Showing 96001 words to 99000 words out of 287659 words
Chapter 33 - KURKUKUN ƘADDARA! (TAKUN FARKO) BY By Boss Bature [www.aihausanovels.com.ng].txt
lace milk colour, idanuwanta na a manne da farin glass medicated, Ta natsuwa tana daddana laptop ɗinta dake asaman Table ɗin gabanta, da alama Komai ya daidaita don yanayinta bai nuna tana acikin damuwa ba,
Gaba ɗaya ta tattara kwandon hankalinta akan aikin da take yi acikin laptop ɗinta,
Sautin Dirar motoci ta juyo acikin Apartment din nasu, dakatawa ta ɗanyi da daddana laptop din ta ɗago tana kallon bakin kofar shigowa falon, duk da tasan ba lallai In baƙin su bane tun da basu kaɗai bane akwai sauran mutanan dake Haya Acikin Ginin,
*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*
Uncel abdallah ne Ya shigo Falon, Hannun shi ruƙe da key ɗin motarshi, Suit ne ajikin shi, Miƙe wa Hajiya adama tayi fuskarta asake tace "Welcome back dear, I heard the sound of cars Coming in ko munyi baƙi ne"? sai da ya samu wuri ya zauna tukunna ya kalle ta fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Ni ne baƙon ae, fatan na same ki lafiya, Yau naga walwala atattare dake, Ga shi kin ɗau wanka kinyi kyau abunki,"
Ta6e baki ta yi "Ae tun da kayi mun albishir game da komawarmu gida, Nake ta sakin fara'a ni kaɗai abuna, Yanzu haka ma da kaganni a zaune, Ina duba kayayyakin da zan siyane na tsaraba da zanyiwa mutanan gida," takai ƙarshen maganar tare da kama hanyar zuwa kitchen tace"Bari na kawo maka Ruwa mai sanyi kasha"
"Da kanki Hajiyata? Ina mai aikin gidan take ne"? A sukwane ta Juyo tana bin shi da kallon bansan rainin wayau,
"Oh kamanta irin Korar da kayi ma Ajumma daga gidan nan, Saboda laifin da ba nata ba, ƴar baiwar Allah, dama burinka kaga ina shiga kitchen da girmana, ae yanzu hankalin ka ya kwanta, Hajiya adama ta zama kukun mijinta" Dariya Uncle abdalla Yayi"Matar nan kina sani nishaɗi, Abun alfahari ne mace ta girka ma mijinta abinci da hannunta yaci ya sanya mata albarka, Ta samu lada, Ni ae naga Cigaba sosai, da na kori wannan tsohuwar matar, Tun barinta gidan, kika daina shan Soju, gashi yanzu kin samu natsuwa kin dawo Hajiya adamar dana sani,"
Hararar wasa ta jefa mashi daga inda take a tsaye" korar ajumma da kayi ba shi ne yasa na daina shaye shaye ba, Da naso zan fita inje in siyo da kaina ne, Allah ne yayi silar shiryuwata, dama ba halina bane, tsautsayine da ƙaddara, da kuma damuwar da na shiga na rashin mutun uku masu mahimmanci acikin rayuwata.........." muryarta a karye takai ƙarshen maganar, da sauri tajuya ta shige Cikin kitchen,
Jingina bayan shi Yayi a jikin Sofa ɗin da yake zaune, Har ga Allah Shi kanshi yana acikin matsanaciyar damuwa na rashin ya'yan shi da ya yi, Yaji raɗaɗi sosai, sai dai ba yadda zai yi, daure wa kawai ya ke yi, A duk lokacin daya tuna rashin Da yayi, Na ɗan uwansa, Kuma yayansa Malam zahiru, da mahafiyarsu deeja, Sai ya dinga Jin kanshi tamkar marayan da baida mafaɗi aduniya, Dama wake gaya mashi gaskiya idan yay badai dai ba? malam zahiru ne, tun yana yaro shi yake zaunar dashi yayi mashi nasiha game da rayuwar duniyar nan, kalmar da yafi faɗa mashi itace "ABDALLAH KAJI TSORON ALLAH, ' tuna wannan yasa shi kai hannu ya dafe goshinsa, Idanuwanshi suka Cicciko tab da kwalla, haƙika yaji mutuwarsu, Hatta yahana su Mahaifiyar Tajuddeen, Yaji mutuwarta sosai, Mutanan kirkiki, Mutane masu ƙima da daraja,
Ajiyar zuciya ya sauke, tare da lumshe idanuwanshi, Bakomai yake tunawa ba face Tajudeen lokacin da zai raba shi da iyayenshi, Suna kuka yana kuka saboda basu son rabuwa da juna, Suna matuƙar ƙaunar ɗansu, Amma saboda son zuciya yabi ta ƙarfi da yaji don yana da arziƙi, ya ba mahaifiyarsu Cin hanci, aka damƙa mashi yaro, tun da yake bai ta6a danasanin raba tajudeen da iyayenshi ba, Sai bayan rasuwarsu, tsawon shekaru basu yi tozali da dansu ba, har sun koma ga mahaliccin su, Shi ma kuma ɗan nasu An neme shi ƙasa ko sama babu shi, Wannan wata irin ƙaddarar rayuwace? Yanzu idan Allah yasa aka ga su tajudden Taya zai Iya Sanar dashi game da mutuwar Iyayenshi!!? innallahi wa'inna ilaihirraji'un............
Tun ɗazu Hajiya adama ta fito daga cikin kitchen, hannunta ruƙe da plate mai ɗauke da glass cup na ruwa mai sanyi tare da snacks, ta jima a tsaye tana kallon Mijinta nata da ya yi zurfin Cikin tunani, Hawaye ta gani kwance a cikin idanuwanshi, Da alamun damuwa attare da shi ba kamar yadda ya shigo mata ba, A saman C table ta ɗaura plate ɗin dake hannunta,
Kwala mashi kira Tayi A firgice yakai idanuwanshi akanta yana kallonta
"wai lafiya dear, Ina ta kiran sunanka Amma hankalinka sam baya atare dakai, Meya faru ne? Yanzu fa nabarka fuskarka asake, amma kuma na dawo na taras dakai cikin damuwa" tayi maganar tare da kai hannu ta ɗauki Cup ɗin ruwan ta miƙa mashi,
Hannu yasa ya kar6a, tare da kaishi saitin bakinshi yana sha, Zama hajiya adama tayi tana fuskantar shi, Jira take yi ya gama sha yayi mata bayanin dalilin shiga damuwarshi,
A hankali ya sauke Cup ɗin saman table, ya zura hannu Cikin trouser pocket ɗinshi ya zaro hanky ya goge fuskarshi, sai da ya daidaita natsuwar shi tukunna ya kalle ta, gaba ɗaya hankalinta na akanshi, sam baison ya faɗa mata dalilin shiga damuwar tashi, don yasan halitta, Yanzu ta kama yi mashi kuka, shiyasa ko zancen su Taj bai cika son yi mata ba, Rauni ne da ita,
Gudun kada ta ƙara tambayar shi meke damunshi, yasa shi yin saurin canza zancen ta hanyar cewa"Yawwa, Yanzu wani shirye shirye yakamata muyi na komawa Ƙasar mu? Naji kince zaki yi siyayyar kayan tsaraba da zaki yi ma mutanan gida,"
Jinjina kai Hajiya adama tayi tare da cewa"eh, idan ya rage kamar saura 4 weeks Mu tafi, Inaso zamuje Shopping mall atare, Akwai kayayyakin da nake so Na Siyawa ƙanne na, kasan su mayun kallon korean drama ne, suna san suturarsu ba ƙaramin burgesu yake yi ba, inaso na siya masu, hada Jikana zan siyawa kayan wasan yara, da kayansu na al'ada suna burgeni, ita Fatima ma hada cewa in yi masu tsarabar abincinsu, In banda shiririyata, zan dai siya masu chocolates ɗinsu kalar wanda bamu dasu a gida, " magana take yi mashi amma hankalin shi gaba ɗaya baya akanta, har saida Tace"Kai fa? Me zaka yi tsaraba da shi
Murmushin yaƙe ya yi mata, muryarshi a karye yace"Wa nake da shi da zanyi ma tsaraba? Dama ƴa'ƴana ne, yanzu kuma babu su, amma duk da haka zan siyawa Angel kalar suturarsu, a ƙiyashin da nayi yanzu takai 15years a duniya, Zan yi mata siyayya sosai in ajiye mata, hada bags and shoes da teddys, komai ma zan siya mata, duk ranar da Allah ya bayyanar dasu, sai in damƙa mata abunta,' yakai ƙarshen maganar, tare da duƙar da kanshi ƙasa, Shi kanshi baisan yayi waɗannan Zantuttukan ba, Saboda su ne aranshi shiyasa yayi maganar, Shessheƙar Kukan Hajiya adama yajiyo acikin kunnanshi, Kafin ya ɗago da kanshi tuni ta miƙe da sauri ta wuce zuwa bedroom ɗinsu, Binta yayi da kallo har saida ta 6ace ma ganinshi,
Girgiza kai kawai yayi, kafin ya miƙe ya nufi ɗakin, Don ya samu yayi wanka Ya canza kayan jikinshi,
*Back To Prison🥺*
Mutsu mutsun farkawa daga bacci ta ke yi, eye lashes ɗinta sun manne ma juna, daƙyar ta samu ta ware idanuwanta basu sauka akan kowa ba, sai akan fine face ɗin Danish dake ta sharar bacci, kasalalliyar ajiyar zuciya ta sauke a yayin da take kallon shi cikin natsuwa, kamar wani baby ya naɗe Jikinshi cikin bargo, fuskarshi kaɗai ce awaje, tun daga kan yadda yake fitar da numfashin shi, zaka shaida yana acikin kwanciyar hankali, baƙaramin daɗi taji ba, tana fatan Allah ya yaye mashi lalurar dake damunshi,
Almost 15 mins tana kallon shimfiɗarshi, kafin ta yunƙura ta miƙe zaune ta jingina bayanta a jikin bango, gadajensu batool tabi da kallo, Tayi mamakin ganin basu farka ba, Kamar wasu matattu sai sharar bacci suke yi, kowa ya kudundune jikinshi cikin bargo, sunyi matuƙar burgeta sai ta dinga jin inama ace Acikin Gidan Mahaifinta suke ba'a Cikin Gidan Kurkukun ba, da sun more rayuwarsu, tasan cewa Danginta zasu kar6esu hannu bibbiyu, musamman aunty aneelerh, da hajiya adama suna son yara sosai, taci alwashin idan Allah ya bata Ikon musuluntar dasu, Zata nema masu hanyar da zasu gudu daga Cikin Gidan kurkukun ƙaddara, Sai dai babban abunda take yi ma fargaba shine, Taya za'ae Su fita daga Cikin kurkukun da ransu da lafiyarsu? Idan Allah yasa sun samu ƙopar fita kenan, Bayan wannan abunda take matuƙar jimawa Anya kuwa GIDAN KURKUKUN ƘADDARA A cikin ƙasar Nigeria yake!? idan har ba'a Nigeria yake to kuwa dai suna acikin tsaka mai wuya! Fatanta Allah yasa ba awani ƙurmin dajin ginin yake ba, Don kuwa akan hanyar guduwa ma wata dabbatar na iya kai masu hari ta Cinye Naman Jikinsu......."
Tana Cikin yin wannan Zancen Zucin nata, Karaf idanuwanta suka sauka akan danish dake ƙoƙarin faɗowa daga saman gadonshi, Cikin magagin bacci, A hanzarce ta duro daga saman gadonta tayi gaggawar tarbe shi, ƙiris Ya rage ya tiƙo ƙasa, ba don Allah yasa tayi saurin zuwa ba, da kanshi yayi mugun buguwa,
Nannaɗeshi tayi tare da turashi saman gadon, Ya koma yadda yake, Ajiyar zuciya ta sauke yayin da take kallonshi, Soft red lips ɗinsa ta gani suna motsi, alamar yana sambatu, miƙewa tayi ta hau saman gadon, ta duƙar da kanta saitin la66ansa, ta natsu tana sauraron me yake cewa,
_the sounds is soothing me, I can't stop listening to ur voice, pls keep reading it in my ears, am really enjoying it_
Murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, jin sambatun da danish yake yi, duk akan Karatun kur'anin da tayi mashi jiya ne, ta fahimci cewa ba ƙaramin daɗi yaji ba, shiyasa ma har yake sambatu acikin Baccinsa,
Whispering tayi mashi acikin ear ɗin nashi tace"Kana so In koya maka"? sam batayi tunanin zai amsa bata, sai ji tayi yace"yeah," da sauri ta kalle fuskarshi, Abun mamaki Bacci yake yi bai farka ba, amma yana magana, ƙumshe dariya tayi kafin ta ƙara cewa"Dame zaka biya ni idan na koya maka"? Tayi tambayar Tana sauraron amsar da zai bata,
Cikin muryar bacci yace"I ave nothing to pay you, but I can promise you myself if you want" Cikin nishaɗi angel take dariya, A maganar da yayi mata idan har zata fassarata a matsayinta na wadda tayi rayuwa awajen kurkuku, Tamkar kalaman soyayya ne, Amma shi awurin shi bakomai bane, ya faɗi mata hakan ne saboda baida abunda zai iya biyanta da shi, idan ba kan nashi ba,
"does that mean you will be my slave? If I give you an order, will you follow?"
Amsa mata yayi"yeah" koda wankin Uniform ɗina ne? Tayi tambayar tana kallon fuskarshi, idanuwanshi na arufe gam, wannan karan bai bata amsar tambayarta ba, da alama ya kuma yin nisa Cikin baccin sa,
Ruƙo bargon shi ta yi tare da ƙara janshi ta rufe mashi har zuwa saman fuskarshi, Tana ƙoƙarin saukowa daga saman gadon danish, Ta ji yo motsin buɗe ƙopa, da alama giants ne suka ƙaraso, Yau Abinci ya riga masu Cin shi, ƙarasowa,
Ƙarasa saukowa tayi daga kan gadon nashi, ta tsaya a tsaye tana Jiran su ƙarasa shigowa Ciki, Takun tafiyarsu ta soma jiyowa, kafin su bayyana su ukun nan hannayensu a ruƙe da wooden trays, mai ɗauke da kayan Kalacinsu,
Akan idonta suka wuce zuwa saman dining carpet ɗinsu, Kowa ya sauke Farantin dake a hannunshi, Ja da baya su kayi atare suka ƙame kamar yadda suka saba, tunani ta shiga yi Kowanene acikinsu Ya damƙeta aranar nan har yayi wurgi da ita, bazata ta6a manta azabar da tasha ba, Ta tsani giants a rayuwarta, ko son ganinsu bata yi, Saboda basu da Imani, Ga ƙarfi kamar na dawakai, ta jima tana kokwanto akansu Anya kuwa Cikakkun mutanene? Kodai half jins ne?
Ta yi zurfi Acikin tunaninta, taji motsinsu, Ras taji gabanta ya faɗi ganin suna tattara kayan abincin da suka ajiye masu, aruɗe tace" ina zaku tafi da abincin mu? Bayan bamu Ci ba" babu alamun suna sauraronta,
"Magana fa nake Yi maku, idan saboda suna yin bacci ne yanzu zan tashe su, pls kada ku tafi" ko waiwaye wannan basuyi mata ba, Tana ji tana gani suka haura saman bene da abincin suka fuce daga Cikin ɗakin, Tana Jiyo sautin garkame ƙopa da su kayi,
"Ya salam" ta ambaci hakan tare da dafe kanta, muryar batool ce ta katse ta da cewa"Angel lafiya naji kina sambatu ke kaɗai"? Da sauri angel ta juya baya tana kallon batool dake kwance saman gadonta, farkawarta kenan daga bacci,
"Giants ne, Sun kawo abinci kuma sun tafi dashi bansan meyasa ba"?
Waro ido waje batool tayi fuskarta da alamun tashin hankali tace"mun shiga uku! Shikenan yau mun rasa abincin da zamu ci, angel meyasa baki tada mu daga bacci ba lokacin da suka zo"? Fuskarta a hargitse tayi maganar,
"Ina fa kokarin in tada ku daga bacci, sai naga suna tattara kayan abincin, kuma har roƙonsu nayi su tsaya amma basu saurare ni ba....." tunkan takai ƙarshen maganarta, suka soma Jin shessheƙar kukan Parveen, gaba ɗaya suka kai idanuwansu akanta, zaune take saman gadonta, ta wage baki tana ta kuka, Jin cewa Giants sun zo sun tafi da abincinsu,
Sautin Kukan Parveen ne ya farkar da sauran Ƴan uwan nasu, Hanna tana hamma tace"wai meke faruwa ne? Me akayi ma Parveen take kuka"
Javed yace"Yanzu haka rigimartace kawai, duk tabi ta tashi mutane daga bacci, saboda tsabar jarabarta,
Hannu danish ya sanya tare da zame bargon da ke lullu6e a jikin shi, idanuwanshi sun ƙanƙance daƙyar yake iya ware su, saboda baccin bai ishe shi ba,
Haris dake faman yin miƙa yace"kun yi shiru baku bamu amsa ba, Meyasa take kuka"?
Batool ce ta bashi amsa da cewa"Saboda giants sun kawo abinci, Angel bata samu damar tada mu daga bacci ba, har suka tafi da kayan abincin shine take ma kuka"
saboda tsabar tashin hankali Har suna haɗa baki wurin cewa"What? giants sunxo sun tafi da abincin mu"? Amatuƙar ruɗe kowannasu yake faman baza ido,
Dafe kai javed yayi"ae shikenan mun rasa abinci yau, Mu da ganinsu kuma sai gobe, kafin lokacin mun gama jigata,"
Yana rufe baki Rubina tace"Wlh bazan iya jurewa ba, da matsiyaciyar yunwa na farka yau...." mubeen yace"ae ba ke kaɗai ba, Cikina har wani kukan yunwa yake yi" yayi maganar yana shafa stomach ɗinshi,
"Yanzu ya zamu yi kenan"? Naufal ne yayi tambayar yana kallonsu,
Azeeza tace"Mu ci hakuri kawai, Idan munji ƙishi musha ruwa sai mu kwanta muyita bacci har gobe tayi, Harara Hibba ta jefa mata daga inda take zaune saman gadonta"Wannan fa ba abun wasa bane azeeza, magana ake ta babu abincin da zamuci yau, " azeeza tace"idan bamuyi haƙuri ba, to ya zamuyi" tayi maganar tana watsa hannayenta,
Da buɗar bakin deeja sai cewa tayi"bakowa bane ya jamana xama da yunwa ba face angel, meyasa da suka zo baki tashe mu daga bacci ba? Saboda tsabar mugunta,'
Shiru angel tayi don bazata biye mata su yi cece kuce ba, tun da ita halinta ne bata gajiya da shiga sabgar mutane,
"Kodai naje na faɗa ma tsohuwa, ta taimaka tayi magana, su giants su dawo mana da abincin mu," fuska amarairaice parveen tayi maganar, tagama shan kukan nata, taga babu mai lallashinta ta haƙura don kanta,
"Koda kinje babu abunda tsohuwa zata iya yi mana, kema kinsani" yasmin ce tayi maganar, fuskarta a hade, shi dai danish yayi lamo saman gadonshi yana bin bakunansu da kallo, sam baison hayaniyar da suke yi, don ba yadda ya iya ne daya dakatarsu,
Bakowa Angel tafi jima tausayi ba, Sai danish sanin cewa Jiya baici abincin shi ba, ya basu suka cinye, yanzu ga shi sun rasa abincin yau, dole yafi kowa jin yunwa bawan Allah,
Yau fa ba kanta, Duk jikinsu yayi laushi, Ko toilet babu wanda ya shiga don yin wanka ko wanke fuska, damuwarsu Yunwar da zasu kwasa yau, an sanyasu yin azumin dole batare da sunyi niya ba,
Saukowa haris yayi daga saman gadonshi, Ya wuce gadon danish, daga ƙasa ya zuƙunna tare da ruƙo hannun danish acikin nashi, idonsu cikin na juna, yace"ɗan uwana, ya jikin naka"? Cikin sanyin murya ya amsa mashi da cewa"da sauƙi sosai," murmushin haris yayi"Am glad to hear that, Nayi kewarka sosai na tsawon kwana biyar din nan, saina ji kamar na rasa wani sashe na jikina ne" wannan maganar ta haris ba ƙaramin faranta mashi rai tayi ba, shi kanshi ya shaida irin ƙaunar da haris ke yi mashi aduk duniya bai da tamkar shi,
"Haris, nima nayi missing ɗinku sosai, har bazan iya misaltawa ba........." dakatawa ya ɗanyi da yin maganar, ya juya bayan shi yana kallonsu batool,
"Can i talk to u"? Danish ne yayi tambayar yana kallon kowannnsu, Jin haka yasa suka sauko daga saman beds ɗinsu, suka Nufi gadon danish, a kewaye da gadon suka tsaya curko cirko suna yi mashi Yaji ki, ƙasa ƙasa da murya yake amsa masu, yayin da idanuwanshi ke akan fuskar angel dake a tsaye can nesa da su, Batool ce ta lura da kallon angel da yake yi, ta fahimci yana son itama tazo ne, amma tasan bazai iya kiranta ba, hakan yasa ita ta kira ta da kanta tace"Ki zo mana, danish yana son yin magana damu" tafiya ta soma yi xuwa bakin gadonshi ta tsaya a gefensu tare da goya hannayenta saman kirjinta,
Calmly yaci gaba da cewa"dama inaso nayi maku godiya ne, bisa irin nuna kulawarku agare ni, kun damu dani sosai, nasan kunyi missing ɗina na tsawon 5 days da bana acikin ku, nima kuma duk da bana atare daku kuna araina, i luv u so much guys......" tun da ya soma magana suka natsu suna sauraronshi, Yaushe rabon da suji danish yayi magana mai tsayi irin wannan har sun manta, lallai jiki yayi sauƙi suka ayyana hakan acikin ransu,
still bai janye idanuwanshi daga kan fuskar angel ba, itama shi ɗin take kallo, So yake yayi mata godiya amma ya kasa, ita kanta angel ɗin ta lura da hakan amma saita basar, Jira take taga idan zaiyi mata magana,
Muryar javed ce ta janyo hankalinta wurin kallonshi"