Showing 84001 words to 87000 words out of 149432 words
Chapter 29 - INTEESAR Book Complete by Zainab Abdullahi.txt
a falon Nan bayan kinsan za'a iya yin bak'i a gidan ko?"
"Nifa bansan kowa ya shigo ba ba daga ni sai Gwaggo nayi barci"
Tsawa ya daka Mata
"Zaki je ki sauya kayan ko kuma kisa hijabi ne ko kuma zaki tsaya kina bani labari ne."
Mi'kewa tayi ta nufi d'akinta, shi kuma ya zauna kan kujera, kallonsa Gwaggo tayi ta ce,
"Sai kishin banza da wofi, ka damu da ita ne tunda ka tafi baka iya cewa a bata waya kaji lafiyarta ba?"
Inteesar ta dawo sanye da hijab har k'asa, kallon Jabeer tayi tare da gaishe sa cikin girmamawa.
"Yaya Jabeer ina wuni?"
"Lafiya qalau Inteesar, ya hak'uri da rayuwa?"
"Alhamdulillah, yanzun ka shigo ne?"
"Eh hanya ce ta biyo dani nace bari na lek'o mu gaisa."
"Allah sarki mungode, ya Aunty Maryam?"
"Tana lafiya lau"
Murmushi tayi tare da cewa
"Masha Allah"
Mi'kewa tayi ta nufi kitchen ta dawo d'auke da faranti da ruwa da lemu akai, ajiye tayi a gabansu, dama Muhdeen gefen Jabeer ya zauna, bayan ta ajiye ne Jabeer ya d'auki ruwa yasha, sannan ya ce,
"Amarya ai ba ruwa kad'ai ba har da abinci, don shi nafi buk'ata."
Murmushi tayi ta nufi hanyar kitchen, ba jimawa sai gata ta dawo da faranti Babba, anjera food flask da plates da spoon, a gabansu ta ajiye ganin zata bud'e ta zuba yayi saurin cewa
"Barshu kawai hakan ma mungode"
Komawa tayi ta zauna a mazauninta, Jabeer ya bud'e food flask d'in,tuwon shinkafa ne da miyar agushi da ganyen ugun da yaji naman sa, d'iba yayi ya sauka ya zauna Kan center carpet ya Fara ci, kallon Muhdeen yayi tare da cewa,
"Mutumin Abuja ba zaka ci abincin bane? ko kuma Wanda ka ci a Abujan ya ishe ka?"
Ki kallonsa baiyi ba idonsa na kan waya, Gwaggo ce ta ce
"Tun Abinci da ya ci na Abuja ai yakamata ace yaji yunwa tunda doguwar tariya yayi."
Jabeer ya kece da dariya sannan ya ce,
"Ai Gwaggo ba Zaki Gane bane, baki san Abujar da yaje ba wacce kika sani bane wata ce."
Kallon rashin fahimtar inda zancensa ya dosa ta ce,
"Kai Jabeeru Abujar guda nawa ne?"
"Nidai d'aya na sani amma wannan shalelen jikar naki Abujansa ba d'aya bace, wacce yaje shekaranjiya ba wacce kika sani bane wata ce."
"Kai Jabeeru zancen ya Isa haka nan don naga alamar santi kawai kake, saboda dad'in girkin Jika ta da tayi, don kasan ita ta iya girki mai d'an Karen dad'i, bansan girkinta na sanya sambatau marasa kai ba sai akanka, dama waccan solo'biyar matarka bata iya girki ba."
Jinjina Kai yayi
"Shikenan Gwaggo tunda haka kika ce"
Yana gama cin abincinsa ya wanke hannu, ganin Muhdeen baida niyyar cin abincin ne yasa Inteesar ta tattara kayan ta Kai kitchen.
Bayan ta dawo ne suka cigaba da firar su sama-sama Jabeer ne da Gwaggo suke fira, Inteesar ta lura da tsarabar da aka ajiye d'auka tayi takai kitchen ta dawo ta zauna, Gwaggo ce ta fara Gyangyad'i, fira suka tsakanin Jabeer da Inteesar,inda ran Muhdeen ya sake 'baci kenan,wato da shi da banza duk d'aya a wajenta ko? tasan yayi tafiya ba sannu da dawowa ba komai,bata gaishe shi ba, bata bashi ruwa ba ballantana abinci sannan ta zauna tana hira da wani a gabansa ko kallonsa ma batayi ba, girgiza Kai yayi sannan ya mik'e ya nufi d'akinsa,Yana Jin muryar Jabeer na cewa a fito lafiya Mutumin Abuja, Bai kula sa ba yayi shigewarsa ciki.
Daga nan Jabeer yayi masu sallama ya ya fice abinsa.
Haka rayuwa tayi ta tafiya, yau alhamis yau ya kama gobe Gwaggo zata tafi, Inteesar ta shiga damuwa sosai har kukanta,Wanda hakan kuwa ki jikin Muhdeen, domin shi so yake ta tafi Sumayya ra dawo gidan,kowa da abunda ke gabansa, Muhdeen na cikin farin ciki Inteesar na cikin bak'in ciki,Wanda Gwaggo duk ta lura da yanayin kowanne a cikinsu, kuma tasan tabbas akwai abunda Muhdeen ke shiryawa da ya matsu tabar gidan sai dai ta kasa gano komai.
Zaune suke a dinning table suna Breakfast, Inteesar gaba d'aya ta kada saka komai a cikinta,tana ta tunanin wahalar da tasha a gidan a hannun Muhdeen, dalilin zuwan Gwaggo gidan ne ta samu 'yanci a cikin gidan, to yanzun gibe Gwaggo zata tafi kenan hakan na nufin zata cigaba da wahala ne kamar yadda yake bautar da ita a baya? ajiyar zuciya ta sauke tare da kallon Gwaggo, Gwaggon ma ita take kallo
"Ke 'yar albarka lafiya kuwa?"
Girgiza kai tayi tare da cewa
"Bakomai Gwaggo"
"Akawai komai"
Sunkuyar da kanta tayi tana juya cokali a cikin kofin tea, Gwaggo ta sake magana ta ce
"Kinga idan akwai wani abu ki sanar dani,Kinga ke amana ce a wurinmu, duk abunda kike buk'ata ki fad'a mani idan ina da halin yi maki shi zan maki, idan kuma banda shi zansa mijinki ya maki idan baifi k'arfinsa ba, amma kada kuce na k'ara kwankin da zanyi a gidan nan."
Marairaice fuska ta yi cikin shagwa'ba ta ce,
"To ai abunda zan nema a wajenki ne kika ce kar na nema."
Dariya tayi
"Dama nasan abunda zaki ce kenan, ki nemi wani abun amma ba wannan ba"
Satar kallon Muhdeen tayi sanna ta fara magana
"To ai banda wayar da zan dinga magana da ke da kuma su Mummy."
Kallon Muhdeen Gwaggo tayi sannan ta ce,
"Kaje ka kawo mata wayarta yanzun nan."
Girgiza Kai yayi sanna ya ce,
"To zan bata."
"Ba haka nake son ji ba, cewa nayi kaje ka kawo mani wayarta, idan kuma ban Isa ba ka fad'a mani yanzun na kira Mahaifiyarka na sanar da ita."
Ba tare da yayi wata magana ya mik'a ya nufi d'akinsa, ba jimawa sai gashi ya dawo da wayar ya mik'awa Gwaggo, amsa tayi ta mi'kawa Inteesar, amsa tayi tana murna tare da godiya.
Da misalin k'arfe goma na dare Gwaggo da Inteesar suna zaune a d'akin Inteesar suna fira,na bankwana har k'arfe goma sha biyun dare yayi, Gwaggo ce ta kalli Inteesar ta ce dare ya tsala
"Yakamata kije mijinki na jiranki"
"Ni Gwaggo ba abunda zan zan masa ki bari mu kwana tare na yau kawai."
"A'a duk fira dai idan ba k'arya zamu fad'a ba duk munyi ta, bana son gardama kije kawai d'akin mijinki."
Sanin haklin Gwaggo ne yasa Inteesar ta mik'e bayan tayiwa Gwaggon sai da ta fice.
A falo ta tsaya ta tabbatar ba Wanda yaganta ta shige d'akin da take kwanciya tana barci,don dama tun ranar da Allah ya k'wace ta hannun Muhdeen ya kuma yo alk'awarin duk ranar da ta shigo masa a irin wannan lokacin sai ya kar'bi hakkin aurensa a kanta, hakan yasa bata sake yarda take d'akinsa dadaddare ba, tana shiga d'ayan dak'in ta tura k'ofar tare da rage hasken d'akin.
Washe gari Gwaggo zata tafi Inteesar sai kuka take kamar wacce aka ce sun rabu kenan, haka Gwaggo ta dinga rarrashinta har ta gaji, k'arshe dai haka ta hak'ura ta kyaleta, Direban Mummy ne yazo d'aukarta,haka suka fice Muhdeen da Inteesar dake tsaye a harabar gidan bayan tafiyar Gwaggo suka koma cikin gidan, har suka shiga Bata daina kuka ba, jin muryarsa tayi yana cewa
"Ke ki rufe mani baki da zaki sakawa mutane kuka na ba gaira ba dalili, ko mutuwa akayi maki ne? to wallahi ki rufe mani baki kafin kisha mamaki anan."
Sanin cewa mai goyon bayanta bata gidan yanzun daga ita sai shi ne a gidan, kum tana tuna irin wahalar da ya gana mata a baya ne yasa tayi shiru.
"Ki tashi ku shiga kitchen, ki shirya abinci lafiyayyae mai kyau kafin na dawo da bak'uwa a cikin gidan nan."
Da sauri ta kalle shi ta ce
"Mummy ce zata zo?"
Koma wace ce idan tazo zaki ganta,sannan wancan d'akin ki share shi ku goge shi tas ko Ina yayi fess kisa turaren wuta."
Murmushi tayi cikin Jin dad'i don a tunaninta bak'uwa ce wacce zata samu abokiyar zaman gida da fira,don haka ta saki murmushi ta nufi kitchen.
Wayarsa ce tayi k'ara ya duba yaga ita ce, d'agawa yayi tare da cewa
"Hello Baby na"
Jin muryarta yayi tana cew
"Wai Baby har yanzun Bata tafi bane?"
"Yanzun nan ta tafi,na bada umarni ne a gayara maki d'akinki a girl's maki lafiyayyaen abinci."
Yamutse fuska tayi
"Wai kana nufin wannan kucakar yarinyar ce zata girka mani abinci? nifa bana son jagwalgwalo."
Dariya yayi tare da cewa
"Kada ki damu, tunda na iya kema zaki iya, yanzun dai bari nayi wanka nazo na d'auke ki."
"Okay l love you"
"Love you too baby"
Dagana nan ya katse kiran ya nufi d'akinsa don yin wanka zaije ya d'auko Sumayyarsa ta dawo kusa dashi, farin cikinsa zata dawo gidan.
Daga alk'amin✍️
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
Don k'arin bayani
09065327995
Love u oll😘😍
Comment & shareFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GXLLwE11VEK6KkBh5sqU89
*INTEESAR*
Story & writing by✍️
Zainab Abdullah K.N.T
(Maman Ihsan)
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_
*Alk’alaminmu ‘yancinmu*
*SADAUKARWA*
Wannan sadaukarwa ne a gare ki Autar Ammi (Sakeenah) kece ta farko da kika fara kira na a waya dan jin lafiya ta kwana biyu shiru baku ji ni ba, naji dad'i da nuna k'auna da kulawa, wannan shafin naki ne kiyi yadda kike so da shi, Allah yabar zumunci.
*GARGA'DI*
Wannan littafin mallakar marubuciyarsa ce, don haka a guji sarrafa mani shi ta kowace siga ba tare da izinina ba.
*SANARWA*
Wannan kagaggen labari ne, banyi tunanin rubuta shi da cin zarafi ga kowa ba, idan suna ko hali yazo d'aya to a gafarce ni bada niyyar yin hakan nayi ba, arashi ne mai kashe auran wawa.
*JINJINA*
Jinjina ta musamman a gare ki members na *INTEESAR HAUSA NOVEL* Nagode sosai da kulawarku a gare ni, Allah yabar zaman tare.
*BISIMILLAHI RAHMANI RAHEEM*
Page5️⃣1️⃣
Daga nan ya katse kiran ya nufi d'akinsa don yin wanka, zaije ya d'auko Sumayyarsa ta dawo kusa da shi, farin cikinsa zata dawo gidan.
Bayan ta gama duk ayyuukan da zata yi ne ta shiga d'akinta wanka tayi, ta shirya cikin riga da siket na leshi, wayarta ta d'auka tana game, k'arar k'ofa taji ta mik'e da sauri duk da bata san wace irin bak'uwa ce tazo ba amma duk da haka da fara'arta ta bud'e k'ofar.
Kwatsam idanunta ya sauka a cikin na Sumayya, sai da gabanta ya fad'i, amma sai ta dake ta k'ak'alo murmushi a fuskarta cikin sakin fuska ta ce,
"Sannu da zuwa Aunty Sumayya."
Kallon banza tayi mata tare da tare da shigowa cikin falon, saura kad'an ta bangaje inteesar sai tayi saurin matsawa baya ta bata hanya, Muhdeen ne ya shigo hannunsa rik'e da jakkarta, kai tsaye falonta ta nufa tare da zama kan kujera ta ce,
"Wash baby na gaji."
Ajiye jakkar yayi tare da cewa
"Ayyah sorry, yanzun ki tashi kici abinci sai ki kwanta ki huta ko?"
Yamutse fuska tayi tare da cewa
"Ina yarinyar nan take ne? tazo ta zuba mun abinci naci."
Juyawa yayi ya kalli falon inteesar, ganin bata nan ne yasa ya k'wala mata kira, ashe tana kwance akan kujera tana tunanin sabuwar rayuwar da zatayi da Sumayya a gidan, ta ji muryarsa yana cewa
"Kina ina ne!"
Da jin haka tasan ita yake kira don haka ta mik'e ta nufi falon Sumayya, koda ta k'arasa zaune ta same shi yayin da Sumayya ta kwanta tayi filo da cinyarsa, kallo d'aya tayi masu ta kauda kanta gefe tare da cewa
"Gani"
Tsawon mintuna uku tana tsaye bai ce mata komai ba, ta d'auka baiganta bane don haka ta juyo ta kalle shi, sai taga idanunsa akanta kallonta yake sunkuyar da kanta tayi ganin yadda idanunsa ke yawo a jikinta, jin muryarsa tayi yana cewa
"Baki ganmu bane"
Ba tare da ta kalle shi ba ta ce
"Naganku"
"Okay, wulak'anci ne yasa kika share mu?"
Shiru tayi masa ba tare da ta ce komai ba, shi kuma abunda ya tsana kenan yayi magana ayi masa shiru kamar ba'aji ba, hakan yasa ya daka mata tsawa.
"Sa'anki ne ni da zanyi maki magana kiyi banza Dani?"
"Cikin sanyin muryarta ta ce,
"Kayi hak'uri"
Ba tare da ya kalle ta ba ya ce,
"Baki ga Sumayya ta dawo bane?"
"Na ganta"
"Tsabar wulak'anci ne yasa kika share ta baki gaishe ta ba?"
Kafin tayi magana ne suka hi jiyo muryar Sumayya ta cewa
"I na kuwa zata gaishe ne bayan muna auren miji d'aya tana ganin dai-dai da ita nake, bari kiji na sanar dake abunda kika manta, ni nan mijina yana sona sosai auren soyayya mukayi auren na gani ina so mukayi, ba irin naki ba auren had'i da kwad'ayi irin na iyayenki yasa suka bayar da ke ga miutumin da baya k'aunarki baya sonki da k'aunarki aka k'k'aba masa ke, to bari kiji nan gidan tamkar kinzo aikatau ne, ki d'auka gidan aikinki be ba gidan aurenki ba, dan ba mijin da ya kalle ji a matsayin matarsa, koba haka bane baby na?"
Jinjina kai yayi tare da cewa
"Duk abunda kika fad'a ai gaskiya ce, ba k'arya "
Jinjina kai Sumayya tayi ta d'ora da cewa
"Kinji abunda ya ce da kunnenki ko 'yar matsiyata kawai."
Kallon Sumayya yayi, kallo mai cike da gargad'i Wanda ta gane manufarsa, amma sai tayi kamar bata gane ba ta d'ora da cewa
"Ko ke ba 'yar matsiya...
"Tsawa ya daka mata tare da cewa."
"Stop"
Da mamaki ta kalle shi da niyyar yin magana taga inteesar na wajen, don haka tayi shiru dan yadda taga fuskarsa ya canza tasan zai iya kunyata ta a gaban yarinyar da ta raina, idanun inteesar cike tab da k'walla don ba Wanda ya ta'ba mata irin cin mutuncin da aka mata yanzun, jin muryarsa tayi ya ce
"Kije ki kawo mana abuncin mu nan"
Ba tare da ta ce komai ba ta nufi dinning area dan d'auko masu abuncin .
A babban faranti ta jero masu shi, tazo ta ajiye tare da komawa ta kawo masu ruwanda drinks, ajiyewa tayi ta koma d'akinta tare da fad'awa kan gado ta saki marayar kuka.
Bayan tafiyarta d'aki ne Muhdeen ya kalli Summayya tare da cewa
"Kada ki zak'e akan yarinyar nan da yawa fa, dan zaki iya fuskantar k'alubale."
Kallon mamaku tayi masa tare da cewa
"Kodai ka fara son yarinyar na ne?"
Gajeren murmushi yayi tare da cewa
"Me kik gani"
Ya za'ayi Ina mata magana Dan tasan banbancin da ke tsakaninmu, kuma tasan matsayinta zaka dakatar Dani?"
"Ba haka bane naga kina neman wuce gona da iri ne, duk abunda zaki mata kada ki ce zaki ci mutuncin iyayenta, ko ki zage su bana so, kuma idan yarinyar ta kura Mummy ko Gwaggo a waya ta sanar dasu abunda kike mata me kike tunanin zai biyo baya? kindai san irin k'aunar da suke mata kema shaida ce, bana son abunda zai janyo muna matsala daga ni har ke "
"Amma ai kai ne da bakimka ka fad'i cewa nan kamar gidan aikinta na d'auka 'yar aiki aka kawo mani ba kishiya ba, don na fad'a mata shine laifi na?"
"Ba sai kin fad'a mata ba, ai aikinta zata san da hakan"
Hannunta ya janyo don ta sauko ta ci abincin, zama suka yi Kan center carpet.
"To ka kira ta ko muna zamu...'
Hannu ya d'aga mata alamar tayi shiru,inda ya bud'e food flask d'in ya d'auki plate
inteesar kuwa tana kwance a d'akinta sai sheshshek'ar kuka take,zagin da Sumayya tayi mata ne ke mata ciwo a zuciya .
Knocking akayi a k'ofar falon, inteesar kama tana can kwance a d'akinta sai kuka take bata ma san anayi ba, Muhdeen ne ya tashi ya he ya bud'e k'ofar, k'anwar Mummynsa ce Aunty Abla tare da Hajiya Bilkisu mai gayaran Amarya, Murmushi Aunty Abla ta sakar masa tare da cewa
"Son wato ko ziyara baby ko?"
Sosa kai yayi tare da cewa
"Bisimillah ku shigo Aunty"
Shigowa sukayi suka zauna a falon inteesar, gaida su yayi cikin girmamawa, suka ansa masa cikin sakin fuska, daga nan ya k'walawa Sumayya kira tare da cewa
"Baby zo ga Aunty Abla ku gaisa, duk da bata so tashi ba haka ta mik'e ta k'araso falon tare da zama kujera ta kalle su tare da cewa
"Hy ya kuke?"
Kallon juna sukayi Aunty Abla da Hajiya Bilkisu, Muhdeen kuma ya dafe goshinsa cike da takaucin abunda Sumayyar tayi, ganin basu amsa va ta mik'e ta kalli Muhdeen ta ce
"Baby bari na kwanta na d'an huta "
Baice mata komai ba ta mik'e ta nufi d'akinta, kallonsa Aunty Abla tayi tare da cewa
"Son where is my daughter?"
Shiru yayi da bai gane wa take tambaya ba, kafin ya ce
"Wai Mufida kike tamabaya?"
Harara ta watsa masa tare da cewa,
"Annan gidan Mufida take da zan tambaye ka? ina 'yata inteesar take?"
"Tana d'aki Ina zaton kamar barci ma takeyi doke ta tashi don ita muka zo gani."
Mik'ewa yayi ya nufi d'akinta, koda ya shiga kwance ya same ta tana kuka? takaici ne yakama shi don yasan tabbas zasu gane inteesar tayi kuka, tsawa ya daka mata wanda hatta su Hajiya Bilkisu da suke falo sunji.
"Ke dalla tashi dukanki akayi ki kuma me?da zaki zo kina kuka ga bak'i munyi salon kija Mani matsala ko?"
Shiru tayi tunda ya fara magana
"To bari kiji, muddin kika bari suka gane wata matsalar wallahi sai nayi masifar 'bata maki rai, dai kukan da zakiyi mai dalili ne, ki tashi ki shiga toilet ki wanke fuska kizo falo, mik'ewa tayi ta nufi toile shi kuma ya fita zuwa falon, bayanbta wanke ne ta nufi k'ofar zuwa falon.
Tana bud'e k'ofar ne taga su Aunty Abla, da sauri ta sauri ta k'arasa gare su ta rungume Aunty Abla, sannna ta rungume Hajiya Bilkisu ta ce,
"Oyoyo sannunku da zuwa, durk'usawa tayi ta gaida su cikin girmamawa.
"Ina wunni?"
Gaba d'ayansu suka amsa da
" Lafiya k'alau inteesar"
"Ido suka zuba mata ganin yadda ta d'an rame kuma ga fuskarta alamun taci kuka, mik'ewa tayi ta nufi kitchen don kawo masu abun ta'bawa, bayan ta nufi hanyar kitchen ne Aunty Abla ta kalli Muhdeen ta ce,
"Ya naga yarinyar nan ta rame? bata da lafiyane."
"Kafiyarta k'alau Aunty Abla."
Jinjina kai tayi ba tare da ta ce komai ba, inteesar ce ta kawo masu ruwa da lemu ta ajiye zata koma kitchen Aunty Abla ta ce,
"Ina kuma zaki?"
"Zan kawo maku abinci ne"
Murmushi sukayi dukansu inda Aunty Abla ta d'ora da cewa
"Kada ki damu yanzun daga gidan Hajiya Bilkisu muke, sai da muka ci abincin kafin muka zo nan."
Dawo wa tayi ta zauna Kan center carpet dake shimfid'e a wajen tana murmushi ta kwantar da kanta akan k'afar Aunty Abla sannan ta fara magana
"Aunty Abla ba Wanda yazo gani na sai Gwaggo, ko Mummy da Umma na basu zo sun ganni ba."
Murmushi