi tare da cewa


"Sorry my Sumy ki garface ni bana kusa da wayar ne shiyasa.yanxun ma dawowa na masallaci kenan naga kiranki da kuma sak'on da kika turo."


Dariya tayi cikin Jin dadi tace,


Kaima fa kasan bazan iya jure hours ba tare da naji muryar ka ba."


Cikin Jin dadin yadda Sumayya ke nuna masa so yace,


"Nima haka ne a wuri na
zaro ido tayi tare da cewa

"Ba wani Nan nida zan kiraka sau uku kafin ka kirani sau d'aya.wani lokacin baka dagawa ko kuma idan ka d'aga kace
I'M busy right now but I will call you letter.kuma bazaka Kara Kira ba sai dai idan nice na Kira,
Kai ya girgiza don yasan gaskiya ta fad'a kuma shi idan Yana aiki a Asibiti baya son yawan d'aga waya musamman idan yaga Sumayya ke Kiran sa don yasan dogon fira zasuyi har dai idan Yana tare da patient.


"Kinga nasani amma yanayin aikin da nakeyi ne." Dai-dai nan Mummy ta turo k'ofar d'akin tare da sallama.daga Kai yayi ya kalle ta tare da cewa Sumayya Kinga zamuyi magana anjima."


Ta'ba fuska tayi tace


" meye kuma yanzun?"


Ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa


"Mummy ce ta shigo"


Yamutse fuska tayi ta ce,


"Ohk to Ina gaishe ta."


ta katse wayar.kallon Mummy ya yi Yana murmushi yace


"Sumayya ce tace na gaishe ki"


Gajeren murmushi mummy tayi Wanda iya fatar baki ta tsaya bata Kai zuci ba,don har ga Allah sumayya bata kwanta mata ba tunda taga pictures d'in ta a wayar Muhdeen taji bata kwanta mata ba.


Ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa


"Ina amsawa,kaxo ga Dadyn ku nan ya daw daga mitin d'in da yaje."


Ta juya ta fita mik'ewa ya yi yabi bayan Mummy.






Daga alk'amin✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)




*DOMIN K'ARIN BAYANI*


09065327995






Love u oll😍😘Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89




*INTEESAR*


Story & writing by✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)










*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*






Wannan kagaggen labari ne,ban Rubuta shi Dan cin zarafi kowaba.idan hali ko suna yazo,to KU gafarceni bada niyyar yin hakan nayi.Arashi ne Mai kashe Auren Wawa.




*BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM*




Page0️⃣5️⃣


Mik'ewa yayi ya bi bayan Mummy kai tsaye upstair din suka nufa part d'in Dady,da sallama suka shiga,Daddy dake zauna kan kujera ya daura laptop akan table yana aiki akai,sanye yake cikin farin jallabiya fuskar sa sanye da farin gilashi,d'ago kai yayi tozali da Babban d'ansa mafi soyuwa a gare shi, murmushi yayi tare da amsa sallamar su.


"Mutanen Egypt barka da dawowa."


Muhdeen d'in ma murmushi ya yi tare da k'arasawa ya ya durk'usa ya gaida mahaifin nasa cikin girmamawa.


"Ina wuni Dady?"


Cikin sakin fuska ya amsa masa.
"Lapiya qalau Muhammad ya gajiyan tafiyar?"


Da Alhamdulillah ya amsa tare da zaunawa kan center carpet d'in dake shinfid'e a tsakiyar falon.


Dady ya rufe laptop d'in dake gaban sa ya juya ya kalli Mummy dake zaune a gefen sa ya ce,


"Ina mufida ce?"


"Tana d'akin ta tana barci"


cewar mummy


Maida dubansa wurin muhdeen yayi tare da cewa,


"Muhammad zuwa gobe idan ka huta sai ka leka asibiti ko?
Domin gaskiya aiki yana yiwa Jabeer yawa a asibitin."


Gyad'a Kai yayi alamun gamsuwa tare da cewa


"Dady insha Allah gobe zan koma aiki na"


"To Masha Allah.Allah yayi maka albarka."


Mummy ce ta amsa da Ameen.


Daga nan hira suka d'an taba ,daga bisani ya Mik'e yayi masu sallama sallama ya fice.


*WANE NE DADY*


Asalin sunan sa shine Alhaji Sani shi mutumin Garin kontagora ne dake nan jihar niger.sunan mahaifinsa Alhaji Mahmud da matar sa Hajiya Hauwa.'ya'yan su uku suka haifa,Babban sunan sa Adam sai mai binsa sunan sa Sani, wato mahaifin Muhdeen kenan sai karamar su Maryam,Babban yayan su Adam yana da 'ya'ya biyu Khalil da Jabir,Jabir ne abokin muhdeen.sai Sani wato mahaifin Muhdeen Yana da 'ya'ya uku Muhdeen ne Babba,Asiya ce ta biyu sai ta ukun su Mufida 'yar autar Mummy kenan,Maryam ita ce kanwar Sani wato itace take bin mahaifin Muhdeen d'in.tana da 'ya'ya biyu tunda ta haifi 'yan biyu bata sake haihuwa ba.daga ita sai tagwayenta Azeeza da Azeema,Adam Babban ma'aikacn gwamnati ne Yana zaune a garin Abuja,yayin da Sani wato mahaifin Muhdeen Yana zaune a Babban birnin jihar niger wato Minna kenan, shahararren 'Dan kasuwa ne da yake kasuwanci kasashe daban-daban yayin da yakai wata ziyara a garin Katsina wajen wani a bokin sa Alhaji Hassan,to a garin ya hadu da Fatima wato Mummy mahaifiyar su Muhdeen kenan,Allah ya k'addara auren su inda ta tare a gidan sa dake unguwar Bosso Estate nan garin Minna,har ta haifi yaran ta guda ukuDuk da a yanxun takan ce 'ya'yan ta hudu har da Inteesar wacce a shekaru uku da suka wuce Allah ya hada ta da inteesar.


Shekaru uku baya wata Rana da safe Mummy zataje unguwa direban ta ya dauko ta a mota tsautsayi ya gifta har Direban ya 'Dan kad'e ta da mota ta fadi a k'asa, kasancewar bataji ciwo ba yasa ta Mik'e da sauri yayin da direban da Mummy suka fito suna salati, cikin hanzari Mummy ta k'arasa gare ta ta ri'ke ta ta ce,


"Sannu ko zo mu tafi asibiti"


Inteesar dake sanye da uniform d'in school ta girgizawa Mummy kai cikin sanyin muryarta ta ce,


"Kada ki damu ba abunda ya same ni Ina lafiya,banji ciwo baAllah ya kawo abun da sauk'i"


Take Mummy taji son yarinyar har cikin ranta,shafa kanta tayi ta ce,


"To muje ga chemist can ko magani ya 'Dan baki saboda tsamin jiki."


Girgiza Kai tayi tare da cewa,


"Wlh ba komai kada ki damu."


Kai mummy ta girgiza tare da cewa,


Ina ne gidan KU take?


Kallonta Inteesar tayi ta ce


"Acan bayan layin ne ba nisa."


Mummy tace


" To muje na rakaki gida.."


Dak'yar Inteesar ta yadda ta shiga motar suka karasa har kofar gidan su Inteesar din,da sallama suka shiga Abba dake zaune kan tabarma yana shan Koko da k'osai yayin da Umma ke gefen shi zaune,tozali sukayi da Hajiya Fatima kamilalliyar mace mai kwarjini,Ummace ta Mi'ke ta d'auko tabarma daga d'aki ta shinfid'e a gefe tare da cewa,


"Maraba lale sannu da zuwa"


Murmushi mummy tayi ta karasa ta zauna,a gefen tabarma,ta zaunar da Inteesar a gefen ta,sannan ta kalli Abba cikin girmamawa ta ce,


"Ina kwana mallam"


Cikin sakin fuska da Kamala irin tasa ya amsa Mata da cewa


"Lafiya qalau ya aik?"


"Alhamdulillah"
tace tare da kallon Umma ta sakar mata murmushi kafin ta gaishe ta Umma ce tayi saurin cewa.


"Ina kwana Hajiya?ya aiki?"


Murmushi Mummy tayi tare da cewa


" Alhamdulillah angodewa Allah."


Umma ce ta K'ara cewa

"Masha Allah Allah dai yasa ba laifi tayi ba naga ankawo ta har gida."


Atunanin ummi ta d'auka Mummy malamar su Inteesar ce.
Mummy ce ta danyi ajiyar zuciya sannan ta basu labarin Yadda akayi direban ya kad'e Inteesar kuma tak'i yadda suje Koda chemist ne,sannan ta basu hak'uri suka ce kada ta damu ba komai.


Abba ne yace to me ya dawo da ita a wannan lokacin ?
Cikin sanyin ta take sanar dasu an Kore ta ta kudin school fees ne shiru sukayi yayinda Abba ya dafa goshin sa
Mummy ce ta Ciro kud'i a jakkar ta masu yawa kimanin naira dubu ashirin
tace gashinan susayi Mata magunguna,
Amma fir sukaki karba kud'in nan Babu yadda Mummy batayi ba har aje masu tayi amma Abba ya rantse akan cewa bazasu kar'bi kud'in ba,ba yadda ta iya dole ta tafi tare da yi masu sallama ta tafi.


Bayan tafiyar ta ne mallam Ali wato Abba ya kalli Umma cikin damuwa ya ce,


"Tun satin da ya wuce nake ta tunanin kud'in makarantar nan Amma na kasa samu wlh."


Umma ce ta kalle shi ta ce,
"To mallam mai zai hana mu mayar da ita makarantar Gwamnati?"






Daga alk'amin✍️


Zainab Abdullahi K.NT
(Maman Ihsan)






*DON K'ARIN BAYANI*


09065327995






Love u oll😍😘Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89




*INTEESAR*




Story & writing by✍️


Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)






*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_


*Alk’alaminmu ‘yancinmu*










*GARGA'DI*




Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.








Wannan kagaggen labari ne,banyi tunanin Rubuta ta Shi dan cin zarafi ga kowa ba.idan suna ko hali yazo daya,to KU gafarceni ni bada niyyar yin hakan nayi ba.Arashi ne Mai kashe Auren Wawa.




*BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM*


Page0️⃣6️⃣




Ajiyar zuciya Abba ya sauke tare da kallon ta ya ce,


"A zahirin gaskiya bana son nasaka Inteesar makarantar Gwamnati,zanyi k'ok'ari na naga na samu kud'in nan."


Aijyar zuciya umma ta sauke tare da kallon Inteesar.


Ya cigaba da cewa


"Bari dai naje kasuwar na dawo muga Abunda Allah zaiyi."


"To Allah ya bada sa'a ya rufa Mana asiri."
cewar umma
Abba ne ya amsa da Ameen.
Inteesar dai tagumi tayi.


To a ranar da yammaci Mummy ta dawo gidan su Inteesar Don ta K'ara duba jikin ta,inda ta kawo masu Sha tara na arzikisannan ta nemi alfarmar cewa tunda unguwa d'aya suke basu da nisa tana son tasa Inteesar makarantar da 'yar ta take zuwa wato mufida dukkan su kusan sa'annin juna ne bazasu wuce shekaru goma Sha biyar ba a lokacin,umma ta ce,


" Yanzun ni bazance komai ba idan mahaifin ta yazo zan sanar dashi duk shawara da muka yanke shikenan."


Daga nan tayi masu sallama kan cewa jibi zata dawo taji shawarar da suka yanke.


Haka kuwa akayi da Abba ya dawo kasuwa bayan yaci abinci ya huta,Umma ta kalleshi tare da cewa,


"Yauwa mallam wannan matar da suka kusan Kad'e Inteesar da mota tazo ta kawo mana abin arziki sannan ta nemi alfarmar a wirin mu."


Kallonta yayi tare da cewa


"Wace Alfarma kuma zata nema a wurin mu kuma?"


"Wai dama cewa tayi Tana son ta canzawa Inteesar makarantar boko ce,wai zata saka ta inda 'yar ta sa'ar Inteesar take makaranta.wai zata had'a su su dinga tafiya tare inda Direban ta zai dinga kaisu idan lokacin tashi yayi yaje ya dauko su."


Girgiza Kai Abba yayi alamun rashin amincewa


"Bazai yuwu ba,bana buk'ata wato don taji Inteesar tace an Kore ta kud'in school fees shine tayi tunanin haka"


Gyada Kai Ummu tayi tace ,
"To shikenan"


Yaci gaba da cewa


"Insha Allah yadda nad'uki nauyin karatun ta tun daga nursery har primary yanzun Tana secondary jss 3 ,insha Allah bazai gagare ni ba,Allah zai shige Mani gaba."


Bayan kwana biyu kuwa sai ga Mummy ta dawo,cikin sa'a kuma ta samau mallam Ali a gidan,bayan sun shimfid'a Mata tabarma ta zauna ne ta kalli malam Ali.


"Mallam barka da safiya ya iyali?"


Cikin sakin fuska kuwa ya amsa Mata tare da cewa


"lapiya qalau Hajiya, ya gajiyan ki?na dawo Naga sako nace meye zakije wani kashe kud'i wajen yi mana siyayya da Ina gidan bazamu kar'bi komai daga gare ki ba ai tsautsayi ne kuma yarinyar da bataji ciwo ba ba buk'atar ki wahalar da kanki."


Murmushi tayi tare da cewa,


"Ai ba wannan ya kawo ni bama,nasan mai d'akin ka ta sanar dakai alfarmar da muke nema a wajen ka ko?"


Kai ya gyada Alamar Eh


"Ta sanar dani amma gsky kiyi hakuri kibar maganar nan kawai, d'aukar nauyin karatun Inteesar bazai gagare ni ba insha Allah, kamar yadda a can baya ban kasa ba."


Ajiyar zuciya ta sauke don ta fahimci inda maganar tasa ta dosa,yana ganin kamar don ya kasa ne zata d'aura daga yanda ya tsaya,ita kuma ba haka bane a zuciyar ta,soyayyar yarinyar take ji har cikin ranta Allah ya d'aura Mata kaunar 'yar su.


Cikin sanyin murya tace,


"Bawai ka kasa bace,a'a wallahi Allah ne ya d'aura Mani soyyayar 'yar ku,Ina kaunar ta fisabilillahi har cikin raina.duk da baku sanni ba kuke tsoron amincewa dani ko?"


Kai Mallam Ali ya girgiza tare da cewa,


"Duk da bansan Halin ku ba Amma da alamu ku mutanen k'warai ne domin inajin yanda jam'ar unguwa ke yabon ku akan kyautatawa da kukewa makwabtan ku,musamman Alhaji Sani mijin ki kowa yabon sa yakeyi akan kyawawan halayyar sa da kyautatawa mabukata musamman watan Ramadan Sai dai Allah ya saka masa da alkhairi."


Murmushi tayi cikin Jin dad'i,yayin da Umma ta amsa da Ameen.


Mummy ta ce,


"Naji dad'in jin hakan,kamar yadda ka sani muna da yara uku da miji na babban wato Muhammad muhdeen Yana can kasar waje Yana karatun masters d'in sayanzun 'yan matan su biyu ne a gaba na Asiya ita ke bin Muhammad Muhdeen,yanxun haka wannan shekaran insha Allah zata kammla karatun secondary din ta sai Auta wacce bazata wuce sa'ar Inteesar ba don Allah ka Amincewa mani da buk'atata kullun da safe idan ta shirya sai tazo Direban ya kaisu tare,idan an tashi yaje ya d'auko su,na d'auki nauyin karatun nata

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads